Sashe 65
Inda Rai Da Rabo Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
D’an savings d’in dake jikinsa yai amfani dasu ya kama madaidaicin d’aki a hotel mai sauk’in kud’i.... Gaba d’aya ya kasa sakin jiki a hotel d’in abinka da wanda bai saba da kwanan irin local hotels haka ba, sai faman d’aga kai sama yake yana bin d’akin da kallo wai shi Khalid yau shine dai zaiyi kwanan wannan hotel d’in... A hankali ya sauk’e ajiyan zuciya had’ida fuzar da iska, kishingid’a yai saman gadon had’ida zaro wayar salulansa a aljihu ya shiga shafawa... Daidai kan lambar wayarta ya tsaya had’ida kafe wayar da idanu... Teddy Bear sunan da ya saving lambarta dashi ya furta a hankali....
Yatsunsa yakai kan lambar kaman zai dialing sai kuma ya tsaya yana kuma kallon wayar... Gajeren tsaki yai had’ida cilla wayar gefensa.... Ya janyo pillow had’ida danna kansa ciki ko baccin dole zatai gaba dashi....
Washe gari sassafe wayar Baffah ne ta tadashi tun kwanciyar bayan sallan asuba da yayi... Ya janyo wayar da k’yar yana kallon screen d’in wayar.... Ganin mai kiran nasa ya sanyashi sakin tsaki a hankali, k’arfe bakwai da rabi na safiya kaman yanda ya bayyana mashi a fuskar wayan... Bai d’aga kiran ba har ta stinke ya kuma maida kansa ya kwanta nan sautin wayar ta kuma tadashi, har ila yau Baffah amininsa ke kiransa...
Da tsaki ya d’aga wayar kana jin muryarsa kaji wanda bai sami wani wadataccen bacci a daren da ya gabata ba....
“Ka fad’a min idan bashi kake bina da zaka kirani this early...” Abinda ya soma fad’i kenan...
Daga d’aya b’angaren Baffah yace “Khalid kana ina ne...?”
“You haven’t answered my question... Why on earth zaka tasheni da sassafen nan... what for...?”
Baffah yai gajeren tsaki kana yace “Drop that ego for once in your life Khalid ba’a fad’a da iyaye... Idan har kana son albarka cikin rayuwanka kabi bayin Allahn nan sauda k’afa... Ta yaya zaka zab’i mace akan iyayenka... Akan mai Khalid....?”
Dafe kansa da ya masa nauyi yai kana yace “It’s too early for this.... I’ve headache already...”
Girgiza kai kurum Baffah yai kana yace “Tell me your location...”
Badon yaso ba sai don Baffah ya nace ya sanar dashi otel d’in da yake.....
Mintuna kad’an Baffah ya iso hotel d’in shaye da tsananin mamakin wai Khalid ke kwanan irin wannan hotel d’in...
Fuska a tab’e Baffah kebin ‘yar d’akin da kallo don shi ko wajen zama bai gani ba a cewarsa...
Khalid ya dubesa a kaikaice kana ya watsar....
Sanin cewa idan zai kwana wajen a tsaye Khalid bazaice masa ga wajen zama ba yasashi zama bakin ‘yar gadon....
K’uri Baffah ya masa kana ya girgiza kai a hankali yace “I never thought ban tab’a tunanin...kai not even in my dreams, the whole Khalid Mainasara the one that I know zai iya falling for wata mace ba waima har ya bar luxury life d’insa his family and everything yazo yana living miserable life irin haka ba... Khalid for crying out loud...!” Bai kai aya ba Khalid ya katse sa da fad’in “Cut it out please... Will you? Haba kazo ka sakani a gaba kana min lecture, wanda kayi a waya bai isheka ba... Look Baffah this is my life and I hate it when people try to intrude...” Katsesa Baffah yayi da fad’in “You can call me intruder or whatever amma bazanga kana abu maras kyau na k’yaleka ba Khalid... Quit this nonsense ka tattara ka koma gida and apologize to your parents...” Cikin tsananin b’acin rai yayi maganan wanda tinda ya soma Khalid bai kallesa ba saima wani gefen da yake duba...
