Sashe 135
Inda Rai Da Rabo Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Mamani taci gaba da fad’in “Ku sani Allah baya bacci kuma wasu sirrika dik tilin k’asan da aka aza masu toh fah ran dik Allah yaso bayyanasu toh da kansu zasu tono kansu... Alk’ali ka bani kunya kaci amanan ‘yanuwantaka... Ka biyewa sharrin wad’annan shed’anun matan ka cutarda ahalinka shin har kanada k’warin gwiwar ci gaba da rayuwa cikin ahalinka... Shin har kana iya bud’e idanu ka dubi d’an uwanka da iyalinsa tsawon shekarun nan.... Shin wane irin mugun zuciya ne da muguwar gaba had’ida mummunar k’eta zaisa ka aikata irin wannan bak’in laifi mai tarin zunubi... Shin ta yaya zaku raba k’aramin yaro d’an shekaru uku wanda baida hakkin kowa da iyayensa.... Shin da wasu idanu ka soma duban Ma’aruf a lokacinda Allah ya dawo mana dashi.... Shin dukanku da kuka salwantar dashi da wasu idanu kuka soma dubansa....? Ku fad’a min da wasu idanu kuka soma duban jikana Ma’aruf..!!!??” Ta k’arashe cikin tsananin kuka tana k’ok’arin duk’awa daidai nan Sameer da shigowarsa kenan tareda Engr yayo rakiyawa Engr dan ya gaisar dasu Mamy suka tarar da wannan iftila’i... Cikin sauri Sameer ya taro Mamani Engr na taimaka masa... Cikin sauri Abbah ya mik’a masu kujeran tsuguno na zaman mata a kitchen dake a tsakar gidan suka zaunar da Dattijuwar wacce basai ance maka ba zuciyarta ta matuk’ar raunana....
Sameer da ya tuni ya tsinci abubuwa da dama da Mamani Ke fad’i take idanunsa suka kad’a sukai jazir, dan sai yanzu yake fahimtar wasu abubuwan.... Sai yanzu ne wasu abubuwan suke dawowa kwanyarsa.....Sai yanzu yake samu amsoshin wasu tambayoyi da suka jima suna Yawo a kwanyarsa.... Take idanunsa suka kuma kad’awa suka rine, fatar jikinsa ta juye ta koma jajazir haka nan duk wata k’ofa da gashi ya ratsa cikin jikinsa saida suka mimmik’e ya d’ago yana dubansu d’aya bayan d’aya, gaban Baba Alhaji ya k’arasa sanda hawaye mai tsananin zafi ta ganagro masa, lokaci guda yake duban Baba Alhaji dake faman huci irinta mai borin kunya, cikin wata irin murya mai cikeda tsoro da kad’a zuciyar azzalumai yake furta “Duk abubuwan da naji da gaske ne.... Ku kuka rabani da iyayena da dangi na...? Kuka jefa rayuwar mahaifiyata cikin garari.... Is it true...?!!!” Ya k’arashe yana mai duban cikin idanun Baba Alhaji hawayen k’unan rai har suna rige rigen zubowa daga idanunsa da suka kad’a sukai jazir....
