Sashe 181
Inda Rai Da Rabo Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Haule ta mik’e a birkice tana tambayarsu lafiya....? Had’ida dafe k’irjinta...
D’ayan wanda yake rungume da gatari yace “Ina take... Ina shegiyar kishiyar taki take... Wllhi muma yai sai mun cire mata sassan jiki yanda take saida mu ana cire mana namu sassan jikin...!!!” Ya k’arashe yana kuma wasa gatarin a k’asa....
Sahariyya da Najah babu shiri suka fito suka rungume mahaifiyarsu ganin wannan kayan tashin hankali dake aukuwa gidansu....
Haule cikin rawar murya take fad’in “Innalillahi wa inna’ilaihi raji’un kunaso ku cemin gasunk’umar’yar ta’adda nake zaune da ita cikin gidan nan... Na shiga uku ni Haule wllhi ko tsuntsu ban tab’a kashewa ba, iyakacin asiri na ban tab’a kashe rai ba... Ma’aruf kawai naso aikatawa hakan shima Allah bai nufa ba dan ya nuna min shikeda cikakken iko akan komai.... Yanzu kunaso kuce matar nan saida mutum take ai tsafi dashi....!!”
D’ayan yace “K’warai kuwa dan ta saida ‘yan uwanmu kuma munji daga bakin d’iyarta sirkarki sannan kema naki d’an abinda suke shirin aikatawa dashi kenan da kuma had’in bakin mijinki...!”
Innalillahi wa inna’ilaihi raji’un..!! Tashin hankali da ba’a saka masa rana... Take Haule ta soma gani bibbiyu duniyar na juya mata.... Bama tasan sanda ta cire d’ankwalin kanta tana furta “Hafiz...! Hafiz d’ina kuke nufi...?!! A’a badai Hafiz d’ina ba...!” Lokaci guda Haule ta shiga janyo Sahariyya da Najah da tuni sunyi mutuwar tsaye tana fad’in “Kunji koh... Yayanku... Zasu kashe Yayanku.... Na shiga uku ni Haulatu... Ya Allah ka kawo min d’auki ka kare min d’ah na ka tsare min shi.... Ya Allah yanda ka kare Ma’aruf daga sharrin da muka nufesa dashi a baya ya Allah ka kare min nawa d’an daga sharrin wad’annan bayi Naka..... Ya Allah kada ka barnida iyawata, Ya Allah ka zamto majib’icin lamurana....!!” Ta k’arashe tana mai duk’a gwiwoyinta gaba d’aya k’asa cikin wani irin kuka mai ban tausayi....
Naja’atu ce ta k’araso ta d’ago Hajiya Haule... Najah na hawaye take fad’in “Allah zai kare Ya Hafiz Hajiya... Kici gaba da masa addu’a....!”
Hajiya ta d’ago idanunta masu zuban hawaye tana duban Najah lokaci guda take furta “Najah gidan Mariya zan tafi... Dole naje na rok’i yafiyar Mariya... Naji da kunnuwana ko ta yafeni wala’alla zan samu sassaucin wannan uk’uba na rayuwa da nake ciki...!” Lokaci guda Haule ta zari mayafi tana hawaye ta nufi gidan Abbah....
Naja’atu ta maidoda dubantaga ‘yan daudun kana tace “Ku kuma Allah yasa wannan ya zamto wa’azi a gareku ku gane cewa wannan hanya da kuka biyo ba turba mai kyau bace... Ita wacce kuka aminta da ita take d’oraku akan mummunar hanya na fasik’anci da sab’awa mahaliccinku gashi ta tabbata cewa azzalumarku ce.... Shin maiyasa zaku bijirewa rahamar ubangijinku...? Shin Maiyasa zaku maida kanku mata bayan Allah yayi ku maza...? Shin da Allah yaso da sai ya halitto duniyar nan Duka mata ko duka maza... Amma ba haka yaso ba, ya rabamu jinsu mabanbanta domin ya cika rahamarsa a garemu, sashenmu su samu natsuwa da sashe... Wannan rahamarsa ce a garemu... Ina fata daku da masu wannan mummunar d’abi’a irin taku zaku wa’azantu ku tuba ku karb’i halittar da Allah Yai maku a matsayin rahama a gareku...!!”
