Sashe 57
Inda Rai Da Rabo Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Daga nan ne suka tambayi Mamyn cewa zasu biya gidan Baba Alhaji su duba Kausar hakan yayi mata don dama suna k’ok’arin shirya randa zasu d’auko yarinyar itada Zulfa’u saidai sabida ciwon Abbah suka dakata sai ya sami sauk’i kar a kuma k’ara masa damuwa kan wata damuwa tinda tasan zai wuya Hajiyar Hafiz ta basu yarinyar cikin sauk’i....
***
Sun k’ule itada Lami a uwar d’aki suna tattauna lamarin, su k’ulla wannan su sak’a wancan kaman daga sama suka jiyo hayaniyar Sahariyya tana faman bambami, Hajiya da Aunty Lami suka dubi juna a tare, a tamanin Hajiya ta mik’e tana gyara d’aurin zani ta nufo waje Aunty Lami na take mata baya...
Sahariyya ta kasa ta tsare tana d’aga k’irji sama tana ci gaba da tafe hannaye tana fad’in “Billahillazi baki isa ba ba’a haifeki ba Kausar ta fiki gadara da gidan Ubanta, tinda ko yaushe yaga dama zai iya sallamarki kaman yanda ya sallami uwar yarinyar....!”
Sawwama tai tak’aitaccen murmushi kana takai dubantaga yanda su Hajiya ke tsaye, lokaci guda ta gyara tsayuwarta had’ida tallabo Kausar dake rik’e a hannunta, cikin yatsina fuska had’ida kuma turo kallabinta gaban goshi tai nuniga Hajiya da ‘yar yatsa kana ta kuma duban Sahariyya tace “Kinga ko wancan ma haka tai ta bari, ki tambayeta kiji idan ta isa ta saka Hafiz ya sakeni.... Balle ke k’aramar ‘yar iska k’aramar marar kunya wacce ko ajin farko baki ida ba...!” Ba Sahariyya data saki baki tana duban ikon Allah ba harta Aunty Lami da Hajiyar Hafiz d’in tsaye sukai tamkar gumaka suna duban Sawwama wacce ta zame masu tamkar dodanniya....
Cikin taku na k’asaita ta k’araso gaban Hajiya kana ta dangwala mata Kausar tana mai fad’in “Gata nan.... Ai dama na fad’i maki kada kiyi gigin barinta gidana domin batada muhalli cikinsa sannan ba raino aka auroni nayi ba rainon d’anki da nake idan baki gode min bazaki k’aromin ba... Gata idan kunga dama ku jefarta waje amma wllhi wllhi kunji na rantse ba cikin gidana ba....!”
Tasa kai tana k’ok’arin juyawa, banda huci da tafasa Sahariyya bata komai, duban Hajiya kawai take tana jira taga matakin da zata d’auka bataga alamun Hajiya zata motsa ba...
A d’ari Sahariyya ta sunkumo Kausar tana fad’in “Wllhi billahillazi kinyi kad’an ki shigo har cikin gidan mahaifina kiciwa mahaifiyata kashi aka k’aramar karuwa, wllhi k’aryar iskanci kike Kausar bata gida sai gidan mahaifinta....!”
Dariyar rainin hankali Sawwama ta d’anyi a tak’aice tana mai watsawa Sahariyya muguwar harara lokaci guda ta d’aga hannu ta d’auke Sahariyya da wata shu’umar mari wanda saida yasa tai kusan sakin Kausar a k’asa...
A daidai lokacinda su Nabila su Raiha suka shigo gidan da sallama....
Tukunyar tafasheshen ruwan d’anwake dake gefe sai faman tafasa yake Sahariyya tai kan Sawwama tana k’ok’arin cakumota had’ida jifa da Kausar da batamasan ina take k’ok’arin jefata ba... Cikin wani irin zabura Raihanah ta saki k’ara ta nufi Kausar da tuni tayi ambaliya cikin ruwan d’anwaken nan, tukunyar ta hantsilo ta zubewa Raihanah a b’angaren jikinta a yayinda take k’ok’arin ceto rayuwar Kausar... Wani irin k’ara Raihanah ta saki sanda ta rungume Kausar da tuni kukanta ya d’auke cak....
