Sashe 72
Inda Rai Da Rabo Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A tare Hafiz da Najah suka shigo cikin gidan, Najah na gaba Hafiz na biyeda ita... Hajiya dake zaune tsakar gida tana faman sak’e sak’e tana ganin shigowarsu ta mik’e don dama shigowar nasu take jira tunda tuni Lami ta kirata ta zayyane mata komai...
Naja’atu batai aune ba Hajiya ta janyota ta shiga lapta tana fad’in “Shegiya mai halin annamimanci.. Ki rasa ma wanda zaki k’ulla sharri sai ‘yar uwarki ta jini... Wato Zulfa’u da danginta sun fiye maki naki ‘yar uwar munafuka annamimiya...” Ta rarumo muciya zata jibga mata Hafiz ya rik’e muciyar da iya k’arfinsa...
Hajiya ta d’ago tana duban Hafiz shaye da mamaki cikin yanayin da Bata tab’a ganinsa a irinta ba.. Idanunsa sun sauya launi sunyi jajazir gaba d’aya haka nan fatar jikinsa tayi ja, jijiyoyin jkinsa sun mimmik’e banda wani irin muguwar kallo da yake watsawa mahaifiyar tasa...
Hajiya ta soma fad’in “Hafiz kada ka yarda da wannan yarinyar munafukace... Ta guje ‘yan uwanta na jini ta zab’i ‘yan uba... Ka yarda dani d’ahna nice mai fad’i maka gaskiya....”
Bai bari takai aya ba cikin dakewar murya yake furta “Ina take...!!!?”
Hajiya tace wafah....
“Ina Sahariyya Hajiya..!!!?” Wannan karon cikin tsananin daka murya yayi maganar....
Hajiya ta rasata cewa sai inda inda da take...
Fincike muciyar yayi ya soma tafiya yana huci tamkar zai kifa k’asa....
Sahariyya dake kwance saman gado earpiece manne a kunne tana sana’arta ta jin kid’a sai sauk’ar muciya taji a gadon bayanta tamkar sauk’an aradu babu zato balle tsammani...
Sahariyya ta mik’e a gigice sabida wani irin azaban zafi dataji, ta saki ihun azaba had’ida jifa da wayar hannunta...
Hajiya da Najah suka nufo d’akin a guje jin irin k’aran da Sahariyya ta saki....
Kururuwa taci gaba da yi tana fad’in “Yaya Dan Allah kayi hak’uri, Wayyo gadon bayana wayyo k’afata... Hajiya kizo ki ceceni....”
Duk k’ok’arin Hajiya ganin ta janye Hafiz daga bugun da yake wa Sahariyya tamkar wanda ya sami busasshen hatsi amma ta kasa janyesa....
Duk yanda ya samu bugu yake tamkar wanda aka aiko, kai da gani kasan dukan huce takaici yake....
Najah da taga za’a kashe ‘yar uwarta cikin sauri ta tari dukan ta kare Sahariyya tana kuka sosai ta durk’usa a wajen tana fad’in “Yaya Dan Allah kayi hak’uri... Ya isa haka nan please Yaya Hafiz....”
Badon yaso daina dukan ba sai don ganin Naja’atu na kuka durk’ushe gabansa yasa shi jifa da muciyar, ba tareda ya kuma furta koda kalma ba ya fice daga gidan....
Naja’atu tayo kan Sahariyya dake kwance tamkar bata numfashi ta shiga jjjigata tana kirawo sunanta, a guje ta tafi d’ibo ruwa don ta yayyafa mata domin da alama Hafiz ya sumar da ita...
Hajiya ta d’aura hannu aka tana kururuwa tana fad’in wayyo ita Haule ta shiga uku....
***
Sameer na shiga sashen Mamani ya samu Salma zata tafi ta gama dressing ma Raihanah... Ta gaishesa ya amsa sama sama, bata tsaya jan dogon zance ba tai masu sallama ta wuce don ta lura da mood d’in Sameer d’in...
A d’aya daga cikin kujerun parlorn ya zauna yana mai duban sashen da Raihanar take, ita ta soma gaisar dashi ya amsa a tak’aice kana ya mata yaya jiki tace da sauk’i...