Daidai lokacin Mamy dake takowa gaban Haule da Lami cikin yanayi mai ban tausayi, ta dubi Lami ta dubi Haule tana tina yanda ta rik’i Lami tamkar k’anwa a gareta ba kishiya ba... Lokaci guda take furta “‘Yan uwa na d’aukeku... Ban tab’a d’aukanku da wata muguwar nufi ba... Allah Shi ne shaidata.... Lami... Haule shin kuka rabani da Ma’aruf....? Ku bud’e baki ku fad’a min.... Ku bud’e bakunanku ku sanar dani dalilinku na aikata haka a gareni....” Ta k’arashe cikin tsananin rawar murya.... Mamani ce ta kuma mik’ewa da k’yar cikeda tausayin Mamy ta isa gareta ta kamo hannayenta tana mai furta “K’warai Mariya wad’annan azzalumai su suka rabaki da gudan jininki... Su suka nisantamu da Ma’aruf, suka jefa gaba tsakaninmu suka sa muka d’aura miki laifin da bakiji ba baki gani ba bayan mun mance kece mahaifiyarsa da ganganci bazaki tab’a salwantar da gudan jininki ba sabida duk k’aunar da zamu nuna masa a bayanki ne... Mariya ki yafeni, ki yafe min duk wasu abubuwan da na miki keda ‘ya’yanki.... Ku yafeni Mariya.. Hak’ik’a yau d’in bazan iya duban cikin idanunki ba... Ked’in kin cika matar kirki, uwa ta gari kuma abokiyar zama ta kwarai sannan sirika wacce ko wace uwar miji zatai mafarkin samu, Mariya ki yafeni....!!”Ta k’arashe cikin tsananin kuka....
Lokaci guda Mamy dake hawaye sosai ta d’agota, bata iya cewa komai ba sai rungume Mamani da tai su duka biyun kuka suke sosai....
Haule dake faman yatsine yatsinen fuska tana kallon wannan drama a cewarta, shewarta ne had’ida rangad’a gud’a ya dawo da hankalin katafarin jama’an dake wajen.... Gaba d’aya duban Haule suke tamkar sabuwar kamun hauka lokaci guda Haule ta soma fad’in “Munji mu d’in maciya amana ne... Munji mud’in azzalumai ne.... Amma dik muguntarmu da makircinmu a bayan AMINIYAR SIRRI muke.....!!!!”
Da tsananin mamaki suke kuma dubanta... Lokaci guda Haule Ke takowa ta k’araso gaban Mamy... Tana wani murmushi had’ida jijjiga take fad’in “Mariya kenan.... Kin zaci mu muka rabaki da d’anki tsawon shekarun nan koh....? Toh a tinaninki zamu cika wad’annan burika namu babu taimakon AMINIYAR SIRRI NE....?”
Wane irin bugu k’irjin Aunty Bara’atu yai lokaci guda.... DUMBA sunan da yazo zuciyarta kenan
Cikin tsananin rud’ani Mamy tace “Wacece AMINIYAR SIRRI...?”
Haule ta kuma murmusawa kana tace “Kin fimu kusanci da ita....!!!”
Da tsananin mamaki Mamy ke duban Haule, lokaci guda hawayen dake idanunta taji sun k’afe... Tsananin hucinta ya k’aru “Haule kina nufin kice DUMBA itace ta taimaka maku kuka salwantar da Ma’aruf.... Shin dama Dumba tana k’asar nan tsawon shekarun nan...?”
Take wannan suna DUMBA tai ranking a k’wak’walwan Sameer, tabbas ya tab’ajin wannan suna, idan bai mance ba DUMBA itace matar da Mummynsa tace ta basu shi.... Toh wacece DUMBA.... How’s she connected to all this...?!!”
(Idan mai karatu bai mance ba dai DUMBA itace matar data bada rik’on Ma’aruf (Sameer) hannun Hajiya Fatahiyya).
SameenaAleeyou📚
*INDA RAI*
_................DA RABO_
*90*
*©️Sameena Aleeyou...✍🏽*
A hankali Sameer Ke takawa har ya isa gaban Mamy... “Mamy wacece Dumba...? Mecece alak’arku....? Ya akai Dumba ta mik’a rik’ona hannun Hajiya Fatahiyya Mummy na....? Idan ban mance ba according to Mummy ta bani labarin cewa ita wannan Dumbar itace matarsa ta bata rik’ona, sannan aikatau takewa Mummy na... Koda Mummy na ta tambayeta cewa daga ina ta samoni sai ta sanar da ita cewa Aminai uku suna yunk’urin hallak’ani shisa ta yanke shawarin turani wani waje mai nisan zango na tafi almajiranci har Allah ya nufa ta mik’a rik’ona hannun Mummy Fatahiyya.... Shin Mamy ita wannan Dumban wacece ita dan koda na tambayi Mummy ina zan sami Dumba a lokacinda nake neman iyayensa na asali Mummy ta sanar dani cewa ita kanta batasan yanda Dumba take rayuwa ba a halin yanzu.... Yanzu na samu wasu k’arin haske na sanadiyar b’acewata na kumaji wad’anda sukeda alhakin hakan... Tambaya guda da zan maki Mamy shin ita wannan Dumbar wacece... And how are you related...??”
