Sashe 80
Inda Rai Da Rabo Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Sanda labarin ya riski Hajiyar Hafiz bayan Lami ta gama labarta mata tashin hankalin dake gabansu ne.... Tabbas idan kan mata ukun nan Mamy da ‘yanuwanta ya had’e shikenan kashinsu ya bushe su kad’ai za’a bari a rana.... Tagajan magajan ta nufi asibitin tana kuka yanda ta riski su Mamy tuni sun isa can, cikeda tausayawa Mamy ta k’araso yanda take tana bata baki had’ida k’arfafa mata gwiwa....
Hajiya bata daina kuka tana furta Hafiz d’inta bazai mutu ba... Shikenan mata d’ah namiji.... Ta kuma d’aura hannaye aka tana kuka kaman wacce batai imani da k’addara ba...
A b’angaren Lami da Aunty B kuwa kowacce kallon kallo kawai suke aikama junansu....
Daga can Abbah da Sameer harma da Shasmu suna tafe tareda wasu likitoci guda biyu suna tattauna lamarin Baba Alhaji ya k’araso tagajan magajan sai sab’a babban riga yake... Abbah yaceda Likitocin ga mahaifin nasa ya iso.... Tuni Baba Alhaji ya nufesu yana tambayan ina Hafiz...? Ina d’ansa....?”
Dr guda d’aya ya dafasa yana k’ok’arin calming d’insa yake sanar dashi Hafiz zai sami lafiya da izinin Allah....
Baba Alhaji yakai dubansaga Abbah da Sameer kana yace “Ya akai ku kuka fara sani...? Meke faruwa...?”
Gaban Sameer ya fad’i don bai sanar dasu cewa shi ya buge Hafiz ba.... Baba Alhaji ya kuma fad’i cikin hasala...
“Usman ka sanar dani meke faruwa... Ya akai kaida d’anka ku labarin had’arin ya soma riska...?”
Dukda jama’a dake faman kai komo bai hana Baba Alhaji d’aga murya yana surfa bala’i ba....
Abbah ganin Yayan nasa zai tara masu jama’a ya d’an bud’e murya yace “Yaya baka fahimta ba... Sameer shine ya kiramu yake sanar damu kasan cewa shi ma’aikacin lafiya ne....”
Baba Alhaji yace “Wanene kuma Sameer...?”
Sameer ya d’ago idanu yana dubansa sanda Abbah yake furta “Dahnah Ma’aruf...”
K’are masa kallo Baba Alhaji yayi ba tareda ya furta komai ba kana ya kuma sab’a babbar rigarsa yabi bayan likitocin don jin bayanin hoton k’irjin da sukaima Hafiz.... A cewar likitocin ya sami rauni sosai ta cikin k’irjinsa dad’ida k’ari alamu sun nuna cewa yana cikin matsanancin tashin hankali da damuwa had’arin ya samesa wanda ya janyo zuciyarsa tai rauni sosai....
Sameer ya dafe kansa a hankali sanda Shamsu ya janyo hannunsa suka keb’e da abokin nasa....
***
Washe gari Nabilah na had’uwa da Yusrah a makaranta sai rungumeta tai tana kuka sosai, lokaci guda take furta “Yusrah ina sonshi... Wllhi ina sonshi, na kasa yakishe tunaninshi cikin zuciyata....”
Tausayinta ya cika Yusrah, rik’o hannunta tai da sauri suka fice daga ajin dashike babu malamin da ya shigo, nan suka keb’e yanda Nabilar ta labarta mata komai, duk yanda abin ya kasance....
Yusrah ta sauk’e ajiyan zuciya kana tace “K’awata ki kwantar da hankalinki ni wllhi inaji ajikina keda Khalid had’in Allah ne kuma d’an adam bai isa ya rabaku ba... Da sannu al’amara zasu daidaita bayan sunyi zafi... Kar ki mance duk tsanani na tareda sauk’i, kawai kici gaba da addu’a Allah ya kawo maku mafita....”
Jinjina kai Nabilah tai ba tareda furta komai ba...
