Sashe 148
Inda Rai Da Rabo Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A can gidan Engr kaw bai sanar da Muhibbah yanda zasuje ba saidai ya umarceta data shirya yaran gaba d’aya dan duk tare zasu fita, ga wani kwalliya na musamman da mijin nata ya buga, saikace wani sabon ango, ta lura yanayin da yake ciki a yau d’in zata iya cewa bata tab’a ganinsa ciki ba tsawon rayuwarsu saiko lokutan data haifo masa yaransu, Toh what’s he up...? Ta tambayi kanta sanda ta hangosa na sauk’owa daga bene waya manne kunnensa... Zumbur ta mik’e gabanta na wani irin yankewa dan wani irin azabebben kyau ya mata ga k’warjininsa da ya kuma fitowa sosai, haka kurum taji hankalinta bai kwanta ba.....
Ya k’araso yana mai saka wayar a aljihu daidai sanda su Najma Irfaan da kuma Samha suka k’araso suna rungumesa suna fad’in “Daddy you look handsome..!” Ya d’auki Najma ya azata a kafad’a yayinda ya shafa kan Irfaan da Samha yace maza su shige Patrick ya bud’e masu mota....
Muhibbah ta raka yaran nata da muguwar kallo a cewarta munafunci ke sa suke nuna sunfi son ubansu sama da ita, bacin haka dik gayu da tasha basuce ta masu kyau ba sai Ubansu, munafukan banza kawai... Duban Engr ta d’an kumayi kana tace “Wai ina ne kam zamuje my Engr....?”
Ba tareda ya dubeta ba yace “It’s Sunday, after all... Idan munje zaki gani...” Daga haka sa kai yai ya shige Najma tana fad’in zata sha ice cream d’in cold stone...
Muhibbah dai tab’e baki tai kana tace a zuciyarta k’ila sabida weekend ne shiyasa zasu fita gaba d’aya da yaran tinda sun jima basu d’an fita haka ba kullum hidiman siyasa bai bari ya zauna, wata zuciyar kuma tace K’ila sabida misunderstanding d’in da kuka samu jiya ne kikai banza dashi shiyasa yau ya shirya maku fita to make it up to you... Ta wani murmusa ita kad’ai tana jin kanta, a hankali ta shiga buga kafad’anta tana fad’in “Ke d’in amanarsa ce dole dik yanda yakaiga fushi ya sauk’o ya baki hak’uri..!” Ta kuma murmusawa kafin ta d’au handbag da mayafinta saman sofa ta take masu baya...
SameenaAleeyou📚
*INDA RAI*
_...............DA RABO_
*95*
*©️Sameena Aleeyou✍🏽*
Suna tafe cikin motar yake sanar da ita yanda zasuje da kuma dalilin zuwan nasu, mamaki da al’ajabi ya cika Muhibbah... Gyara zama ta d’anyi tana dubansa sosai, lokaci guda take furta “Anya kuwa Excellency na... ‘Yan uwanka fah kace...? Mai yasa tintini basu nemeka ba, sai yanzu da sukaga ka zama mai fad’i aji, Nidai inaga kud’inka suke kwad’ayi babu wani ‘yanuwankan nan....”
Wane irin duba da yake aika mata ya sanyata had’iye sauran maganganun nata.... Ta d’an muskuta tana yatsina fuska lokaci guda taci gaba da fad’in “Ni dai shawari nake baka ka bincika da kyau, Frauds sunyi yawa...!”