Innalillahi wa inna’ilaihi raji’un....
Nabila da Marliya daskarewa sukai cikin tsananin tashin hankali yayindasu Hajiya suka d’imauce lokaci guda, harta Sahariyya da Sawwama saida suka tsaya cak da fad’an da suke suna duban Raihana da Kausar da tuni sunyi wanka da tafashesshen ruwan d’anwake....
Zulfah dake k’ok’arin saka k’afafunta cikin ward d’in Abbah wani irin bugawa k’irjinta yai jiri ya kusan aikata k’asa ba tareda sanin dalili ba, da dafe ta ida shigowa cikin ward d’in.....
SameenaAleeyou 📚
*INDA RAI*
_................DA RABO_
*46*
*©️Sameena Aleeyou...✍🏽*
Aunty Lami ce tai kazar kazar aka kwashesu zuwa asibitin masu fama da matsalar k’unan wuta.... Gaba d’aya su Nabilah Hajiya da Marliya harmada Sahariyya suka d’unguma suka take masu baya...
Suna isa asibiti aka wuce dasu emergency.... Dr Awwab abokin aikin Sameer a nan asibitin Kanon shi ya amshi case d’in nasu, saidai gaba d’aya shi kansa lamarin ya shige masa duhu musmman Kausar wacce ta k’one sosai domin kuwa idan ba sa’a ba k’unan ka iya tab’a zuciyarta kuma idan har hakan ne ta kasance yasan abu ne mai matuk’ar wahala ta tashi saidai wani ikon Allah musamman duba da k’aranci na shekarunta da tsananin taushi da fatarta kedashi, a sani hakan yasa dole ya nemi taimakon Sameer domin kaw babu kaman shi a asibitin wajen sanin fata da gyaranta....
Sameer yana gab da shigowa garin Kano akai masa waya daga asibiti cewa akwai emergency.... Bai wata wata ba ya wuce asibitin domin ceton rayukan bayin Allah da suka sami had’arin wuta....
A b’angarensu Nabilah kuwa suna reception kowa da addu’an dake bakinsa dukda cewa babu wanda ya iya tsagaita hawayensa, Aunty Lami ce mai k’arfin hali tana dnnanrsu don harta Hajiya dirshan tai a reception d’in tana matsan k’walla da bakin mayafi tana fad’in ta shiga uku ta lalace sun kashewa Hafiz d’iya.... Kukan nata banda k’ona ran Nabila baya komai ji take tamkar taje ta rufe Hajiya da duka don takaici...
Aunty Lami ce tai k’arfin halin kiran Mamy ta sanar da ita halin da ake ciki da kuma asibitin da suke... Banda salati da ambaton Allah Mamy bata komai, sauk’in abin Abbah yana bacci baisan abindake faruwa ba, Mamy na cikin yanayin ne Zulfah ta turo k’ofa ta shigo da alama daga wajen aiki take, kallo guda taiwa Mamy ta kuma jin gabanta ya mugun fad’uwa.... A b’angaren Mamy ma duban Zulfa’un da tai si taji zuciyarta ta kuma yankewa, ta kasa jurewa domin kaw idanunta sun gaza b’oye hakan....
Cikin tsananin sanyin jiki Zulfah tace “Mamy lafiya ya na ganki haka kodai jikin Abbah ne....?”
Mamy ta kasa jurewa sai k’walla da suka ciko idanunta, cikin sauri ta janyo hannun Zulfah suka fice daga d’akin gudun kada Abbah ya tashi....
Saida tai k’ok’arin kwantarwa Zulfa’u hankali kafin ta sanar da ita halin da ake ciki....
Tuni k’walla sun ciko idanunta, ta kuma duban Mamy tana mai k’ok’arin goge hawayen dake zubo mata take fad’in “Mamy duk laifina ne meyasa na bar masu d’iyata, meyasa na barta babu kula....!” Kuka yaci k’arfinta...