Yusrah ta d’an murmusa tana dubanta kana tace “Ikon Allah da idan akacemin k’awa zata fad’a kogin love haka zance wllhi k’aryane... Where’s the tough Nabila that I used to know... Nabilar da maza basa gabanta... Mafad’aciya wacce baka gano lagonta da wuri... Lallai Khalid ya cire tuta cikin maza tinda har soyayyarsa ke neman canza wannan Nabilar daga mafad’aciya zuwa mai sanyi....” Dukan da Nabila ta kai mata ya sanyata shanyewa tana mai ci gaba da dariya...
Nabila ta galla mata harara tana mai tattare books d’inta take fad’in “Sai ki tashi muje ai gashi can ya shigo...”
Yusrah bata daina zolayarta ba har suka shige aji.....
A b’angaren Zulfa’u kuwa tana zaune ne kurum a office amma zuciyarta na wani wajen daban....
Atika ce ta shigo ta risketa a haka, janyo kujera tai daga can gefe ta zauna tana mai bud’e folder d’in dake gabanta had’ida ciro takardan da zasu gudanar da shirin yau.....
SameenaAleeyou 📚
*INDA RAI*
_................DA RABO_
*65*
Duk maganganun da Atika keyi sam Zulfah ba sauraronta take ba, ta ije takardun hannunta tana mai duban Zulfa’un.... D’an zungurinta da biron hannunta tai kana tace “Wai lafiya kike...?”
Nannuyan ajiyan Zuciya Zulfa’u ta sauk’e kana ta d’an shafi fuskarta tace “Lau nake.... Mu fara gudanar da shirin koh....”
Atika ta jinjina kai bawai don ta gamsu da amsar Zulfa’un ba kana tai alamu ga mai saka sauti da hannunta, suka rufe kunnuwansu da headphones su duka biyun ko wacce da takarda hannunta kafin suka soma gudanar da shirin......
****
Misalin k’arfe goma na hantsi Sameer ya shigo sashen Mamani, a parlor ya risketa ta ida shiri don dama ita yazo d’auka su tafi asibiti can wajen Hafiz.... Raihanah da Naja’atu na zaune daga gefe gaba d’aya suka gaidashi... Ya amsa cikeda kulawa sanda Mamani tai kiran Najah tazo ta duba mata takalminta maras nauyi parlorn ya rage saura Sameer da Raihanah, idanunsa naga ciwon Raihanan yana ganin yanda yake healing slowly... Gaba d’aya bata sakewa idan yana dubanta duk sai tajita ba’a sake ba haka nan, muryarsa ta kuma sinkayowa yanai mata yaya jiki, ta amsa a tak’aice... Ya jinjina kai kana ya k’arada “Salma tazo jiya....?”
Nan ma jinjina kai ta kumayi kana tace “Eh tazo...”
Ya jinjina kai a hankali ba tareda ya kuma furta komai ba.... Fitowan Mamani da Naja’atu ne ya katse firan nasu...
Mamani ta dubi Sameer tace “Ai sai muje koh... Ke Naja’atu ince kinzo mu tafi tarene...?”
Naja’atu tai saurin jinjina kai kana tace “Eh Mamani...”
Sameer yace “Bara naje na kunna motar sai kun fito...”
Mamani ta jinjina kai tana mai fad’in “Yauwa gamu nan fitowa....”
Sallama Raihanah tai masu kana ta basu sak’on gaisuwa su isar zuwaga Yayanta Hafiz da addu’an sauk’i a garesa.... Suna fitowa ne suka had’u da Marliya itama ta take masu baya suka d’unguma gaba d’aya...
Dashike Shamsu ne zaune gaban motar hakan ya sanyasu duka zama a bayan motar, a hanya Marliya ke tambayan Naja’atu jikin Sahariyya don tin dukan da Hafiz ya mata har yanzu bata sami ishesshen lafiya ba, hannunta guda ya karye haka nan ta sami rauni a k’afarta...
Gaba d’aya Hajiya Haule ba a hayyacinta take ba, abubuwa suna kan faruwa ba yanda taso ba ga babban abinda yafi bata mamaki shine tun jiya da aka kawo Hafiz asibiti matarsa Sawwama bata tako k’afarta ba, wannan abu sosai ya dami Hajiya, tai k’udirin da zaran wasu awannni sun shura bata ganta tazo ba toh zata garzaya can gidan Hafiz d’in ta duba ko lafiya ko mai ya hana matarsa kasancewa dashi a daidai irin wannan lokaci....