Waje yai tsit da jin zancen Sameer da tambayoyinsa ga mahaifiyarsa, kowa so yake yaji wad’annan amsoshi... Mamy ta d’ago kai tana dubansa kana tace “Ma’aruf... Hak’ik’a Dumba ‘yar uwata ce da muka taso tare... Dumba d’iyace ga Yayar mahaifiyarmu, sanda ta rasa iyayenta rik’onta ya koma hannun mahaifiyarmu... Kaman yanda na baka labari cewa mud’in ‘yan asalin garin Jada ne ta jihar Adamawa, mahaifinmu haifeffen garin Jada ne, mahaifiyarmu kuwa asalinta ‘yar k’asar Mali ce, bafulatanar K’asar Mali ce, yak’i ya tarwatsa iyayensu a wancan shekarun, shi kuma mahaifinmu a lokacin Soja ne, lokacinda aka turasu yak’i da ‘yanta’adda acan k’asar Mali lokacin ya had’u da mahaifiyarmu har ya aureta kasancewar zasu jima sosai a k’asar Mali suna yak’i da ‘yan ta’adda hakan yasa yai aurensa a can... Sun kwashe shekaru da dama suna zaune a Mali suna yak’an ta’addanci har Allah ya albarkacesu da yara ‘yanmata guda biyu, ni da kuma babbar Yayarmu Abidah.... Toh a wannan shekarun ne lokacin Ina k’arama mahaifinmu ya yanke shawarin dawowa damu k’asarsa ta haihuwa Nigeria sabida gaba d’aya yak’i ya cinye yankinsu mahaifiyata a k’asar Mali, kusan danginta gaba d’aya saiko d’aid’aiku yak’i ya had’edasu ciki harda mahaifan Dumba.. Sanadiyar da yasa rik’on Dumba ya koma hannun mahaifiyarmu kenan.... “ Numfasawa tai kana tace “Barin dakata a nan kar labarin ya shiga cikin wani labari a tak’aice dai kaji alak’ar dake tsakanina da Dumba....”
Sameer ya numfasa kad’an kana yace “Toh ya akai Dumba ta zama wacce alhakin b’acewana Ke hannunta....?”
Wannan karon su Lami da Haule ta kalla kana tace “Wannan ne nima ban sani ba Ma’aruf, Inaga su ya kamata su sanar damu yanda suka had’e kai da Dumba wajen yunk’urin salwantar da rayuwarka... Domin kaw a iyaka sanina rana tsaka Dumba ta matsa min da cewa zata tafi ta nemi danginta a Mali idan mu mahaifinmu d’an Nigeria ne ita bazata tab’a mance cewa asalinta Mali bane.... Dama tin da jimawa Dumba tanada wannan buri shiyasa ko aure tak’i tayi a Nigeria tace har sai ta koma k’asarta ta haihuwa.... Tambayar a nan bansan ya akai ta zamto aminiya gasu Haule ba har suka had’e kai wajen salwantar dakai....”
Kaman daga sama suka sinkayo muryar Haule tana fad’in “Ko a wancan lokacin bama jituwa da Dumba, kuma tabbas Dumba tayi gaskiya da tace Aminai uku suna yunk’urin halak’a rayuwar Ma’aruf.... AMINIYAR SIRRI ba Dumba bace kaman yanda kika d’auka, Aminiyar Sirri tafi Dumba kusanci dake...”