Rik’eta Mamy tai ta zaunarta saman kujera dake gefe, cikin sigan lallashi da lallama take fad’in “Kar kice haka Zulfa’u, komai muk’addari ne daga Allah... Tuni Allah ya hukunta hakan, yau koda Kausar na taredake bazata wuce abinda Allah ya k’addara mata ba, kiyi hak’uri muyi masu addu’a Allah Ubangiji ya basu lafiya, yanzu ki tashi na kira Bara’atu zata taho ku tafi ku duba jikin nasu kinga ni bazai yuwu na tafi na bar Abbanku ba... Zulfa’u ki kwantar da hankalinki kinji koh don Allah kada ki d’aga hankalinki...”
Banda jinjina kai Zulfah bata komai sai matsan hawaye da take...
Jim kad’an Aunty B ta iso a fujajan suka wuce asibiti....
***
Kasancewar Kausar tafi jin jiki domin kaw gaba d’ayanta ta fad’a cikin tafashesshen ruwan danwaken sannan dashike k’aramar yarinyace sosai fatarta akwai taushi sosai hakan yasa k’unar yafi mata illa, Sameer na isowa ita suka soma attending, take aka preparing surgery aka shige da ita....
Sosai k’unar ya shiga jikin yarinyar domin kuwa ya riga da ya tab’a heart d’inta, sanda Sameer ya fuskanci k’unar ya shiga sosai take jikinsa yai sanyi domin yasan zai wuya yarinyar takai labari, Allahu Akbar ai kuwa basu jima da soma aikin ba zuciyar Kausar ta daina bugawa... Baisan dalili ba amma har ransa yaji mutuwar yarinyar, jikinsa yai matuk’ar yin sanyi, ya saba da irin hakan tinda ba yau bane ya soma aikin likitanci amma mutuwar wannan yarinyar a hannunsa yayi bala’ain d’aga masa hankali....
A hankali ya zame hannayensa yana mai k’urama na’urar dake nuna tsayuwan bugun zuciyar idanu...
Dr Awwab ya girgiza masa kai alamun babu ta riga ta rasu....
Sameer ya lumshe idanunsa a hankali kana suka nufo waje shida Awwab sauran nurses na k’ok’arin shirya Kausar...
A bakin theatre room d’in suka tsaya bayan sun kwab’e mask d’in dake bisa hancinsu da bakinsu suna tattauna lamarin yanda Awwab ke sanar dashi family d’in suna reception...
Sameer ya jinjina kai yace “Kace su biyu ne masu case d’in...?”
Awwab ya jinjina kai yace “Yes su biyu ne babbar tana ward nata bai shiga deep kaman na ita wannan k’aramar ba....”
Sameer ya d’an jinjina kai a hankali kana yace “Ok ka sanar da nurses d’in they should get the second patient ready zan k’arasa nai magana da family d’insu....”
Awwab ya jinjina kai yace “Ok sai ka iso....”
Jinjina masa kai kurum Sameer yai kafin ya nufi reception...
Zulfa’u da Aunty B suna isowa Su Marliya da Nabilah suka k’arasa a guje suka rungume Addarsu suna kuka... Aunty B kuwa banda jifa da kallo tskaninta dasu Hajiya bata komai, jira kawai take taji silan k’unan taji su waye sukai sanadi..
Zulfah ta kuma karaya ganin ‘yan uwanta sun rungumeta suna kuka, cikin tsananin rawar murya take furta “Nabilah ku fad’a min ina Kausar da Raiha...? Dan Allah ku fad’a min d’akin da suke naje na gansu....”
Wani irin bugu Sameer yaji k’irjinsa nayi sanda ya danno reception yai tozali da mutanen da bai jima da sanin cewa ‘yan uwansa bane... Zulfa’u Nabilah da Marliya yake duba da raunannun idanunsa yanda suka rungume juna suna kuka.... Yana jiyo sanda Zulfah ke fad’in ina d’iyarta...? Zuciyarsa ta kuma karyewa... Kenan yarinyar ‘yar uwarshi ce ta rasu a hannunsa... Ta yaya zai soma sanar da ita cewa d’iyarta ta rasu... Shin wannan shine farkon abinda zai soma had’asa da ‘yan uwansa... Mummunar labari irin wannan, ta yaya zai iya jurewa ya tink’ari ‘yan uwansa da wannan batu...? Tsananin tausayinsu gaba d’aya shida ‘yan uwan nasa ya rufe masa zuciya.... A hankali ya soma takawa har ya isa garesu yai tsaye ba tareda sunsan cewa wani na tsaye kansu ba.... Aunty B kuwa nata aikin lallashinsu tana fad’in addu’a zasuyi ba kuka ba In sha Allah Kausar da Raihanah zasu sami lafiya....