Tinda Naja’atu ta soma magana jikkunan ‘yan daudun nan yai sanyi sosai.. Kan kace mai sun soma warware zannuwan da suke d’aure dasu had’ida d’ankwalayen kansu.... D’aya daga cikin su yana hawaye yake furta “Wllhi gaskiya kika fad’i... Mu d’in mun kasance masu bijirewa rahamar ubangijimu... Daga rana mai kaman ta yau na daina Daudu kuma zan koma gaban iyayena na rok’i yafiyarsu...!” Ya k’arashe yana mai jifa da zanin hannunsa had’ida goge gazal d’in dake girarsa....
D’ayanma yai jifa da takalmin k’afarsa ta mata yana mai furta “Nima daga yau na daina kamanceceniya da mata, iyayena sunmin iyaka da gidanmu dan haka zanje na mik’a kainaga hukumar hizba su zasu taimaka su dank’ani ga iyayena... Allahu Akbar su Shazali ashe Magajiya ce ta kashesu....!” Ya k’arashe yana mai kuma matse k’wallan da suka ciko idanunsa...
Haka ‘yandaudun nan suka dinga tuba suna fad’in sun daina kamanceceniya da mata da dik wani aikin assha da suke... Daka masu cewa zasu koma garinsu gaban iyayensu sai masu cewa zasu mik’a kansu ga hukumar Hizba...
Sahariyya ta k’araso ta rungume ‘yaruwarta Naja’atu hawaye na gangaro masu su duka biyun....
***
A can gidan Abbah kaw Haule duk’e take gabansu tana kuka na nadama wanda bata tab’a irinsa ba...
Mamy dake hawaye a hankali ta kamo kafad’un Hajiya Haule ta d’agota, lokaci guda ta rungumeta ba tareda ta iya cewa komai ba sai hawaye dake gangaro mata....
Baba Alhaji ya d’an kamo gefen rigarsa ya share k’wallan da ya mak’ale masa a idanu shima.... Lokaci guda yai k’ok’arin saita kansa kana yace “Zama a nan bai ganni ba dole na tafi ga jami’an tsaro domin ceton rayuwar Hafiz....”
Mamy dake share hawayen idanunta jinjina kai tai kana tace “Wannan haka ne Abban Ma’aruf...!”
Haule dake rakub’e tai saurin cewa “Usman zanso naje dakai can wajen jami’an tsaron, zamana a nan hankalina bazai kwanta ba....!”
Abbah ya d’an dubi Haule kana ya dubi Mamy lokaci guda yake furta “Inaga ku zauna a nan zaifi... Ni zanje na sami jami’an tsaron....”
Haule na hawaye take fad’in “Dan Allah ka barni naje Abbah... Ina matuk’ar son sanin halinda d’ah na Ke ciki..!!”
Abbah ya d’anyi Jim kana ya jinjina kai a hankali... Mamy tace itama zata tafi taredasu... Gaba d’aya su duka ukun suka d’unguma suka nufi ofishin ‘yansanda domin filing report...
Har yanzu Abbah ya kasa gasgata Wai d’an uwansa Baba Alhaji zai iya aikata hakan wa Hafiz, d’ansa na cikinsa da ya haifa... Gaba d’aya jikin Abbah a matuk’ar sanyaye yake yana mamakin shin Baba Alhaji wane irin mutum ne mai matuk’ar son zuciya... Ashe dik abubuwan da suka faru basu ishesa ishara ba.... Can wani b’angare kaw na zuciyarsa yana fad’a masa rashin imanin Baba Alhaji bazai kai nan ba... Allah sa ba hakan bane da gaske... Dan dik abubuwan da yai masa bazai so ya tab’e har haka ba...
***
A nan hideout d’in nasu kaw suka had’u gaba d’ayansu... Baba Alhaji sai muzurai yake cikeda firgici.. kana ganinsa basai ance maka hankalinsa a matuk’ar tashe yake ba... Magajiya ta kuma darara masa tsawa da fad’in “Ka shige nace... Kana wani tafiya kana lalumen hanya....!”
Suna cikin tafiya saiga Babba Duna ya fito daga cikin kangon ginin tamkar wanda aka jefosa....
Kallo guda zaka masa ka fahimci wannan anyi shed’anin k’arshen zamani wanda ya tsufa yana b’arna da fasadi a doron k’asa....
Baba Alhaji saida ya firgita da ganin Babba Duna...