Shiru na wasu ‘yan dak’ik’ai ya biyo baya dashike Mamani na k’uryar d’aki bataji shigowar Sameer d’in ba...
Gaba d’aya Raihanah a tsarge take da kasancewarsa a wajen... Ko d’ago idanu ta kasa don wani irin naiuyinsa takeji sosai... Idanunta suka sauk’a kan hannunta da yaketa dunk’ulesu nan ta hangi jini na d’iga a hannun nasa gabanta ya yanke ya fad’i... Kar dai ciwo yaji....
SameenaAleeyou📚
*INDA RAI*
_................DA RABO_
59
*©️Sameena Aleeyou...✍🏽*
NOT EDITED
“A’a Babban Mai gidan an shigo...” Mamani tace sanda take d’age labulen d’akin, Raiha dake k’ok’arin janyo bandage ta saki a hankali ganin Mamani ta fito...
Sameer yai k’ok’arin saita kansa kana ya saki murmushi a hankali yana mai gaida Mamani...
Birki tai ganin jini a hannunsa, ta shiga salati tana sallalami tana tambayarsa mai ya sami hannunsa....
Duk sai yaji wani iri ganin ba wani babban ciwo bane d’an karjewa ne wanda baida shakku dakan bakin Hafiz da yayi ne hak’waransa sukaji masa ciwon...
Ganin hankalin Mamani ya tashi sosai ya sanyashi kwantar mata da hankali da nuna mata ba wani ciwo bane...
Mamani tace “Yo dole in damu mana Maigidan, bakasan ko k’uda banaso ya tab’aka ba balle ciwo.... Bani nan na gani...” Ta k’arashe tana janyo hannun.. Ba wai don Sameer d’in yaso ba, abin na Mamani ya soma damunsa gaba d’aya maidashi take saikace wani jinjiri, kodai don bai girma dasu bane take masa hakan k’ilan...
Raihanah takai dubantaga hannun nasa sanda Mamani ke jujjuyawa...
Ta juyo ta dubi Raiha tace “Dubu bani abin wanke ciwon naki na wanke masa...”
Raiha ta amsada “Toh Mamani tamkar wacce take jira...
Sameer yaga bilhakk’i da gaskiya Mamani take....
Cikin sauri yace “A’a Mamani ai ba sai an wanke ba ciwon ba sosai bane, bendejin ma ya isa....”
Mamani tace “Ka tabbata dai ko...?”
Sameer ya jinjina mata kai, ta amshi bandage d’in hannun Raiha tana k’ok’arin warwarewa amma bata iya ba... Ta yab’e baki tace “Ohni Halimatu ai kaga tsiyar abin nasaran naku, ni ya ake kwancewa....”
Sameer ya saki murmushi da gefen bakinsa ganin yanda take juya bandage d’in...
“Ke Dubu zoki taimaka min, zaki iya tashi aiko...?”
Raihanah ta amsada “Eh Mamani...”
Shiko Sameer kallo ya bita dashi ganin ba k’oshin lafiya bane da ita, idanunsu suka had’e waje guda, Raiha tai saurin sadda nata idanun....
Sameer ya maido da dubansaga Mamani kana yace “Karki damu Mamani zan iyayi....”
Mamani tace “A’a ta yaya zaka iya bayan hannunka guda da ciwo, Dubu maza warware ki d’aure masa barin nemo masa maganin zogi, ina tsamman akwai cikin d’aki...” Ta k’arashe tana mai shigewa d’aki...
Sameer ya tsaya kurum yana kallon ikon Allah wai shi za’a nemowa maganin zogi, k’ila Mamani ta mance shi likitane...
Ya maido da dubansaga Raiha dake durk’ushe gabansa tana warware bandage d’in a hankali tamkar mai tausayin bandage d’in... K’uri Sameer ya mata yana kallon yanda take gudanar da al’amranta cikin natsuwa da tsananin sanyi...
Ya d’anyi gyaran murya a hankali kana yace “Barshi haka nan... Give me that... Jeki ki huta I can do it...”
Ta girgiza kai a hankali kana tace “A’a zan iya Yaya....”
Ya kafeta da idanu kana ya furta “Are you sure...?”
Ta jinjina kai a hankali tana mai k’ak’aro murmushi bacin kaw banda bugu babu abinda k’irjinta keyi...