A kaikaice ya dibeshi gira a sama yace “Are you done... Ka gama...?”
Baffah yayi shiru yana duban sa kurum sanda ya isa k’ofa ya bud’e masa yana mai masa alama da hannu yake fad’in “Get out please....”
Baffah yasan hakan ka iya faruwa yasan kafiya irinta Khalid mutum ne da sam bai tank’waruwa don haka bai Kuma cewa uffan ba sai mik’ewa da yayi jiki babu laka ya nufi k’ofa... Har ya isa k’ofar yaja ya tsaya, hannu yasa cikin aljihu ya ciro wallet d’insa ya zaro katin atm ya mik’a masa yana fad’in “One of your Bank cards Ammi ta bayar a kawo maka Incase you may need...”
Murmushi yai kana yace “Ka mayar mata bana buk’ata....”
Girgiza kai Baffah ya kumayi bai tsaya jan inja da Khalid ba yayi ficewarsa rai b’ace....
***
KANO
Zulfa’u na kwance uwar d’akin Mamy k’aramar alk’ur’ani rik’e hannunta tana karantawa Marliya ta shigo da sallama
A hankali ta goge hawayen da suka zubo mata kana ta dasa aya ma karatun nata ta amsa sallaman Marliya...
“Addah wai wasu bak’i ke sallama a parlorn Abbah zasu gaisheki....”
Da shike tunda akayi rasuwar parlorn Abbah ta waje na bud’e maza sukan shiga parlorn suyi gaisuwarsu musamman dangin Mamy dashike dangin Abbah wasu nacan gidan Baba Alhaji mahaifin Hafiz...
Zulfah ta dubeta da mamaki kana tace “ Bak’i kuma.... Baki sansu ba..?”
Marliya ta girgiza kai a hankali tace “Ban shiga ba Addah, Aunty B ce tace nai kiranki....”
D’an jim Zulfa’u tai kana ta mik’e ta zura hijab d’inta, hannun Marliya ta janyo da nufin tai mata rakiya...
A daidai k’ofar parlorn ta hangi Hafiz ya turo k’aramar k’ofan gate ya shigo cikin gidan... K’irjinta ya bada wani irin sauti, ganin Ya Hafiz ya sanyata shiga sabon tashin hankali domin kaw kamanninsa d’aya da d’iyarsa Kausar ne babu abinda yarinyar ta rage masa, take taji k’walla na neman ciko idanunta, tai tsaye ta kasa ci gaba da tafiya... Shima Hafiz d’in tinda ya hangeta sai ji yayi k’afafunsa sun kasa d’aukansa sai sabbin k’walla da yaji suna neman ciko idanunsa...
Marliya takai dubantaga yanda Zulfa’u ke duba ganin ta kasa ci gaba da tafiya... Ganin Ya Hafiz ne ya sata k’ok’arin juyawa da zummar komawa cikin gida amma saidai tuni Zulfa’u ta janyo hannunta sun shige cikin parlorn yanda suka bar Hafiz nan tsaye tamkar wanda ruwa ya shanye....
SameenaAleeyou📚
*INDA RAI*
_...............DA RABO_
*53*
*©️Sameena Aleeyou...✍🏽*
Marliya ce ta fara yin sallama Zulfa’u na biyeda ita, muryar da ta daki dodon kunnuwan Akram sai yaji tamkar wacce yake saurare a gidan radio, d’ago idanu yai yana duban k’ofan wanda ya sanyasa yin idanu hud’u da mai sallaman domin kaw itama Marliyan su take duba idan ka d’auke Zulfa’u da kanta ke k’asa...
Cikin sauri Hafiz ya take masu baya, bai shiga parlorn ba sai tsayawa da yayi daga bakin k’ofa yana jiyo abindake wakana, haka kurum yaji zuciyarsa sam bai kwanta masa dasu Akram ba musamman da yaga irin wankan shadda da hula da suka zuba....
Bayan sun gaisane Zulfa’u ke fad’in “Saidai ban gane daga ina bane...”