Ba don shid’in bai kasance daga cikin maza masu dukan mata ba tabbas da ya shasshafeta da mari masu kyau, sannan yaransu dake bayan motar baiso su d’ago wani abu, shisa ma yai mata shiru, amma kam duba guda zaka masa ka fahimci tsananin b’acin rai da maganganun Muhibbah ya jefasa ciki, ta yaya zai kawo mata wannan labari mai dad’in gaske da yaso surprising d’inta dashi ta karb’i zancen a haka... A matsayinta na matarsa abokiyar rayuwarsa, tsawon shekarun nan ya zaci zatafi kowa nuna Farin cikinta, ya zaci zata tayasa Farin ciki bayan tulin shekarun nan da yayi cikin duhun rashin sanin ina asalinsa... Tareda ita akaita gwagwarmaya lokacin da ‘yan adawa sukaso b’ata masa suna cewa baida asali wanda badon Allah ya kiyaye ba da maganan yai tasiri, amma dik Muhibbah ta mance wannan, ya yana sanar da ita mahaifiyarsa na raye kuma ya sameta amma tana cewa Allah sa ba ‘yan wanki bane... Bai iya furta mata komai ba sai murza tafin hannunsa a hankali da yake sabida tsananin b’acin rai....
Ta d’an saci kallonsa had’ida tab’e baki kad’an, ita dai dikda cewa ya sanar da ita tinaninsa da ya b’ace sanda yake k’arami ya dawo amma bata yarda wad’annan mutanen ba dukiyar mijinta suke bibiya ba dan haka kawai taji sam bata yarda dasu ba, tin kafin tayi ido hud’u dasu taji ta tsanesu sosai...
*****
A tare Marliya da Raihanah suka gaidashi, ya amsa idanunsa kan Raihanar, ta masa kyau sosai, rigar ta amsheta... Har saida yaji ya kasa janye idanunsa daga barin dubanta, dikda cewa itad’in nata idanun a k’asa suke... Bud’e murya ya d’anyi kana yace “Kun shirya...?”
Suka jinjina kai a tare Marliya na fad’in “Eh mun shirya Yaya....”
Jinjina kai shima d’in yai kana yace “Alright kuje mota ku jiran barin duba Abbah Ina zuwa....”
Amsa mar sukai da toh kana yasa kai ya juya, sai sannan Raihanah ta d’ago ta dubesa sanda yake ficewa... Yau d’in shadda ce dakakkiyar wagambari mai ruwan sararin samaniya da akai mata d’inkin jampa jikinsa saiko hula zanna bukar mai kalan shud’i wato dark blue wanda ya dace da zarenda akai ado ma kayan dashi, yayi kyau matuk’a kaman wani sabon ango... Koda Sameer ya isa sashen Abbah bai tadda Abbah ba, dan rufe ya tadda sashen nasa, Toh Ina Abban ya tafi kuma ai yau d’in weekend ne....? Kasa samo amsar yai hakan ya sanyashi juyowa yana tinanin yanda Abbah ya tafi, daga nan sashen Mamani ya lek’a nan ma sammakal bata nan kaman yanda bak’in Kazaure ma dik sun tafi da alama wasu kuma suna b’angaren su Baffah Ado.... Ajiyan zuciya ya sauk’e a hankali kana ya nufo waje ya taddasu Raihanah, alamun bud’e mota da sukaji ya sanya Marliya saurin kaman marfin backseat ta shige abinta... Raihanah tai rau rau tana duban Marliya dake mata alama da ta shiga gaba.. Girgiza kai kurum tai dan ita yanzu ta gama gane Marliya neman magana ne da ita had’ida jin baki, haka nan ta kama marfin front seat d’in ta shige dik tana jinta wane iri... Itakam maiyasa dik sanda suka kasance tare take jin wannan yanayi...? Tambayar da ta tabbata bata da amsar sa, hakan sai ya tuna mata d’aukota daga islamiya da yai kwanakin baya, tana jin sanda ya daidaita saman driver’s seat bugun zuciyarta ya k’aru gaba d’aya a tak’ure take, Allah ya sani mugun nauyinsa takeji... Zata iya cewa har suka isa yanda zasuje a d’arare take... Tanajin sanda ya ida parking ya bud’e central lock, Marliya ta kama marfin motar ta fice yayinda itakam Raihanah ta shiga kiciniya da seatbelt dan sanda zasu wuce road safety ya umarceta ta d’aura seatbelt, gaba d’aya sai kokawan zame jikinta take daga cikin seatbelt d’in... Sameer yai mata k’uri yana duban yanda take kokawa da seatbelt... A hankali ya d’an rank’wafo had’ida kai hannu yana k’ok’arin cire mata, yanda fuskokinsu sukai dap da juna ya haifar masu da fad’uwan gaba mai tsanani, dan gaba d’ayansu bugun zuciyarsu saida ya k’aru.... Tai saurin janye fuskarta k’irjinta bai daina bugu ba, gashi ya kasa janye jikinsa saima k’ura mata idanu da yai abin har sai ya soma bata tsoro, maiyasa zai mata haka...? A iyaka saninta shid’in ba mutumin banza bane... Tana tsaka da tinanin taji ya mik’e ya daidaita zamansa saman nasa kujeran tamkar wanda ya tuno wani abin... Murya a hankali taji yana furta “Kina iya fita, be careful next time kar Ki had’a seatbelt da rigarki...”