Isowarsu da kad’an suke samun labarin farkawan Hafiz d’in... Kalman Zulfa’u itace a bakinsa sanda ya farka... Hajiya Haule dake zaune gefensa wani k’atutun bak’in ciki ya tokare mata mak’oshi... Ta mik’e zunbur tana karanto hamdala had’ida tambayarsa mai yakeso.... Maimakon ya bata amsa sai sunan Zulfa’u da ya kuma kira.... Daidai lokacindasu Abbah da Sameer suka shigo d’akin...
Hafiz yaci gaba da fad’in “Hajiya ki taimakeni ki ceceni ki kirawo min Zulfa’u... Inaso na rok’eta gafara kafin na bar duniya.... Hajiya bazanso na mutu da hakkinta ba....” Ya k’arashe maganar da k’yar yana mai k’ok’arin kai hannu don dafe k’irjinsa.... Cikin sauri Sameer ya k’arasa yana fad’in “Take things easy, a halinda kake ciki yanzu hutu ya kamata ka samu....”
Hafiz ya k’ura masa idanu yana mai tunanin tabbas yaga fuskar nan before he lost consciousness... Tabbas ya ga Sameer akansa na k’ok’arin taimaka masa.... Yai shiru suna duban juna shida Sameer d’in...
Baba Alhaji ya k’araso cikin sauri yana dafe hannayen Hafiz d’in yake tambayarsa ya sanar dashi mai ya faru...? Ya akai ya sami accident...?
Hafiz ya dubi mahaifin nasa, ya kuma duban Sameer dake tsaye gefe, ya maido da dubansaga mahaifinsa alamun zai soma magana, caraf ya sinkayo muryar Sameer na fad’in “It was me... Ni ne na bigesa da mota....” Ai bai kai aya ba Baba Alhaji yayi tsalle ya cakumosa yana fad’in “Kashesa kayi niyya, kashesa zakai akan ya saki k’anwarka... Shin kai mai ka sani Ma’aruf...? Fansa ka dawo d’auka....? Ka sanar dani fansa ka dawo d’auka....? Idan fansa ka dawo d’auka ka sani ba akan Hafiz zaka d’auka ba don ba shi yayi sanadiyan b’acewarka ba... Wad’anda zaka d’auki fansa akansu....” Baikai aya ba Hajiya tai wuf ta shiga k’ok’arin janye Baba Alhaji ganin zai saki layi.... Mamani dasu Najah suka shigo a birkice jiyo muryar Baba Alhaji da sukai yana tashi cikin karaji....
Marliya jiki na rawa ta isa tana k’ok’arin janye d’an uwanta ganin yanda Baba Alhaji ya shak’e masa wuya tamkar zai aikasa lahira...
Mamani kam kuka ta saki tana fad’iwa Baba Alhaji ya sakar mata jika ko ta masa baki... Jin haka ne ya sanya Baba Alhaji janye hannayensa daga wuyan Sameer, Hajiya ba haka taso ba, taso ya aikasa lahira kowa ya huta, asirinsu ya rufu ruf rufuwa ta har abada.... Shamsu da shigowarsa kenan ya k’arasa a guje yana mai tallafo abokinsa yake tambayarsa ko yana lafiya....
Hafiz dake tari a hankali yana yunk’urin magana amma ya kasa.... Da k’yar ya iya furta “Baba dan Allah ka k’yale Sameer, babu laifinsa... Laifinane da nake tafiya ba tareda sanin yanda nake zuwa ba... Hasalima ni ya kamaci na rok’eshi gafara halinda na jefashi ciki.... Ya mik’o hannayensa yana k’ok’arin kamo hannayen Sameer lokaci guda yake furta “Ma’aruf ka yafe min please..... Ka yafe min duk wasu abubuwan da na maka.....”
Sameer na sosa wuyarsa yake girgiza kai lokaci guda ya rik’e hannun Hafiz yace “Ka daina fad’in haka Hafiz, bakamin laifin komai ba.... Fatana Allah ya baka lafiya....”