Ta k’arashe maganar tana duban Bara’atu da kanta Ke kife tana hawaye... Dum! Dum!!Dum!!! Sautin bugun k’irjin Mamy.... Gaba d’aya kallo ya komaga Aunty Bara’atu....
Girgiza kai Mamy ta shiga yi cikin rashin yarda da abinda take gani, lokaci guda bakinta na tsanani rawa take furta “A’a... A’a Haule, hakan ba mai yuwa bane.... Haule hakan bazai tab’a kasancewa gaskiya ba....!!!”
Haule ta shek’e da wani irin dariya kana tace “Gata nan gabanki ta musa idan ba itace AMINIYAR SIRRI BA, ta musa idan ba itace ta jagoranci ragamar salwantar da d’anki ba... Gata nan gabanki....”
Sameer da ya tuni ya tsinci abubuwa da dama da Mamani Ke fad’i take idanunsa suka kad’a sukai jazir, dan sai yanzu yake fahimtar wasu abubuwan.... Sai yanzu ne wasu abubuwan suke dawowa kwanyarsa.....Sai yanzu yake samu amsoshin wasu tambayoyi da suka jima suna Yawo a kwanyarsa.... Take idanunsa suka kuma kad’awa suka rine, fatar jikinsa ta juye ta koma jajazir haka nan duk wata k’ofa da gashi ya ratsa cikin jikinsa saida suka mimmik’e ya d’ago yana dubansu d’aya bayan d’aya, gaban Baba Alhaji ya k’arasa sanda hawaye mai tsananin zafi ta ganagro masa, lokaci guda yake duban Baba Alhaji dake faman huci irinta mai borin kunya, cikin wata irin murya mai cikeda tsoro da kad’a zuciyar azzalumai yake furta “Duk abubuwan da naji da gaske ne.... Ku kuka rabani da iyayena da dangi na...? Kuka jefa rayuwar mahaifiyata cikin garari.... Is it true...?!!!” Ya k’arashe yana mai duban cikin idanun Baba Alhaji hawayen k’unan rai har suna rige rigen zubowa daga idanunsa da suka kad’a sukai jazir....
Daidai lokacin Mamy dake takowa gaban Haule da Lami cikin yanayi mai ban tausayi, ta dubi Lami ta dubi Haule tana tina yanda ta rik’i Lami tamkar k’anwa a gareta ba kishiya ba... Lokaci guda take furta “‘Yan uwa na d’aukeku... Ban tab’a d’aukanku da wata muguwar nufi ba... Allah Shi ne shaidata.... Lami... Haule shin kuka rabani da Ma’aruf....? Ku bud’e baki ku fad’a min.... Ku bud’e bakunanku ku sanar dani dalilinku na aikata haka a gareni....” Ta k’arashe cikin tsananin rawar murya.... Mamani ce ta kuma mik’ewa da k’yar cikeda tausayin Mamy ta isa gareta ta kamo hannayenta tana mai furta “K’warai Mariya wad’annan azzalumai su suka rabaki da gudan jininki... Su suka nisantamu da Ma’aruf, suka jefa gaba tsakaninmu suka sa muka d’aura miki laifin da bakiji ba baki gani ba bayan mun mance kece mahaifiyarsa da ganganci bazaki tab’a salwantar da gudan jininki ba sabida duk k’aunar da zamu nuna masa a bayanki ne... Mariya ki yafeni, ki yafe min duk wasu abubuwan da na miki keda ‘ya’yanki.... Ku yafeni Mariya.. Hak’ik’a yau d’in bazan iya duban cikin idanunki ba... Ked’in kin cika matar kirki, uwa ta gari kuma abokiyar zama ta kwarai sannan sirika wacce ko wace uwar miji zatai mafarkin samu, Mariya ki yafeni....!!”Ta k’arashe cikin tsananin kuka....