Mik’ar mata da hannun yayi yana mai ci gaba da duban yanda take zagaye hannun nasa da bandage... Baisan mai yazo cikin zuciyarsa ba amma ba kowa ya tuna ba illa matarsa Siyama, shin ko yaya zata amshi ‘yan uwansa...? Wannan tambaya ya jima yana yawo a kwanyarsa, sanin hali da yanayin matar tasa....
Har Raihanah ta kusan ida zagaye yatsun hannun nasa da bandage d’in kana ta sinkayo muryarsa yana jefo mata tambaya....
“Ya jikin naki...? How are you feeling now...?”
Idanunta naga abinda take tace “Da sauk’i sosai....”
Sameer ya jinjina kai yace “Zogin yana raguwa....?”
Nan ma jinjina masa kai tayi still idanunta naga aikin da take kana tace “Eh ya ragu, bai ciwo sosai saiko da dare....”
Sameer ya jinjina kai a hankali kana yace “You’re lucky skin d’inki nada kyau....”
Wannan karon d’agowa tai suka had’a idanu...
Kawar dakai gefe yayi tamkarma bashi yai maganar ba, daidai sanda ta ida rufe masa ciwon...
Ba tareda ya dubebtan ba yace “Kwanan nan zai warke gaba d’aya In sha Allah kinji koh....”
Ta jinjina kai a hankali...
Duban hannun nasa yayi yanda ta rufe masa tsaf kana yace “Thank you...”
Bata iya cewa komai ba sai k’ok’arin mik’ewa da tayi a daidai lokacin da Mamani ta fito tana fad’in ta nemi maganin nata sama da k’asa ta rasashi taci gaba da fad’in “Yanzu haka Sakina ce ta shigo ta d’auka kai wannan yarinya tayo halin ubanta Ado, haka nan nayi fama dashi sanda yake k’arami, ba dai na aje abin amfanina ba sai na rasashi ga b’arna kaman b’era....”
Sameer ya shafi sumarsa a hankali da d’aya hannun jin Mamani na maganganu da bai kamata suji ba, da gani wannan tsohuwa ansha fama da ita....
Mik’ewa tsaye yayi yana fad’in “Babu damuwa Mamani kar ki damu zan sha inadasu a gida... Yanzu zan zaga ko wane k’ofa ne na gaishesu kafin na wuce gidan Baba Alhaji na masa gaisuwa shima...”
Mamani ta wage baki tace “A’a lallai kaga d’an Albarka... Yawwa nace ba....”
Sameer ya d’ago yana dubanta...
Mamani taci gaba da fad’in “Ya kamata ka dawo cikin gida nan da zama, ga sashen dake gefena nan babu kowa ciki dama Alk’ali ne zai gyare min na koma ciki amma yanzu tinda Allah yayi ka dawo sai ka dawo ciki ka zauna, kaga sai mu samu musan iyalin taka sosai koh....”
Sameer ya jinjina kai a hankali kana yace “Babu damuwa Mamani zan sami Abbah da maganar...”
Mamani ta fad’ad’a murmushinta tana fad’in “Allah sarki ashe dai bazaka k’i gida ba, ai yanda kake d’an gayun nan na zaci bazakazo cikinmu ka zauna ba, Allah Ubangiji dai shi maka albarka yaci gaba da kare mana kai daga duk mai nemanka da sharri...”
Sameer yana mai amsa mata da Ameen yake ficewa amma har ya fice Mamani batai shiru ba tana mai ci gaba da masa addu’an kariya da tsari daga mugu...
***
Shagon Magaji abokinsa ya shige daga gidan Hajiya, yanda Magaji ya gansa yasan wani babban abu na damunsa ga fuskarsa a kumbure...
Magaji ya janyo benchi ya zauna kusan Hafiz kana yace “Duk wanda ya ganka Hafiz yasan kana cikin matsanancin matsala, abokina Dan Allah ka sanar dani meke damunka, naji kace fuskarka had’ari kayi, amma fah Hafiz ba fuskarka kurum ba ga dukkan alamu kai d’in cikin damuwa kake, ni tun bayan rabuwarka da Zulfa’u ban kuma gane kanka ba, ga wannan matar taka da maganganu keta fitowa akanta... Hafiz Wai Dan Allah meke faruwa dakai..... Ko kanaso kacemin har yanzu bakai tawakkali da mutuwar d’iyarka bane...?”