Hafiz da siririyar hawaye ke zubo masa yaci gaba da fad’in “Na gode.... Na gode Sameer, kanada zuciya mai kyau, dan Allah ka tayani rok’on Zulfa’u ta yafemin.....”
Hajiya bata daina kuka tana furta Hafiz d’inta bazai mutu ba... Shikenan mata d’ah namiji.... Ta kuma d’aura hannaye aka tana kuka kaman wacce batai imani da k’addara ba...
A b’angaren Lami da Aunty B kuwa kowacce kallon kallo kawai suke aikama junansu....
Daga can Abbah da Sameer harma da Shasmu suna tafe tareda wasu likitoci guda biyu suna tattauna lamarin Baba Alhaji ya k’araso tagajan magajan sai sab’a babban riga yake... Abbah yaceda Likitocin ga mahaifin nasa ya iso.... Tuni Baba Alhaji ya nufesu yana tambayan ina Hafiz...? Ina d’ansa....?”
Dr guda d’aya ya dafasa yana k’ok’arin calming d’insa yake sanar dashi Hafiz zai sami lafiya da izinin Allah....
Baba Alhaji yakai dubansaga Abbah da Sameer kana yace “Ya akai ku kuka fara sani...? Meke faruwa...?”
Gaban Sameer ya fad’i don bai sanar dasu cewa shi ya buge Hafiz ba.... Baba Alhaji ya kuma fad’i cikin hasala...
“Usman ka sanar dani meke faruwa... Ya akai kaida d’anka ku labarin had’arin ya soma riska...?”
Dukda jama’a dake faman kai komo bai hana Baba Alhaji d’aga murya yana surfa bala’i ba....
Abbah ganin Yayan nasa zai tara masu jama’a ya d’an bud’e murya yace “Yaya baka fahimta ba... Sameer shine ya kiramu yake sanar damu kasan cewa shi ma’aikacin lafiya ne....”
Baba Alhaji yace “Wanene kuma Sameer...?”
Sameer ya d’ago idanu yana dubansa sanda Abbah yake furta “Dahnah Ma’aruf...”
K’are masa kallo Baba Alhaji yayi ba tareda ya furta komai ba kana ya kuma sab’a babbar rigarsa yabi bayan likitocin don jin bayanin hoton k’irjin da sukaima Hafiz.... A cewar likitocin ya sami rauni sosai ta cikin k’irjinsa dad’ida k’ari alamu sun nuna cewa yana cikin matsanancin tashin hankali da damuwa had’arin ya samesa wanda ya janyo zuciyarsa tai rauni sosai....
Sameer ya dafe kansa a hankali sanda Shamsu ya janyo hannunsa suka keb’e da abokin nasa....
***
Washe gari Nabilah na had’uwa da Yusrah a makaranta sai rungumeta tai tana kuka sosai, lokaci guda take furta “Yusrah ina sonshi... Wllhi ina sonshi, na kasa yakishe tunaninshi cikin zuciyata....”
Tausayinta ya cika Yusrah, rik’o hannunta tai da sauri suka fice daga ajin dashike babu malamin da ya shigo, nan suka keb’e yanda Nabilar ta labarta mata komai, duk yanda abin ya kasance....
Yusrah ta sauk’e ajiyan zuciya kana tace “K’awata ki kwantar da hankalinki ni wllhi inaji ajikina keda Khalid had’in Allah ne kuma d’an adam bai isa ya rabaku ba... Da sannu al’amara zasu daidaita bayan sunyi zafi... Kar ki mance duk tsanani na tareda sauk’i, kawai kici gaba da addu’a Allah ya kawo maku mafita....”
Jinjina kai Nabilah tai ba tareda furta komai ba...
Yusrah ta d’an murmusa tana dubanta kana tace “Ikon Allah da idan akacemin k’awa zata fad’a kogin love haka zance wllhi k’aryane... Where’s the tough Nabila that I used to know... Nabilar da maza basa gabanta... Mafad’aciya wacce baka gano lagonta da wuri... Lallai Khalid ya cire tuta cikin maza tinda har soyayyarsa ke neman canza wannan Nabilar daga mafad’aciya zuwa mai sanyi....” Dukan da Nabila ta kai mata ya sanyata shanyewa tana mai ci gaba da dariya...