Magajiya ta risina ta gaida Babba kana tace “Abokin huld’a kuna daji muna gari muna maku yak’i.... !”
Babba ya kuma kecewa da dariya kana yace “An gaida mai ‘yandaudu... Wannan shine sabon member da kikai masa register...?”
Magajiya ta jinjina kai tace “Shine wannan, mijina kuma mahaifiga Hafiz....”
Gaban Baba Alhaji ya tsananta fad’uwa a daidai sanda aka fito da Hafiz... Wani irin tsoro da firgici had’ida rud’ani suka d’arsar masa a zuciya ganin yanda azzaluman mutanen nan suka sauyawa Hafiz d’insa kamanni sabida tsananin bugu....
***
Bayan Sawwama kaw tasha da k’yar Daga hannun ‘yan daudun nan kaw take jami’an DSS d’in suka take mata baya ba tareda saninta ba, d’ayan ya shafi ‘yar k’aramar na’uran magana dake mak’ale kunnensa yana mai furta “Positive Sir, we need backup ASAP...!”
SameenaAleeyou📚
*INDA RAI*
_................DA RABO_
*108*
*©️Sameena Aleeyou...✍🏽*
NOT EDITED
A nan police station su Mamy sunyi jigum jigum suna jiran ba’asi daga jami’an tsaro, Hajiya Haule abin tausayi idan ka ganta dole ta baka tausayi, haka nan Mamy keta dannarta tana bata baki...
Wasu ‘yansanda ne suka fito daga wata k’ofa Abbah na biye dasu... Nan su Mamy ma suka mik’e ganin zugan ‘yansandan sun fice, jagaban nasu wanda da gani basai ance maka shine jagora ba waya yake yana fad’in team d’insa sun zama ready.... Hilox da motocinsu Jami’an tsaron suka nufa yayinda Mamy da Haule suka nufi wajen Abbah yanda wani jami’in tsaron ke kuma jadadda masa kada suyi yunk’urin bin bayansu sabida had’ari dake tattareda yanda suka nufa d’in...
Haule na hawaye take fad’ida Abbah “Ni dai Alhaji Usman ka taimaka ka barni na bisu... Inason sanin halinda d’ah na Ke ciki.... Ka taimaka ka k’yaleni na bisu Hafiz d’ina na can....!” Ta k’arashe tana mai had’e hannayenta biyu waje guda alamun rok’o...
Daga Abbah har Mamy tausayi Haule tai mugun basu, bazasu iya k’yaleta a wannan yanayi ba, Abbah ya nusa kad’an kana yace “Inaga mubi bayan nasu...”
Mamy ta jinjina kai tana mai furta hakan yayi, nan suka nufi motar Abban kana suka take ma jami’an tsaron baya...
****
Girgiza kai kurum Baba Alhaji yake yana duban wannan tashin hankali da tinda yazo duniya bai tab’a ganin irinta ba.... Jikinsa har wane irin tsuma yake, ya dubi Magajiya dake tsaye yawa ‘yar gunda tana faman k’yak’yata dariya ganin yanda Hafiz ya koma abin kwatance.....
Cikin wane irin murya mai cikeda tashin hankali Baba Alhaj Ke fad’in “Amma Magajiya kedai babu zuciya cikin k’irjinki idan kuma akwai toh fah ta riga ta gama bushewa... Shin mai muka maki da tsanani...? Mai Hafiz ya maki da zaki jefasa cikin wannan mummunar tashin hankali irin haka....?!”
Banda uwar harara bata aika masa komai, lokaci guda taci gaba da fad’in “Kai saurara Alhaji nifa taimakon ka nake idan bazaka amshi kud’in fansar sassan jikin Hafiz ba nifa gaba Ta kaini, kuma da kake cewa mai Hafiz yamin, idan baimin ba ai yayiwa d’iyata dan haka ko a k’asar gyalena idan Babba yaga dama yai gunduwa gunduwa dashi yanzu gabanmu babu abinda ya shalleni matuk’a zan caske kud’ad’ena....!” Ta k’arashe tana watsa masa mugun kallo lokaci guda Ta shige k’ofar da Babba da wani yaron sa suka bi...
Cikin sauri Baba Alhaji jiki na wani irin kyarma ya k’araso zai kwance Hafiz.... A wane irin fusace Hafiz d’in yace dashi “Don’t ...! Kada ka kuskura kazo kusana... Kada ka yarda kai kuskuren tab’ani...!!!!” Yai maganar yana tsananin haki..