Naja’atu batai aune ba Hajiya ta janyota ta shiga lapta tana fad’in “Shegiya mai halin annamimanci.. Ki rasa ma wanda zaki k’ulla sharri sai ‘yar uwarki ta jini... Wato Zulfa’u da danginta sun fiye maki naki ‘yar uwar munafuka annamimiya...” Ta rarumo muciya zata jibga mata Hafiz ya rik’e muciyar da iya k’arfinsa...
Hajiya ta d’ago tana duban Hafiz shaye da mamaki cikin yanayin da Bata tab’a ganinsa a irinta ba.. Idanunsa sun sauya launi sunyi jajazir gaba d’aya haka nan fatar jikinsa tayi ja, jijiyoyin jkinsa sun mimmik’e banda wani irin muguwar kallo da yake watsawa mahaifiyar tasa...
Hajiya ta soma fad’in “Hafiz kada ka yarda da wannan yarinyar munafukace... Ta guje ‘yan uwanta na jini ta zab’i ‘yan uba... Ka yarda dani d’ahna nice mai fad’i maka gaskiya....”
Bai bari takai aya ba cikin dakewar murya yake furta “Ina take...!!!?”
Hajiya tace wafah....
“Ina Sahariyya Hajiya..!!!?” Wannan karon cikin tsananin daka murya yayi maganar....
Hajiya ta rasata cewa sai inda inda da take...
Fincike muciyar yayi ya soma tafiya yana huci tamkar zai kifa k’asa....
Sahariyya dake kwance saman gado earpiece manne a kunne tana sana’arta ta jin kid’a sai sauk’ar muciya taji a gadon bayanta tamkar sauk’an aradu babu zato balle tsammani...
Sahariyya ta mik’e a gigice sabida wani irin azaban zafi dataji, ta saki ihun azaba had’ida jifa da wayar hannunta...
Hajiya da Najah suka nufo d’akin a guje jin irin k’aran da Sahariyya ta saki....
Kururuwa taci gaba da yi tana fad’in “Yaya Dan Allah kayi hak’uri, Wayyo gadon bayana wayyo k’afata... Hajiya kizo ki ceceni....”
Duk k’ok’arin Hajiya ganin ta janye Hafiz daga bugun da yake wa Sahariyya tamkar wanda ya sami busasshen hatsi amma ta kasa janyesa....
Duk yanda ya samu bugu yake tamkar wanda aka aiko, kai da gani kasan dukan huce takaici yake....
Najah da taga za’a kashe ‘yar uwarta cikin sauri ta tari dukan ta kare Sahariyya tana kuka sosai ta durk’usa a wajen tana fad’in “Yaya Dan Allah kayi hak’uri... Ya isa haka nan please Yaya Hafiz....”
Badon yaso daina dukan ba sai don ganin Naja’atu na kuka durk’ushe gabansa yasa shi jifa da muciyar, ba tareda ya kuma furta koda kalma ba ya fice daga gidan....
Naja’atu tayo kan Sahariyya dake kwance tamkar bata numfashi ta shiga jjjigata tana kirawo sunanta, a guje ta tafi d’ibo ruwa don ta yayyafa mata domin da alama Hafiz ya sumar da ita...
Hajiya ta d’aura hannu aka tana kururuwa tana fad’in wayyo ita Haule ta shiga uku....
***
Sameer na shiga sashen Mamani ya samu Salma zata tafi ta gama dressing ma Raihanah... Ta gaishesa ya amsa sama sama, bata tsaya jan dogon zance ba tai masu sallama ta wuce don ta lura da mood d’in Sameer d’in...
A d’aya daga cikin kujerun parlorn ya zauna yana mai duban sashen da Raihanar take, ita ta soma gaisar dashi ya amsa a tak’aice kana ya mata yaya jiki tace da sauk’i...
Shiru na wasu ‘yan dak’ik’ai ya biyo baya dashike Mamani na k’uryar d’aki bataji shigowar Sameer d’in ba...