Yusuf ya d’anyi gyaran murya bayan Akram ya d’an dubeshi a kaikaice.... Nan Yusuf yaci gaba da fad’in “Mu wakilan ALHERI Party ne, mun kasance muna matuk’ar k’aunan shirye shiryenki a tasharku ta gidan radio RY, muna kuma jin dad’i sosai yanda kuke k’ok’arin gayyato manyan manazarta masu fayyace gaskiyar abindake faruwa a siyasar k’asan nan da kuma wayarwa jama’a kai a b’angaren abinda ya shafi sanin mahimmancin k’uru’unsu... Wannan dalili yasa Party d’inmu ta wakilcemu a madadin d’aukacin sauran ‘ya’ayanta kama daga shi Eng Ma’aruf MUTALLAB mai neman takaran kujeran gwabna har izuwa sauran ‘ya’yan jamk’iya suka wakiltamu domin mu mik’a gaisuwar ta’aziyanmu na rashin da aka miki... Ubangiji yajik’anta yasa kuma mai ceto ce...”
Gaba d’aya suka amsa da ameen ida ka d’auke Hafiz da k’irjinsa ke tsananin bugu da sauri da sauri, abinda yafi d’aga masa hankali ba komai bane illa ji da yayi Wai Zulfa’unsa ce ta soma aiki a gidan radio ba tareda yasan hakan ba harma wad’annan ‘yan iskan ‘yan siyasan suna saurarenta, watoma gaurayuwa kenan takeyi da maza tana masu interview... Bai ida tunanin nasa ba ya tsinkayo muryarta tana fad’in
“Allah sarki mun gode k’warai da gaisuwarku, Allah Ubangiji kuma yasa a mizani amma saidai ina fata ba sabida siyasarku kukayi haka ba domin ni aikina kwai nakeyi yadda aka umarceni...”
Yusuf ya murmusa yace “A’a Rankishi dad’e ko d’aya bamuyi hakan domin k’arawa jamk’iyarmu martaba sai don kyautata alak’armu da d’aukacin jama’an wannan jiha ina fata hakan bazai kawo wata mishkila ba...”
Kafin Zulfa’u ta sami zarafin basa amsa sukaji an banko labule an shigo.... D’aga kan da zatai tai tozali da Hafiz sai faman huci yake lokaci guda yake nuna Yusuf da Akram da ‘yar yatsa yana fad’in “Idan baku tashi kun fice ba ina mai tabbatar maku zakuga babban mishkila, don mace na aiki a gidan radio hakan bai baku dama ku dinga bibiyan matan mutane ba kuna fakewa da siyasa!” Yanda yake maganan har wani irin zabura yake sabida tsananin b’acin rai...
Zulfa’u ta mik’e a zabure tana fad’in “Ya Hafiz dan Allah ya isa haka... Not now please...”
Tsawa ya daka mata da fad’in “Kimin shiru kekuma, shine sabida tsaban iskanci har aiki kika soma gidan radio kina watsa ra’ayinki na siyasa salon maza su biyoki har gida koh... Toh wllhi kinji na rantse kin gama wannan shegen aikin gidan radio din...” Tinda ya soma magana kuka ya kufce mata yayinda Marliya ta fice a guje ta nufi cikin gida neman d’auki ganin Hafiz ya fice a giya....
Gadan gadan yayi kansu tamkar wanda zai kai masu duka yana fad’in idan basu fita ba zaiyi ajalinsu... Ganin haka yasa Zulfa’u yin kansa a guje tana k’ok’arin janyoshi amma inaa tuni ya bangajeta ta fad’i k’asa...
Sai lokacin Akram ya zabura ya mik’e yayi tsaye gaban Hafiz tamkar k’irajensu zasu gogi juna, In a husky voice Akram ke nunasa da yatsa yake fad’in “Don’t hurt her or else....”