D’ayan wanda yake rungume da gatari yace “Ina take... Ina shegiyar kishiyar taki take... Wllhi muma yai sai mun cire mata sassan jiki yanda take saida mu ana cire mana namu sassan jikin...!!!” Ya k’arashe yana kuma wasa gatarin a k’asa....
Sahariyya da Najah babu shiri suka fito suka rungume mahaifiyarsu ganin wannan kayan tashin hankali dake aukuwa gidansu....
Haule cikin rawar murya take fad’in “Innalillahi wa inna’ilaihi raji’un kunaso ku cemin gasunk’umar’yar ta’adda nake zaune da ita cikin gidan nan... Na shiga uku ni Haule wllhi ko tsuntsu ban tab’a kashewa ba, iyakacin asiri na ban tab’a kashe rai ba... Ma’aruf kawai naso aikatawa hakan shima Allah bai nufa ba dan ya nuna min shikeda cikakken iko akan komai.... Yanzu kunaso kuce matar nan saida mutum take ai tsafi dashi....!!”
D’ayan yace “K’warai kuwa dan ta saida ‘yan uwanmu kuma munji daga bakin d’iyarta sirkarki sannan kema naki d’an abinda suke shirin aikatawa dashi kenan da kuma had’in bakin mijinki...!”
Innalillahi wa inna’ilaihi raji’un..!! Tashin hankali da ba’a saka masa rana... Take Haule ta soma gani bibbiyu duniyar na juya mata.... Bama tasan sanda ta cire d’ankwalin kanta tana furta “Hafiz...! Hafiz d’ina kuke nufi...?!! A’a badai Hafiz d’ina ba...!” Lokaci guda Haule ta shiga janyo Sahariyya da Najah da tuni sunyi mutuwar tsaye tana fad’in “Kunji koh... Yayanku... Zasu kashe Yayanku.... Na shiga uku ni Haulatu... Ya Allah ka kawo min d’auki ka kare min d’ah na ka tsare min shi.... Ya Allah yanda ka kare Ma’aruf daga sharrin da muka nufesa dashi a baya ya Allah ka kare min nawa d’an daga sharrin wad’annan bayi Naka..... Ya Allah kada ka barnida iyawata, Ya Allah ka zamto majib’icin lamurana....!!” Ta k’arashe tana mai duk’a gwiwoyinta gaba d’aya k’asa cikin wani irin kuka mai ban tausayi....
Naja’atu ce ta k’araso ta d’ago Hajiya Haule... Najah na hawaye take fad’in “Allah zai kare Ya Hafiz Hajiya... Kici gaba da masa addu’a....!”
Hajiya ta d’ago idanunta masu zuban hawaye tana duban Najah lokaci guda take furta “Najah gidan Mariya zan tafi... Dole naje na rok’i yafiyar Mariya... Naji da kunnuwana ko ta yafeni wala’alla zan samu sassaucin wannan uk’uba na rayuwa da nake ciki...!” Lokaci guda Haule ta zari mayafi tana hawaye ta nufi gidan Abbah....
Naja’atu ta maidoda dubantaga ‘yan daudun kana tace “Ku kuma Allah yasa wannan ya zamto wa’azi a gareku ku gane cewa wannan hanya da kuka biyo ba turba mai kyau bace... Ita wacce kuka aminta da ita take d’oraku akan mummunar hanya na fasik’anci da sab’awa mahaliccinku gashi ta tabbata cewa azzalumarku ce.... Shin maiyasa zaku bijirewa rahamar ubangijinku...? Shin Maiyasa zaku maida kanku mata bayan Allah yayi ku maza...? Shin da Allah yaso da sai ya halitto duniyar nan Duka mata ko duka maza... Amma ba haka yaso ba, ya rabamu jinsu mabanbanta domin ya cika rahamarsa a garemu, sashenmu su samu natsuwa da sashe... Wannan rahamarsa ce a garemu... Ina fata daku da masu wannan mummunar d’abi’a irin taku zaku wa’azantu ku tuba ku karb’i halittar da Allah Yai maku a matsayin rahama a gareku...!!”