***
Sun k’ule itada Lami a uwar d’aki suna tattauna lamarin, su k’ulla wannan su sak’a wancan kaman daga sama suka jiyo hayaniyar Sahariyya tana faman bambami, Hajiya da Aunty Lami suka dubi juna a tare, a tamanin Hajiya ta mik’e tana gyara d’aurin zani ta nufo waje Aunty Lami na take mata baya...
Sahariyya ta kasa ta tsare tana d’aga k’irji sama tana ci gaba da tafe hannaye tana fad’in “Billahillazi baki isa ba ba’a haifeki ba Kausar ta fiki gadara da gidan Ubanta, tinda ko yaushe yaga dama zai iya sallamarki kaman yanda ya sallami uwar yarinyar....!”
Sawwama tai tak’aitaccen murmushi kana takai dubantaga yanda su Hajiya ke tsaye, lokaci guda ta gyara tsayuwarta had’ida tallabo Kausar dake rik’e a hannunta, cikin yatsina fuska had’ida kuma turo kallabinta gaban goshi tai nuniga Hajiya da ‘yar yatsa kana ta kuma duban Sahariyya tace “Kinga ko wancan ma haka tai ta bari, ki tambayeta kiji idan ta isa ta saka Hafiz ya sakeni.... Balle ke k’aramar ‘yar iska k’aramar marar kunya wacce ko ajin farko baki ida ba...!” Ba Sahariyya data saki baki tana duban ikon Allah ba harta Aunty Lami da Hajiyar Hafiz d’in tsaye sukai tamkar gumaka suna duban Sawwama wacce ta zame masu tamkar dodanniya....
Cikin taku na k’asaita ta k’araso gaban Hajiya kana ta dangwala mata Kausar tana mai fad’in “Gata nan.... Ai dama na fad’i maki kada kiyi gigin barinta gidana domin batada muhalli cikinsa sannan ba raino aka auroni nayi ba rainon d’anki da nake idan baki gode min bazaki k’aromin ba... Gata idan kunga dama ku jefarta waje amma wllhi wllhi kunji na rantse ba cikin gidana ba....!”
Tasa kai tana k’ok’arin juyawa, banda huci da tafasa Sahariyya bata komai, duban Hajiya kawai take tana jira taga matakin da zata d’auka bataga alamun Hajiya zata motsa ba...
A d’ari Sahariyya ta sunkumo Kausar tana fad’in “Wllhi billahillazi kinyi kad’an ki shigo har cikin gidan mahaifina kiciwa mahaifiyata kashi aka k’aramar karuwa, wllhi k’aryar iskanci kike Kausar bata gida sai gidan mahaifinta....!”
Dariyar rainin hankali Sawwama ta d’anyi a tak’aice tana mai watsawa Sahariyya muguwar harara lokaci guda ta d’aga hannu ta d’auke Sahariyya da wata shu’umar mari wanda saida yasa tai kusan sakin Kausar a k’asa...
A daidai lokacinda su Nabila su Raiha suka shigo gidan da sallama....
Tukunyar tafasheshen ruwan d’anwake dake gefe sai faman tafasa yake Sahariyya tai kan Sawwama tana k’ok’arin cakumota had’ida jifa da Kausar da batamasan ina take k’ok’arin jefata ba... Cikin wani irin zabura Raihanah ta saki k’ara ta nufi Kausar da tuni tayi ambaliya cikin ruwan d’anwaken nan, tukunyar ta hantsilo ta zubewa Raihanah a b’angaren jikinta a yayinda take k’ok’arin ceto rayuwar Kausar... Wani irin k’ara Raihanah ta saki sanda ta rungume Kausar da tuni kukanta ya d’auke cak....
Innalillahi wa inna’ilaihi raji’un....
Nabila da Marliya daskarewa sukai cikin tsananin tashin hankali yayindasu Hajiya suka d’imauce lokaci guda, harta Sahariyya da Sawwama saida suka tsaya cak da fad’an da suke suna duban Raihana da Kausar da tuni sunyi wanka da tafashesshen ruwan d’anwake....