Lokaci guda Mamy dake hawaye sosai ta d’agota, bata iya cewa komai ba sai rungume Mamani da tai su duka biyun kuka suke sosai....
Haule dake faman yatsine yatsinen fuska tana kallon wannan drama a cewarta, shewarta ne had’ida rangad’a gud’a ya dawo da hankalin katafarin jama’an dake wajen.... Gaba d’aya duban Haule suke tamkar sabuwar kamun hauka lokaci guda Haule ta soma fad’in “Munji mu d’in maciya amana ne... Munji mud’in azzalumai ne.... Amma dik muguntarmu da makircinmu a bayan AMINIYAR SIRRI muke.....!!!!”
Da tsananin mamaki suke kuma dubanta... Lokaci guda Haule Ke takowa ta k’araso gaban Mamy... Tana wani murmushi had’ida jijjiga take fad’in “Mariya kenan.... Kin zaci mu muka rabaki da d’anki tsawon shekarun nan koh....? Toh a tinaninki zamu cika wad’annan burika namu babu taimakon AMINIYAR SIRRI NE....?”
Wane irin bugu k’irjin Aunty Bara’atu yai lokaci guda.... DUMBA sunan da yazo zuciyarta kenan
Cikin tsananin rud’ani Mamy tace “Wacece AMINIYAR SIRRI...?”
Haule ta kuma murmusawa kana tace “Kin fimu kusanci da ita....!!!”
Da tsananin mamaki Mamy ke duban Haule, lokaci guda hawayen dake idanunta taji sun k’afe... Tsananin hucinta ya k’aru “Haule kina nufin kice DUMBA itace ta taimaka maku kuka salwantar da Ma’aruf.... Shin dama Dumba tana k’asar nan tsawon shekarun nan...?”
Take wannan suna DUMBA tai ranking a k’wak’walwan Sameer, tabbas ya tab’ajin wannan suna, idan bai mance ba DUMBA itace matar da Mummynsa tace ta basu shi.... Toh wacece DUMBA.... How’s she connected to all this...?!!”
(Idan mai karatu bai mance ba dai DUMBA itace matar data bada rik’on Ma’aruf (Sameer) hannun Hajiya Fatahiyya).
SameenaAleeyou📚
*INDA RAI*
_................DA RABO_
*90*
*©️Sameena Aleeyou...✍🏽*
A hankali Sameer Ke takawa har ya isa gaban Mamy... “Mamy wacece Dumba...? Mecece alak’arku....? Ya akai Dumba ta mik’a rik’ona hannun Hajiya Fatahiyya Mummy na....? Idan ban mance ba according to Mummy ta bani labarin cewa ita wannan Dumbar itace matarsa ta bata rik’ona, sannan aikatau takewa Mummy na... Koda Mummy na ta tambayeta cewa daga ina ta samoni sai ta sanar da ita cewa Aminai uku suna yunk’urin hallak’ani shisa ta yanke shawarin turani wani waje mai nisan zango na tafi almajiranci har Allah ya nufa ta mik’a rik’ona hannun Mummy Fatahiyya.... Shin Mamy ita wannan Dumban wacece ita dan koda na tambayi Mummy ina zan sami Dumba a lokacinda nake neman iyayensa na asali Mummy ta sanar dani cewa ita kanta batasan yanda Dumba take rayuwa ba a halin yanzu.... Yanzu na samu wasu k’arin haske na sanadiyar b’acewata na kumaji wad’anda sukeda alhakin hakan... Tambaya guda da zan maki Mamy shin ita wannan Dumbar wacece... And how are you related...??”