Nabila ta galla mata harara tana mai tattare books d’inta take fad’in “Sai ki tashi muje ai gashi can ya shigo...”
Yusrah bata daina zolayarta ba har suka shige aji.....
A b’angaren Zulfa’u kuwa tana zaune ne kurum a office amma zuciyarta na wani wajen daban....
Atika ce ta shigo ta risketa a haka, janyo kujera tai daga can gefe ta zauna tana mai bud’e folder d’in dake gabanta had’ida ciro takardan da zasu gudanar da shirin yau.....
SameenaAleeyou 📚
*INDA RAI*
_................DA RABO_
*65*
Duk maganganun da Atika keyi sam Zulfah ba sauraronta take ba, ta ije takardun hannunta tana mai duban Zulfa’un.... D’an zungurinta da biron hannunta tai kana tace “Wai lafiya kike...?”
Nannuyan ajiyan Zuciya Zulfa’u ta sauk’e kana ta d’an shafi fuskarta tace “Lau nake.... Mu fara gudanar da shirin koh....”
Atika ta jinjina kai bawai don ta gamsu da amsar Zulfa’un ba kana tai alamu ga mai saka sauti da hannunta, suka rufe kunnuwansu da headphones su duka biyun ko wacce da takarda hannunta kafin suka soma gudanar da shirin......
****
Misalin k’arfe goma na hantsi Sameer ya shigo sashen Mamani, a parlor ya risketa ta ida shiri don dama ita yazo d’auka su tafi asibiti can wajen Hafiz.... Raihanah da Naja’atu na zaune daga gefe gaba d’aya suka gaidashi... Ya amsa cikeda kulawa sanda Mamani tai kiran Najah tazo ta duba mata takalminta maras nauyi parlorn ya rage saura Sameer da Raihanah, idanunsa naga ciwon Raihanan yana ganin yanda yake healing slowly... Gaba d’aya bata sakewa idan yana dubanta duk sai tajita ba’a sake ba haka nan, muryarsa ta kuma sinkayowa yanai mata yaya jiki, ta amsa a tak’aice... Ya jinjina kai kana ya k’arada “Salma tazo jiya....?”
Nan ma jinjina kai ta kumayi kana tace “Eh tazo...”
Ya jinjina kai a hankali ba tareda ya kuma furta komai ba.... Fitowan Mamani da Naja’atu ne ya katse firan nasu...
Mamani ta dubi Sameer tace “Ai sai muje koh... Ke Naja’atu ince kinzo mu tafi tarene...?”
Naja’atu tai saurin jinjina kai kana tace “Eh Mamani...”
Sameer yace “Bara naje na kunna motar sai kun fito...”
Mamani ta jinjina kai tana mai fad’in “Yauwa gamu nan fitowa....”
Sallama Raihanah tai masu kana ta basu sak’on gaisuwa su isar zuwaga Yayanta Hafiz da addu’an sauk’i a garesa.... Suna fitowa ne suka had’u da Marliya itama ta take masu baya suka d’unguma gaba d’aya...
Dashike Shamsu ne zaune gaban motar hakan ya sanyasu duka zama a bayan motar, a hanya Marliya ke tambayan Naja’atu jikin Sahariyya don tin dukan da Hafiz ya mata har yanzu bata sami ishesshen lafiya ba, hannunta guda ya karye haka nan ta sami rauni a k’afarta...
Gaba d’aya Hajiya Haule ba a hayyacinta take ba, abubuwa suna kan faruwa ba yanda taso ba ga babban abinda yafi bata mamaki shine tun jiya da aka kawo Hafiz asibiti matarsa Sawwama bata tako k’afarta ba, wannan abu sosai ya dami Hajiya, tai k’udirin da zaran wasu awannni sun shura bata ganta tazo ba toh zata garzaya can gidan Hafiz d’in ta duba ko lafiya ko mai ya hana matarsa kasancewa dashi a daidai irin wannan lokaci....