Zulfah dake k’ok’arin saka k’afafunta cikin ward d’in Abbah wani irin bugawa k’irjinta yai jiri ya kusan aikata k’asa ba tareda sanin dalili ba, da dafe ta ida shigowa cikin ward d’in.....
SameenaAleeyou 📚
*INDA RAI*
_................DA RABO_
*46*
*©️Sameena Aleeyou...✍🏽*
Aunty Lami ce tai kazar kazar aka kwashesu zuwa asibitin masu fama da matsalar k’unan wuta.... Gaba d’aya su Nabilah Hajiya da Marliya harmada Sahariyya suka d’unguma suka take masu baya...
Suna isa asibiti aka wuce dasu emergency.... Dr Awwab abokin aikin Sameer a nan asibitin Kanon shi ya amshi case d’in nasu, saidai gaba d’aya shi kansa lamarin ya shige masa duhu musmman Kausar wacce ta k’one sosai domin kuwa idan ba sa’a ba k’unan ka iya tab’a zuciyarta kuma idan har hakan ne ta kasance yasan abu ne mai matuk’ar wahala ta tashi saidai wani ikon Allah musamman duba da k’aranci na shekarunta da tsananin taushi da fatarta kedashi, a sani hakan yasa dole ya nemi taimakon Sameer domin kaw babu kaman shi a asibitin wajen sanin fata da gyaranta....
Sameer yana gab da shigowa garin Kano akai masa waya daga asibiti cewa akwai emergency.... Bai wata wata ba ya wuce asibitin domin ceton rayukan bayin Allah da suka sami had’arin wuta....
A b’angarensu Nabilah kuwa suna reception kowa da addu’an dake bakinsa dukda cewa babu wanda ya iya tsagaita hawayensa, Aunty Lami ce mai k’arfin hali tana dnnanrsu don harta Hajiya dirshan tai a reception d’in tana matsan k’walla da bakin mayafi tana fad’in ta shiga uku ta lalace sun kashewa Hafiz d’iya.... Kukan nata banda k’ona ran Nabila baya komai ji take tamkar taje ta rufe Hajiya da duka don takaici...
Aunty Lami ce tai k’arfin halin kiran Mamy ta sanar da ita halin da ake ciki da kuma asibitin da suke... Banda salati da ambaton Allah Mamy bata komai, sauk’in abin Abbah yana bacci baisan abindake faruwa ba, Mamy na cikin yanayin ne Zulfah ta turo k’ofa ta shigo da alama daga wajen aiki take, kallo guda taiwa Mamy ta kuma jin gabanta ya mugun fad’uwa.... A b’angaren Mamy ma duban Zulfa’un da tai si taji zuciyarta ta kuma yankewa, ta kasa jurewa domin kaw idanunta sun gaza b’oye hakan....
Cikin tsananin sanyin jiki Zulfah tace “Mamy lafiya ya na ganki haka kodai jikin Abbah ne....?”
Mamy ta kasa jurewa sai k’walla da suka ciko idanunta, cikin sauri ta janyo hannun Zulfah suka fice daga d’akin gudun kada Abbah ya tashi....
Saida tai k’ok’arin kwantarwa Zulfa’u hankali kafin ta sanar da ita halin da ake ciki....
Tuni k’walla sun ciko idanunta, ta kuma duban Mamy tana mai k’ok’arin goge hawayen dake zubo mata take fad’in “Mamy duk laifina ne meyasa na bar masu d’iyata, meyasa na barta babu kula....!” Kuka yaci k’arfinta...
Rik’eta Mamy tai ta zaunarta saman kujera dake gefe, cikin sigan lallashi da lallama take fad’in “Kar kice haka Zulfa’u, komai muk’addari ne daga Allah... Tuni Allah ya hukunta hakan, yau koda Kausar na taredake bazata wuce abinda Allah ya k’addara mata ba, kiyi hak’uri muyi masu addu’a Allah Ubangiji ya basu lafiya, yanzu ki tashi na kira Bara’atu zata taho ku tafi ku duba jikin nasu kinga ni bazai yuwu na tafi na bar Abbanku ba... Zulfa’u ki kwantar da hankalinki kinji koh don Allah kada ki d’aga hankalinki...”