Tinda Naja’atu ta soma magana jikkunan ‘yan daudun nan yai sanyi sosai.. Kan kace mai sun soma warware zannuwan da suke d’aure dasu had’ida d’ankwalayen kansu.... D’aya daga cikin su yana hawaye yake furta “Wllhi gaskiya kika fad’i... Mu d’in mun kasance masu bijirewa rahamar ubangijimu... Daga rana mai kaman ta yau na daina Daudu kuma zan koma gaban iyayena na rok’i yafiyarsu...!” Ya k’arashe yana mai jifa da zanin hannunsa had’ida goge gazal d’in dake girarsa....
D’ayanma yai jifa da takalmin k’afarsa ta mata yana mai furta “Nima daga yau na daina kamanceceniya da mata, iyayena sunmin iyaka da gidanmu dan haka zanje na mik’a kainaga hukumar hizba su zasu taimaka su dank’ani ga iyayena... Allahu Akbar su Shazali ashe Magajiya ce ta kashesu....!” Ya k’arashe yana mai kuma matse k’wallan da suka ciko idanunsa...
Haka ‘yandaudun nan suka dinga tuba suna fad’in sun daina kamanceceniya da mata da dik wani aikin assha da suke... Daka masu cewa zasu koma garinsu gaban iyayensu sai masu cewa zasu mik’a kansu ga hukumar Hizba...
Sahariyya ta k’araso ta rungume ‘yaruwarta Naja’atu hawaye na gangaro masu su duka biyun....
***
A can gidan Abbah kaw Haule duk’e take gabansu tana kuka na nadama wanda bata tab’a irinsa ba...
Mamy dake hawaye a hankali ta kamo kafad’un Hajiya Haule ta d’agota, lokaci guda ta rungumeta ba tareda ta iya cewa komai ba sai hawaye dake gangaro mata....
Baba Alhaji ya d’an kamo gefen rigarsa ya share k’wallan da ya mak’ale masa a idanu shima.... Lokaci guda yai k’ok’arin saita kansa kana yace “Zama a nan bai ganni ba dole na tafi ga jami’an tsaro domin ceton rayuwar Hafiz....”
Mamy dake share hawayen idanunta jinjina kai tai kana tace “Wannan haka ne Abban Ma’aruf...!”
Haule dake rakub’e tai saurin cewa “Usman zanso naje dakai can wajen jami’an tsaron, zamana a nan hankalina bazai kwanta ba....!”
Abbah ya d’an dubi Haule kana ya dubi Mamy lokaci guda yake furta “Inaga ku zauna a nan zaifi... Ni zanje na sami jami’an tsaron....”
Haule na hawaye take fad’in “Dan Allah ka barni naje Abbah... Ina matuk’ar son sanin halinda d’ah na Ke ciki..!!”
Abbah ya d’anyi Jim kana ya jinjina kai a hankali... Mamy tace itama zata tafi taredasu... Gaba d’aya su duka ukun suka d’unguma suka nufi ofishin ‘yansanda domin filing report...
Har yanzu Abbah ya kasa gasgata Wai d’an uwansa Baba Alhaji zai iya aikata hakan wa Hafiz, d’ansa na cikinsa da ya haifa... Gaba d’aya jikin Abbah a matuk’ar sanyaye yake yana mamakin shin Baba Alhaji wane irin mutum ne mai matuk’ar son zuciya... Ashe dik abubuwan da suka faru basu ishesa ishara ba.... Can wani b’angare kaw na zuciyarsa yana fad’a masa rashin imanin Baba Alhaji bazai kai nan ba... Allah sa ba hakan bane da gaske... Dan dik abubuwan da yai masa bazai so ya tab’e har haka ba...
***
A nan hideout d’in nasu kaw suka had’u gaba d’ayansu... Baba Alhaji sai muzurai yake cikeda firgici.. kana ganinsa basai ance maka hankalinsa a matuk’ar tashe yake ba... Magajiya ta kuma darara masa tsawa da fad’in “Ka shige nace... Kana wani tafiya kana lalumen hanya....!”
Suna cikin tafiya saiga Babba Duna ya fito daga cikin kangon ginin tamkar wanda aka jefosa....
Kallo guda zaka masa ka fahimci wannan anyi shed’anin k’arshen zamani wanda ya tsufa yana b’arna da fasadi a doron k’asa....
Baba Alhaji saida ya firgita da ganin Babba Duna...
Magajiya ta risina ta gaida Babba kana tace “Abokin huld’a kuna daji muna gari muna maku yak’i.... !”