Ita dai kai kurum ta jinjina masa dan har yanzu jikinta a mace yake, da k’yar ta iya ficewa daga cikin motar k’afafunta sai rawa suke tamkar wanda zasu gaza d’aukarta....
Shiko Sameer jingina cikin motar yai had’ida lumshe idanu... God! Wai yau shi Sameer ke jin wani abu gameda wata mace ba Siyama ba..? Ya d’an ware idanunsa kad’an yana mai murmusawa a hankali, shi kad’ai yasan zancen da yakeda zuciyarsa saiko mak’aginsa...A haka su Engr suka k’araso, Sameer yai saurin daidaita kansa kana shima ya fito daga motar tasa, kai tsaye wajensu ya nufa suna gaisawa, take Engr ya soma introducing family d’insa ma Sameer... Muhibbah dai da alama hankalinta dik bai wajen dan tin a mota Shamzy ta isheta da waya bata d’agawa saidai ta danna a silent... K’arshe Shamzy text ta turo mata cewa dik yanda za’ai su had’u anjima dan Oga Bash yace kaya masu yawa zasu fitar a satin da za’a shiga, so itama dole ana buk’atarta.... Rausayar da idanu kurum tai sanda ta ida karance sak’on, yanzu dik basa samun attention d’inta sosai tinda ta soma prioritizing zaman aurenta sama da business d’insu... She can’t afford to lose this millions dole dik yanda za’ai tasan wata hanyar da zasuke had’uwa dasu Shamzy su Bash a store d’in Bash na saida garin siminti a zahiri amma a bad’ini waje ne na hada hadan miyagun k’wayoyi...
Shi kansa Engr ya kula gaba d’aya mind d’in Muhibba was somewhere else amma baice mata komai ba saima jerawa da sukai shida Sameer suka nufi cikin gidan suna fira, Sameer d’aukeda d’iyar Engr k’arama... Basu kaiga main k’ofar shiga gidan ba Daddy da Khalid suka iso, hakan yasa Engr da Sameer dakatawa dan gaisawa dasu Daddyn.... Muhibbah dake tsaye daga can b’angaren da suka parking motarsu tana amsa waya lokaci ta ida wayar nata tana sanarda Shamzy cewa gidan biological parents d’in Engr sukazo dan ya sanar da ita dik abindake faruwa cikin mota saidai bai bata labarin auren nasa ba dan shima magana ne mai zaman kansa...
Ya k’araso yana mai saka wayar a aljihu daidai sanda su Najma Irfaan da kuma Samha suka k’araso suna rungumesa suna fad’in “Daddy you look handsome..!” Ya d’auki Najma ya azata a kafad’a yayinda ya shafa kan Irfaan da Samha yace maza su shige Patrick ya bud’e masu mota....
Muhibbah ta raka yaran nata da muguwar kallo a cewarta munafunci ke sa suke nuna sunfi son ubansu sama da ita, bacin haka dik gayu da tasha basuce ta masu kyau ba sai Ubansu, munafukan banza kawai... Duban Engr ta d’an kumayi kana tace “Wai ina ne kam zamuje my Engr....?”