Hafiz na d’aga jijiyan wuya yake fad’in “Or else what...? Mai zakumin, zaku sa a kasheni ne irin yanda ‘yan siyasa irinku sukeyi zakusa ‘yan dabanku suyi ajalina ne ko mai... Ka fad’a mana...!” Ya k’arashe yana kuma d’aga k’irji saman yana sakin huci daidai lokacin dasu Mamy suka shigo babu shiri suna sallalami... Aunty B ce tai k’ok’arin janye Hafiz tana mai baiwasu Akram hak’uri yayinda Mamy ta nufi d’iyarta dake durk’ushe wajen a k’asa tana kuka mai tsuma zuciya....
Yatsunsa yakai kan lambar kaman zai dialing sai kuma ya tsaya yana kuma kallon wayar... Gajeren tsaki yai had’ida cilla wayar gefensa.... Ya janyo pillow had’ida danna kansa ciki ko baccin dole zatai gaba dashi....
Washe gari sassafe wayar Baffah ne ta tadashi tun kwanciyar bayan sallan asuba da yayi... Ya janyo wayar da k’yar yana kallon screen d’in wayar.... Ganin mai kiran nasa ya sanyashi sakin tsaki a hankali, k’arfe bakwai da rabi na safiya kaman yanda ya bayyana mashi a fuskar wayan... Bai d’aga kiran ba har ta stinke ya kuma maida kansa ya kwanta nan sautin wayar ta kuma tadashi, har ila yau Baffah amininsa ke kiransa...
Da tsaki ya d’aga wayar kana jin muryarsa kaji wanda bai sami wani wadataccen bacci a daren da ya gabata ba....
“Ka fad’a min idan bashi kake bina da zaka kirani this early...” Abinda ya soma fad’i kenan...
Daga d’aya b’angaren Baffah yace “Khalid kana ina ne...?”
“You haven’t answered my question... Why on earth zaka tasheni da sassafen nan... what for...?”
Baffah yai gajeren tsaki kana yace “Drop that ego for once in your life Khalid ba’a fad’a da iyaye... Idan har kana son albarka cikin rayuwanka kabi bayin Allahn nan sauda k’afa... Ta yaya zaka zab’i mace akan iyayenka... Akan mai Khalid....?”
Dafe kansa da ya masa nauyi yai kana yace “It’s too early for this.... I’ve headache already...”
Girgiza kai kurum Baffah yai kana yace “Tell me your location...”
Badon yaso ba sai don Baffah ya nace ya sanar dashi otel d’in da yake.....
Mintuna kad’an Baffah ya iso hotel d’in shaye da tsananin mamakin wai Khalid ke kwanan irin wannan hotel d’in...
Fuska a tab’e Baffah kebin ‘yar d’akin da kallo don shi ko wajen zama bai gani ba a cewarsa...
Khalid ya dubesa a kaikaice kana ya watsar....
Sanin cewa idan zai kwana wajen a tsaye Khalid bazaice masa ga wajen zama ba yasashi zama bakin ‘yar gadon....
K’uri Baffah ya masa kana ya girgiza kai a hankali yace “I never thought ban tab’a tunanin...kai not even in my dreams, the whole Khalid Mainasara the one that I know zai iya falling for wata mace ba waima har ya bar luxury life d’insa his family and everything yazo yana living miserable life irin haka ba... Khalid for crying out loud...!” Bai kai aya ba Khalid ya katse sa da fad’in “Cut it out please... Will you? Haba kazo ka sakani a gaba kana min lecture, wanda kayi a waya bai isheka ba... Look Baffah this is my life and I hate it when people try to intrude...” Katsesa Baffah yayi da fad’in “You can call me intruder or whatever amma bazanga kana abu maras kyau na k’yaleka ba Khalid... Quit this nonsense ka tattara ka koma gida and apologize to your parents...” Cikin tsananin b’acin rai yayi maganan wanda tinda ya soma Khalid bai kallesa ba saima wani gefen da yake duba...
A kaikaice ya dibeshi gira a sama yace “Are you done... Ka gama...?”
Baffah yayi shiru yana duban sa kurum sanda ya isa k’ofa ya bud’e masa yana mai masa alama da hannu yake fad’in “Get out please....”