Banda jinjina kai Zulfah bata komai sai matsan hawaye da take...
Jim kad’an Aunty B ta iso a fujajan suka wuce asibiti....
***
Kasancewar Kausar tafi jin jiki domin kaw gaba d’ayanta ta fad’a cikin tafashesshen ruwan danwaken sannan dashike k’aramar yarinyace sosai fatarta akwai taushi sosai hakan yasa k’unar yafi mata illa, Sameer na isowa ita suka soma attending, take aka preparing surgery aka shige da ita....
Sosai k’unar ya shiga jikin yarinyar domin kuwa ya riga da ya tab’a heart d’inta, sanda Sameer ya fuskanci k’unar ya shiga sosai take jikinsa yai sanyi domin yasan zai wuya yarinyar takai labari, Allahu Akbar ai kuwa basu jima da soma aikin ba zuciyar Kausar ta daina bugawa... Baisan dalili ba amma har ransa yaji mutuwar yarinyar, jikinsa yai matuk’ar yin sanyi, ya saba da irin hakan tinda ba yau bane ya soma aikin likitanci amma mutuwar wannan yarinyar a hannunsa yayi bala’ain d’aga masa hankali....
A hankali ya zame hannayensa yana mai k’urama na’urar dake nuna tsayuwan bugun zuciyar idanu...
Dr Awwab ya girgiza masa kai alamun babu ta riga ta rasu....
Sameer ya lumshe idanunsa a hankali kana suka nufo waje shida Awwab sauran nurses na k’ok’arin shirya Kausar...
A bakin theatre room d’in suka tsaya bayan sun kwab’e mask d’in dake bisa hancinsu da bakinsu suna tattauna lamarin yanda Awwab ke sanar dashi family d’in suna reception...
Sameer ya jinjina kai yace “Kace su biyu ne masu case d’in...?”
Awwab ya jinjina kai yace “Yes su biyu ne babbar tana ward nata bai shiga deep kaman na ita wannan k’aramar ba....”
Sameer ya d’an jinjina kai a hankali kana yace “Ok ka sanar da nurses d’in they should get the second patient ready zan k’arasa nai magana da family d’insu....”
Awwab ya jinjina kai yace “Ok sai ka iso....”
Jinjina masa kai kurum Sameer yai kafin ya nufi reception...
Zulfa’u da Aunty B suna isowa Su Marliya da Nabilah suka k’arasa a guje suka rungume Addarsu suna kuka... Aunty B kuwa banda jifa da kallo tskaninta dasu Hajiya bata komai, jira kawai take taji silan k’unan taji su waye sukai sanadi..
Zulfah ta kuma karaya ganin ‘yan uwanta sun rungumeta suna kuka, cikin tsananin rawar murya take furta “Nabilah ku fad’a min ina Kausar da Raiha...? Dan Allah ku fad’a min d’akin da suke naje na gansu....”
Wani irin bugu Sameer yaji k’irjinsa nayi sanda ya danno reception yai tozali da mutanen da bai jima da sanin cewa ‘yan uwansa bane... Zulfa’u Nabilah da Marliya yake duba da raunannun idanunsa yanda suka rungume juna suna kuka.... Yana jiyo sanda Zulfah ke fad’in ina d’iyarta...? Zuciyarsa ta kuma karyewa... Kenan yarinyar ‘yar uwarshi ce ta rasu a hannunsa... Ta yaya zai soma sanar da ita cewa d’iyarta ta rasu... Shin wannan shine farkon abinda zai soma had’asa da ‘yan uwansa... Mummunar labari irin wannan, ta yaya zai iya jurewa ya tink’ari ‘yan uwansa da wannan batu...? Tsananin tausayinsu gaba d’aya shida ‘yan uwan nasa ya rufe masa zuciya.... A hankali ya soma takawa har ya isa garesu yai tsaye ba tareda sunsan cewa wani na tsaye kansu ba.... Aunty B kuwa nata aikin lallashinsu tana fad’in addu’a zasuyi ba kuka ba In sha Allah Kausar da Raihanah zasu sami lafiya....