Gaba d’aya Raihanah a tsarge take da kasancewarsa a wajen... Ko d’ago idanu ta kasa don wani irin naiuyinsa takeji sosai... Idanunta suka sauk’a kan hannunta da yaketa dunk’ulesu nan ta hangi jini na d’iga a hannun nasa gabanta ya yanke ya fad’i... Kar dai ciwo yaji....
SameenaAleeyou📚
*INDA RAI*
_................DA RABO_
59
*©️Sameena Aleeyou...✍🏽*
NOT EDITED
“A’a Babban Mai gidan an shigo...” Mamani tace sanda take d’age labulen d’akin, Raiha dake k’ok’arin janyo bandage ta saki a hankali ganin Mamani ta fito...
Sameer yai k’ok’arin saita kansa kana ya saki murmushi a hankali yana mai gaida Mamani...
Birki tai ganin jini a hannunsa, ta shiga salati tana sallalami tana tambayarsa mai ya sami hannunsa....
Duk sai yaji wani iri ganin ba wani babban ciwo bane d’an karjewa ne wanda baida shakku dakan bakin Hafiz da yayi ne hak’waransa sukaji masa ciwon...
Ganin hankalin Mamani ya tashi sosai ya sanyashi kwantar mata da hankali da nuna mata ba wani ciwo bane...
Mamani tace “Yo dole in damu mana Maigidan, bakasan ko k’uda banaso ya tab’aka ba balle ciwo.... Bani nan na gani...” Ta k’arashe tana janyo hannun.. Ba wai don Sameer d’in yaso ba, abin na Mamani ya soma damunsa gaba d’aya maidashi take saikace wani jinjiri, kodai don bai girma dasu bane take masa hakan k’ilan...
Raihanah takai dubantaga hannun nasa sanda Mamani ke jujjuyawa...
Ta juyo ta dubi Raiha tace “Dubu bani abin wanke ciwon naki na wanke masa...”
Raiha ta amsada “Toh Mamani tamkar wacce take jira...
Sameer yaga bilhakk’i da gaskiya Mamani take....
Cikin sauri yace “A’a Mamani ai ba sai an wanke ba ciwon ba sosai bane, bendejin ma ya isa....”
Mamani tace “Ka tabbata dai ko...?”
Sameer ya jinjina mata kai, ta amshi bandage d’in hannun Raiha tana k’ok’arin warwarewa amma bata iya ba... Ta yab’e baki tace “Ohni Halimatu ai kaga tsiyar abin nasaran naku, ni ya ake kwancewa....”
Sameer ya saki murmushi da gefen bakinsa ganin yanda take juya bandage d’in...
“Ke Dubu zoki taimaka min, zaki iya tashi aiko...?”
Raihanah ta amsada “Eh Mamani...”
Shiko Sameer kallo ya bita dashi ganin ba k’oshin lafiya bane da ita, idanunsu suka had’e waje guda, Raiha tai saurin sadda nata idanun....
Sameer ya maido da dubansaga Mamani kana yace “Karki damu Mamani zan iyayi....”
Mamani tace “A’a ta yaya zaka iya bayan hannunka guda da ciwo, Dubu maza warware ki d’aure masa barin nemo masa maganin zogi, ina tsamman akwai cikin d’aki...” Ta k’arashe tana mai shigewa d’aki...
Sameer ya tsaya kurum yana kallon ikon Allah wai shi za’a nemowa maganin zogi, k’ila Mamani ta mance shi likitane...
Ya maido da dubansaga Raiha dake durk’ushe gabansa tana warware bandage d’in a hankali tamkar mai tausayin bandage d’in... K’uri Sameer ya mata yana kallon yanda take gudanar da al’amranta cikin natsuwa da tsananin sanyi...
Ya d’anyi gyaran murya a hankali kana yace “Barshi haka nan... Give me that... Jeki ki huta I can do it...”
Ta girgiza kai a hankali kana tace “A’a zan iya Yaya....”
Ya kafeta da idanu kana ya furta “Are you sure...?”
Ta jinjina kai a hankali tana mai k’ak’aro murmushi bacin kaw banda bugu babu abinda k’irjinta keyi...