Babba ya kuma kecewa da dariya kana yace “An gaida mai ‘yandaudu... Wannan shine sabon member da kikai masa register...?”
Magajiya ta jinjina kai tace “Shine wannan, mijina kuma mahaifiga Hafiz....”
Gaban Baba Alhaji ya tsananta fad’uwa a daidai sanda aka fito da Hafiz... Wani irin tsoro da firgici had’ida rud’ani suka d’arsar masa a zuciya ganin yanda azzaluman mutanen nan suka sauyawa Hafiz d’insa kamanni sabida tsananin bugu....
***
Bayan Sawwama kaw tasha da k’yar Daga hannun ‘yan daudun nan kaw take jami’an DSS d’in suka take mata baya ba tareda saninta ba, d’ayan ya shafi ‘yar k’aramar na’uran magana dake mak’ale kunnensa yana mai furta “Positive Sir, we need backup ASAP...!”
SameenaAleeyou📚
*INDA RAI*
_................DA RABO_
*108*
*©️Sameena Aleeyou...✍🏽*
NOT EDITED
A nan police station su Mamy sunyi jigum jigum suna jiran ba’asi daga jami’an tsaro, Hajiya Haule abin tausayi idan ka ganta dole ta baka tausayi, haka nan Mamy keta dannarta tana bata baki...
Wasu ‘yansanda ne suka fito daga wata k’ofa Abbah na biye dasu... Nan su Mamy ma suka mik’e ganin zugan ‘yansandan sun fice, jagaban nasu wanda da gani basai ance maka shine jagora ba waya yake yana fad’in team d’insa sun zama ready.... Hilox da motocinsu Jami’an tsaron suka nufa yayinda Mamy da Haule suka nufi wajen Abbah yanda wani jami’in tsaron ke kuma jadadda masa kada suyi yunk’urin bin bayansu sabida had’ari dake tattareda yanda suka nufa d’in...
Haule na hawaye take fad’ida Abbah “Ni dai Alhaji Usman ka taimaka ka barni na bisu... Inason sanin halinda d’ah na Ke ciki.... Ka taimaka ka k’yaleni na bisu Hafiz d’ina na can....!” Ta k’arashe tana mai had’e hannayenta biyu waje guda alamun rok’o...
Daga Abbah har Mamy tausayi Haule tai mugun basu, bazasu iya k’yaleta a wannan yanayi ba, Abbah ya nusa kad’an kana yace “Inaga mubi bayan nasu...”
Mamy ta jinjina kai tana mai furta hakan yayi, nan suka nufi motar Abban kana suka take ma jami’an tsaron baya...
****
Girgiza kai kurum Baba Alhaji yake yana duban wannan tashin hankali da tinda yazo duniya bai tab’a ganin irinta ba.... Jikinsa har wane irin tsuma yake, ya dubi Magajiya dake tsaye yawa ‘yar gunda tana faman k’yak’yata dariya ganin yanda Hafiz ya koma abin kwatance.....
Cikin wane irin murya mai cikeda tashin hankali Baba Alhaj Ke fad’in “Amma Magajiya kedai babu zuciya cikin k’irjinki idan kuma akwai toh fah ta riga ta gama bushewa... Shin mai muka maki da tsanani...? Mai Hafiz ya maki da zaki jefasa cikin wannan mummunar tashin hankali irin haka....?!”
Banda uwar harara bata aika masa komai, lokaci guda taci gaba da fad’in “Kai saurara Alhaji nifa taimakon ka nake idan bazaka amshi kud’in fansar sassan jikin Hafiz ba nifa gaba Ta kaini, kuma da kake cewa mai Hafiz yamin, idan baimin ba ai yayiwa d’iyata dan haka ko a k’asar gyalena idan Babba yaga dama yai gunduwa gunduwa dashi yanzu gabanmu babu abinda ya shalleni matuk’a zan caske kud’ad’ena....!” Ta k’arashe tana watsa masa mugun kallo lokaci guda Ta shige k’ofar da Babba da wani yaron sa suka bi...
Cikin sauri Baba Alhaji jiki na wani irin kyarma ya k’araso zai kwance Hafiz.... A wane irin fusace Hafiz d’in yace dashi “Don’t ...! Kada ka kuskura kazo kusana... Kada ka yarda kai kuskuren tab’ani...!!!!” Yai maganar yana tsananin haki..