Baffah yasan hakan ka iya faruwa yasan kafiya irinta Khalid mutum ne da sam bai tank’waruwa don haka bai Kuma cewa uffan ba sai mik’ewa da yayi jiki babu laka ya nufi k’ofa... Har ya isa k’ofar yaja ya tsaya, hannu yasa cikin aljihu ya ciro wallet d’insa ya zaro katin atm ya mik’a masa yana fad’in “One of your Bank cards Ammi ta bayar a kawo maka Incase you may need...”
Murmushi yai kana yace “Ka mayar mata bana buk’ata....”
Girgiza kai Baffah ya kumayi bai tsaya jan inja da Khalid ba yayi ficewarsa rai b’ace....
***
KANO
Zulfa’u na kwance uwar d’akin Mamy k’aramar alk’ur’ani rik’e hannunta tana karantawa Marliya ta shigo da sallama
A hankali ta goge hawayen da suka zubo mata kana ta dasa aya ma karatun nata ta amsa sallaman Marliya...
“Addah wai wasu bak’i ke sallama a parlorn Abbah zasu gaisheki....”
Da shike tunda akayi rasuwar parlorn Abbah ta waje na bud’e maza sukan shiga parlorn suyi gaisuwarsu musamman dangin Mamy dashike dangin Abbah wasu nacan gidan Baba Alhaji mahaifin Hafiz...
Zulfah ta dubeta da mamaki kana tace “ Bak’i kuma.... Baki sansu ba..?”
Marliya ta girgiza kai a hankali tace “Ban shiga ba Addah, Aunty B ce tace nai kiranki....”
D’an jim Zulfa’u tai kana ta mik’e ta zura hijab d’inta, hannun Marliya ta janyo da nufin tai mata rakiya...
A daidai k’ofar parlorn ta hangi Hafiz ya turo k’aramar k’ofan gate ya shigo cikin gidan... K’irjinta ya bada wani irin sauti, ganin Ya Hafiz ya sanyata shiga sabon tashin hankali domin kaw kamanninsa d’aya da d’iyarsa Kausar ne babu abinda yarinyar ta rage masa, take taji k’walla na neman ciko idanunta, tai tsaye ta kasa ci gaba da tafiya... Shima Hafiz d’in tinda ya hangeta sai ji yayi k’afafunsa sun kasa d’aukansa sai sabbin k’walla da yaji suna neman ciko idanunsa...
Marliya takai dubantaga yanda Zulfa’u ke duba ganin ta kasa ci gaba da tafiya... Ganin Ya Hafiz ne ya sata k’ok’arin juyawa da zummar komawa cikin gida amma saidai tuni Zulfa’u ta janyo hannunta sun shige cikin parlorn yanda suka bar Hafiz nan tsaye tamkar wanda ruwa ya shanye....
SameenaAleeyou📚
*INDA RAI*
_...............DA RABO_
*53*
*©️Sameena Aleeyou...✍🏽*
Marliya ce ta fara yin sallama Zulfa’u na biyeda ita, muryar da ta daki dodon kunnuwan Akram sai yaji tamkar wacce yake saurare a gidan radio, d’ago idanu yai yana duban k’ofan wanda ya sanyasa yin idanu hud’u da mai sallaman domin kaw itama Marliyan su take duba idan ka d’auke Zulfa’u da kanta ke k’asa...
Cikin sauri Hafiz ya take masu baya, bai shiga parlorn ba sai tsayawa da yayi daga bakin k’ofa yana jiyo abindake wakana, haka kurum yaji zuciyarsa sam bai kwanta masa dasu Akram ba musamman da yaga irin wankan shadda da hula da suka zuba....
Bayan sun gaisane Zulfa’u ke fad’in “Saidai ban gane daga ina bane...”