Mik’ar mata da hannun yayi yana mai ci gaba da duban yanda take zagaye hannun nasa da bandage... Baisan mai yazo cikin zuciyarsa ba amma ba kowa ya tuna ba illa matarsa Siyama, shin ko yaya zata amshi ‘yan uwansa...? Wannan tambaya ya jima yana yawo a kwanyarsa, sanin hali da yanayin matar tasa....
Har Raihanah ta kusan ida zagaye yatsun hannun nasa da bandage d’in kana ta sinkayo muryarsa yana jefo mata tambaya....
“Ya jikin naki...? How are you feeling now...?”
Idanunta naga abinda take tace “Da sauk’i sosai....”
Sameer ya jinjina kai yace “Zogin yana raguwa....?”
Nan ma jinjina masa kai tayi still idanunta naga aikin da take kana tace “Eh ya ragu, bai ciwo sosai saiko da dare....”
Sameer ya jinjina kai a hankali kana yace “You’re lucky skin d’inki nada kyau....”
Wannan karon d’agowa tai suka had’a idanu...
Kawar dakai gefe yayi tamkarma bashi yai maganar ba, daidai sanda ta ida rufe masa ciwon...
Ba tareda ya dubebtan ba yace “Kwanan nan zai warke gaba d’aya In sha Allah kinji koh....”
Ta jinjina kai a hankali...
Duban hannun nasa yayi yanda ta rufe masa tsaf kana yace “Thank you...”
Bata iya cewa komai ba sai k’ok’arin mik’ewa da tayi a daidai lokacin da Mamani ta fito tana fad’in ta nemi maganin nata sama da k’asa ta rasashi taci gaba da fad’in “Yanzu haka Sakina ce ta shigo ta d’auka kai wannan yarinya tayo halin ubanta Ado, haka nan nayi fama dashi sanda yake k’arami, ba dai na aje abin amfanina ba sai na rasashi ga b’arna kaman b’era....”
Sameer ya shafi sumarsa a hankali da d’aya hannun jin Mamani na maganganu da bai kamata suji ba, da gani wannan tsohuwa ansha fama da ita....
Mik’ewa tsaye yayi yana fad’in “Babu damuwa Mamani kar ki damu zan sha inadasu a gida... Yanzu zan zaga ko wane k’ofa ne na gaishesu kafin na wuce gidan Baba Alhaji na masa gaisuwa shima...”
Mamani ta wage baki tace “A’a lallai kaga d’an Albarka... Yawwa nace ba....”
Sameer ya d’ago yana dubanta...
Mamani taci gaba da fad’in “Ya kamata ka dawo cikin gida nan da zama, ga sashen dake gefena nan babu kowa ciki dama Alk’ali ne zai gyare min na koma ciki amma yanzu tinda Allah yayi ka dawo sai ka dawo ciki ka zauna, kaga sai mu samu musan iyalin taka sosai koh....”
Sameer ya jinjina kai a hankali kana yace “Babu damuwa Mamani zan sami Abbah da maganar...”
Mamani ta fad’ad’a murmushinta tana fad’in “Allah sarki ashe dai bazaka k’i gida ba, ai yanda kake d’an gayun nan na zaci bazakazo cikinmu ka zauna ba, Allah Ubangiji dai shi maka albarka yaci gaba da kare mana kai daga duk mai nemanka da sharri...”
Sameer yana mai amsa mata da Ameen yake ficewa amma har ya fice Mamani batai shiru ba tana mai ci gaba da masa addu’an kariya da tsari daga mugu...
***
Shagon Magaji abokinsa ya shige daga gidan Hajiya, yanda Magaji ya gansa yasan wani babban abu na damunsa ga fuskarsa a kumbure...
Magaji ya janyo benchi ya zauna kusan Hafiz kana yace “Duk wanda ya ganka Hafiz yasan kana cikin matsanancin matsala, abokina Dan Allah ka sanar dani meke damunka, naji kace fuskarka had’ari kayi, amma fah Hafiz ba fuskarka kurum ba ga dukkan alamu kai d’in cikin damuwa kake, ni tun bayan rabuwarka da Zulfa’u ban kuma gane kanka ba, ga wannan matar taka da maganganu keta fitowa akanta... Hafiz Wai Dan Allah meke faruwa dakai..... Ko kanaso kacemin har yanzu bakai tawakkali da mutuwar d’iyarka bane...?”