Isowarsu da kad’an suke samun labarin farkawan Hafiz d’in... Kalman Zulfa’u itace a bakinsa sanda ya farka... Hajiya Haule dake zaune gefensa wani k’atutun bak’in ciki ya tokare mata mak’oshi... Ta mik’e zunbur tana karanto hamdala had’ida tambayarsa mai yakeso.... Maimakon ya bata amsa sai sunan Zulfa’u da ya kuma kira.... Daidai lokacindasu Abbah da Sameer suka shigo d’akin...
Hafiz yaci gaba da fad’in “Hajiya ki taimakeni ki ceceni ki kirawo min Zulfa’u... Inaso na rok’eta gafara kafin na bar duniya.... Hajiya bazanso na mutu da hakkinta ba....” Ya k’arashe maganar da k’yar yana mai k’ok’arin kai hannu don dafe k’irjinsa.... Cikin sauri Sameer ya k’arasa yana fad’in “Take things easy, a halinda kake ciki yanzu hutu ya kamata ka samu....”
Hafiz ya k’ura masa idanu yana mai tunanin tabbas yaga fuskar nan before he lost consciousness... Tabbas ya ga Sameer akansa na k’ok’arin taimaka masa.... Yai shiru suna duban juna shida Sameer d’in...
Baba Alhaji ya k’araso cikin sauri yana dafe hannayen Hafiz d’in yake tambayarsa ya sanar dashi mai ya faru...? Ya akai ya sami accident...?
Hafiz ya dubi mahaifin nasa, ya kuma duban Sameer dake tsaye gefe, ya maido da dubansaga mahaifinsa alamun zai soma magana, caraf ya sinkayo muryar Sameer na fad’in “It was me... Ni ne na bigesa da mota....” Ai bai kai aya ba Baba Alhaji yayi tsalle ya cakumosa yana fad’in “Kashesa kayi niyya, kashesa zakai akan ya saki k’anwarka... Shin kai mai ka sani Ma’aruf...? Fansa ka dawo d’auka....? Ka sanar dani fansa ka dawo d’auka....? Idan fansa ka dawo d’auka ka sani ba akan Hafiz zaka d’auka ba don ba shi yayi sanadiyan b’acewarka ba... Wad’anda zaka d’auki fansa akansu....” Baikai aya ba Hajiya tai wuf ta shiga k’ok’arin janye Baba Alhaji ganin zai saki layi.... Mamani dasu Najah suka shigo a birkice jiyo muryar Baba Alhaji da sukai yana tashi cikin karaji....
Marliya jiki na rawa ta isa tana k’ok’arin janye d’an uwanta ganin yanda Baba Alhaji ya shak’e masa wuya tamkar zai aikasa lahira...
Mamani kam kuka ta saki tana fad’iwa Baba Alhaji ya sakar mata jika ko ta masa baki... Jin haka ne ya sanya Baba Alhaji janye hannayensa daga wuyan Sameer, Hajiya ba haka taso ba, taso ya aikasa lahira kowa ya huta, asirinsu ya rufu ruf rufuwa ta har abada.... Shamsu da shigowarsa kenan ya k’arasa a guje yana mai tallafo abokinsa yake tambayarsa ko yana lafiya....
Hafiz dake tari a hankali yana yunk’urin magana amma ya kasa.... Da k’yar ya iya furta “Baba dan Allah ka k’yale Sameer, babu laifinsa... Laifinane da nake tafiya ba tareda sanin yanda nake zuwa ba... Hasalima ni ya kamaci na rok’eshi gafara halinda na jefashi ciki.... Ya mik’o hannayensa yana k’ok’arin kamo hannayen Sameer lokaci guda yake furta “Ma’aruf ka yafe min please..... Ka yafe min duk wasu abubuwan da na maka.....”
Sameer na sosa wuyarsa yake girgiza kai lokaci guda ya rik’e hannun Hafiz yace “Ka daina fad’in haka Hafiz, bakamin laifin komai ba.... Fatana Allah ya baka lafiya....”
Hafiz da siririyar hawaye ke zubo masa yaci gaba da fad’in “Na gode.... Na gode Sameer, kanada zuciya mai kyau, dan Allah ka tayani rok’on Zulfa’u ta yafemin.....”