Waje yai tsit da jin zancen Sameer da tambayoyinsa ga mahaifiyarsa, kowa so yake yaji wad’annan amsoshi... Mamy ta d’ago kai tana dubansa kana tace “Ma’aruf... Hak’ik’a Dumba ‘yar uwata ce da muka taso tare... Dumba d’iyace ga Yayar mahaifiyarmu, sanda ta rasa iyayenta rik’onta ya koma hannun mahaifiyarmu... Kaman yanda na baka labari cewa mud’in ‘yan asalin garin Jada ne ta jihar Adamawa, mahaifinmu haifeffen garin Jada ne, mahaifiyarmu kuwa asalinta ‘yar k’asar Mali ce, bafulatanar K’asar Mali ce, yak’i ya tarwatsa iyayensu a wancan shekarun, shi kuma mahaifinmu a lokacin Soja ne, lokacinda aka turasu yak’i da ‘yanta’adda acan k’asar Mali lokacin ya had’u da mahaifiyarmu har ya aureta kasancewar zasu jima sosai a k’asar Mali suna yak’i da ‘yan ta’adda hakan yasa yai aurensa a can... Sun kwashe shekaru da dama suna zaune a Mali suna yak’an ta’addanci har Allah ya albarkacesu da yara ‘yanmata guda biyu, ni da kuma babbar Yayarmu Abidah.... Toh a wannan shekarun ne lokacin Ina k’arama mahaifinmu ya yanke shawarin dawowa damu k’asarsa ta haihuwa Nigeria sabida gaba d’aya yak’i ya cinye yankinsu mahaifiyata a k’asar Mali, kusan danginta gaba d’aya saiko d’aid’aiku yak’i ya had’edasu ciki harda mahaifan Dumba.. Sanadiyar da yasa rik’on Dumba ya koma hannun mahaifiyarmu kenan.... “ Numfasawa tai kana tace “Barin dakata a nan kar labarin ya shiga cikin wani labari a tak’aice dai kaji alak’ar dake tsakanina da Dumba....”
Sameer ya numfasa kad’an kana yace “Toh ya akai Dumba ta zama wacce alhakin b’acewana Ke hannunta....?”
Wannan karon su Lami da Haule ta kalla kana tace “Wannan ne nima ban sani ba Ma’aruf, Inaga su ya kamata su sanar damu yanda suka had’e kai da Dumba wajen yunk’urin salwantar da rayuwarka... Domin kaw a iyaka sanina rana tsaka Dumba ta matsa min da cewa zata tafi ta nemi danginta a Mali idan mu mahaifinmu d’an Nigeria ne ita bazata tab’a mance cewa asalinta Mali bane.... Dama tin da jimawa Dumba tanada wannan buri shiyasa ko aure tak’i tayi a Nigeria tace har sai ta koma k’asarta ta haihuwa.... Tambayar a nan bansan ya akai ta zamto aminiya gasu Haule ba har suka had’e kai wajen salwantar dakai....”
Kaman daga sama suka sinkayo muryar Haule tana fad’in “Ko a wancan lokacin bama jituwa da Dumba, kuma tabbas Dumba tayi gaskiya da tace Aminai uku suna yunk’urin halak’a rayuwar Ma’aruf.... AMINIYAR SIRRI ba Dumba bace kaman yanda kika d’auka, Aminiyar Sirri tafi Dumba kusanci dake...”
Ta k’arashe maganar tana duban Bara’atu da kanta Ke kife tana hawaye... Dum! Dum!!Dum!!! Sautin bugun k’irjin Mamy.... Gaba d’aya kallo ya komaga Aunty Bara’atu....
Girgiza kai Mamy ta shiga yi cikin rashin yarda da abinda take gani, lokaci guda bakinta na tsanani rawa take furta “A’a... A’a Haule, hakan ba mai yuwa bane.... Haule hakan bazai tab’a kasancewa gaskiya ba....!!!”
Haule ta shek’e da wani irin dariya kana tace “Gata nan gabanki ta musa idan ba itace AMINIYAR SIRRI BA, ta musa idan ba itace ta jagoranci ragamar salwantar da d’anki ba... Gata nan gabanki....”