Yusuf ya d’anyi gyaran murya bayan Akram ya d’an dubeshi a kaikaice.... Nan Yusuf yaci gaba da fad’in “Mu wakilan ALHERI Party ne, mun kasance muna matuk’ar k’aunan shirye shiryenki a tasharku ta gidan radio RY, muna kuma jin dad’i sosai yanda kuke k’ok’arin gayyato manyan manazarta masu fayyace gaskiyar abindake faruwa a siyasar k’asan nan da kuma wayarwa jama’a kai a b’angaren abinda ya shafi sanin mahimmancin k’uru’unsu... Wannan dalili yasa Party d’inmu ta wakilcemu a madadin d’aukacin sauran ‘ya’ayanta kama daga shi Eng Ma’aruf MUTALLAB mai neman takaran kujeran gwabna har izuwa sauran ‘ya’yan jamk’iya suka wakiltamu domin mu mik’a gaisuwar ta’aziyanmu na rashin da aka miki... Ubangiji yajik’anta yasa kuma mai ceto ce...”
Gaba d’aya suka amsa da ameen ida ka d’auke Hafiz da k’irjinsa ke tsananin bugu da sauri da sauri, abinda yafi d’aga masa hankali ba komai bane illa ji da yayi Wai Zulfa’unsa ce ta soma aiki a gidan radio ba tareda yasan hakan ba harma wad’annan ‘yan iskan ‘yan siyasan suna saurarenta, watoma gaurayuwa kenan takeyi da maza tana masu interview... Bai ida tunanin nasa ba ya tsinkayo muryarta tana fad’in
“Allah sarki mun gode k’warai da gaisuwarku, Allah Ubangiji kuma yasa a mizani amma saidai ina fata ba sabida siyasarku kukayi haka ba domin ni aikina kwai nakeyi yadda aka umarceni...”
Yusuf ya murmusa yace “A’a Rankishi dad’e ko d’aya bamuyi hakan domin k’arawa jamk’iyarmu martaba sai don kyautata alak’armu da d’aukacin jama’an wannan jiha ina fata hakan bazai kawo wata mishkila ba...”
Kafin Zulfa’u ta sami zarafin basa amsa sukaji an banko labule an shigo.... D’aga kan da zatai tai tozali da Hafiz sai faman huci yake lokaci guda yake nuna Yusuf da Akram da ‘yar yatsa yana fad’in “Idan baku tashi kun fice ba ina mai tabbatar maku zakuga babban mishkila, don mace na aiki a gidan radio hakan bai baku dama ku dinga bibiyan matan mutane ba kuna fakewa da siyasa!” Yanda yake maganan har wani irin zabura yake sabida tsananin b’acin rai...
Zulfa’u ta mik’e a zabure tana fad’in “Ya Hafiz dan Allah ya isa haka... Not now please...”
Tsawa ya daka mata da fad’in “Kimin shiru kekuma, shine sabida tsaban iskanci har aiki kika soma gidan radio kina watsa ra’ayinki na siyasa salon maza su biyoki har gida koh... Toh wllhi kinji na rantse kin gama wannan shegen aikin gidan radio din...” Tinda ya soma magana kuka ya kufce mata yayinda Marliya ta fice a guje ta nufi cikin gida neman d’auki ganin Hafiz ya fice a giya....
Gadan gadan yayi kansu tamkar wanda zai kai masu duka yana fad’in idan basu fita ba zaiyi ajalinsu... Ganin haka yasa Zulfa’u yin kansa a guje tana k’ok’arin janyoshi amma inaa tuni ya bangajeta ta fad’i k’asa...
Sai lokacin Akram ya zabura ya mik’e yayi tsaye gaban Hafiz tamkar k’irajensu zasu gogi juna, In a husky voice Akram ke nunasa da yatsa yake fad’in “Don’t hurt her or else....”
Hafiz na d’aga jijiyan wuya yake fad’in “Or else what...? Mai zakumin, zaku sa a kasheni ne irin yanda ‘yan siyasa irinku sukeyi zakusa ‘yan dabanku suyi ajalina ne ko mai... Ka fad’a mana...!” Ya k’arashe yana kuma d’aga k’irji saman yana sakin huci daidai lokacin dasu Mamy suka shigo babu shiri suna sallalami... Aunty B ce tai k’ok’arin janye Hafiz tana mai baiwasu Akram hak’uri yayinda Mamy ta nufi d’iyarta dake durk’ushe wajen a k’asa tana kuka mai tsuma zuciya....