Ba tareda ya dubeta ba yace “It’s Sunday, after all... Idan munje zaki gani...” Daga haka sa kai yai ya shige Najma tana fad’in zata sha ice cream d’in cold stone...
Muhibbah dai tab’e baki tai kana tace a zuciyarta k’ila sabida weekend ne shiyasa zasu fita gaba d’aya da yaran tinda sun jima basu d’an fita haka ba kullum hidiman siyasa bai bari ya zauna, wata zuciyar kuma tace K’ila sabida misunderstanding d’in da kuka samu jiya ne kikai banza dashi shiyasa yau ya shirya maku fita to make it up to you... Ta wani murmusa ita kad’ai tana jin kanta, a hankali ta shiga buga kafad’anta tana fad’in “Ke d’in amanarsa ce dole dik yanda yakaiga fushi ya sauk’o ya baki hak’uri..!” Ta kuma murmusawa kafin ta d’au handbag da mayafinta saman sofa ta take masu baya...
SameenaAleeyou📚
*INDA RAI*
_...............DA RABO_
*95*
*©️Sameena Aleeyou✍🏽*
Suna tafe cikin motar yake sanar da ita yanda zasuje da kuma dalilin zuwan nasu, mamaki da al’ajabi ya cika Muhibbah... Gyara zama ta d’anyi tana dubansa sosai, lokaci guda take furta “Anya kuwa Excellency na... ‘Yan uwanka fah kace...? Mai yasa tintini basu nemeka ba, sai yanzu da sukaga ka zama mai fad’i aji, Nidai inaga kud’inka suke kwad’ayi babu wani ‘yanuwankan nan....”
Wane irin duba da yake aika mata ya sanyata had’iye sauran maganganun nata.... Ta d’an muskuta tana yatsina fuska lokaci guda taci gaba da fad’in “Ni dai shawari nake baka ka bincika da kyau, Frauds sunyi yawa...!”
Ba don shid’in bai kasance daga cikin maza masu dukan mata ba tabbas da ya shasshafeta da mari masu kyau, sannan yaransu dake bayan motar baiso su d’ago wani abu, shisa ma yai mata shiru, amma kam duba guda zaka masa ka fahimci tsananin b’acin rai da maganganun Muhibbah ya jefasa ciki, ta yaya zai kawo mata wannan labari mai dad’in gaske da yaso surprising d’inta dashi ta karb’i zancen a haka... A matsayinta na matarsa abokiyar rayuwarsa, tsawon shekarun nan ya zaci zatafi kowa nuna Farin cikinta, ya zaci zata tayasa Farin ciki bayan tulin shekarun nan da yayi cikin duhun rashin sanin ina asalinsa... Tareda ita akaita gwagwarmaya lokacin da ‘yan adawa sukaso b’ata masa suna cewa baida asali wanda badon Allah ya kiyaye ba da maganan yai tasiri, amma dik Muhibbah ta mance wannan, ya yana sanar da ita mahaifiyarsa na raye kuma ya sameta amma tana cewa Allah sa ba ‘yan wanki bane... Bai iya furta mata komai ba sai murza tafin hannunsa a hankali da yake sabida tsananin b’acin rai....
Ta d’an saci kallonsa had’ida tab’e baki kad’an, ita dai dikda cewa ya sanar da ita tinaninsa da ya b’ace sanda yake k’arami ya dawo amma bata yarda wad’annan mutanen ba dukiyar mijinta suke bibiya ba dan haka kawai taji sam bata yarda dasu ba, tin kafin tayi ido hud’u dasu taji ta tsanesu sosai...
*****
A tare Marliya da Raihanah suka gaidashi, ya amsa idanunsa kan Raihanar, ta masa kyau sosai, rigar ta amsheta... Har saida yaji ya kasa janye idanunsa daga barin dubanta, dikda cewa itad’in nata idanun a k’asa suke... Bud’e murya ya d’anyi kana yace “Kun shirya...?”
Suka jinjina kai a tare Marliya na fad’in “Eh mun shirya Yaya....”
Jinjina kai shima d’in yai kana yace “Alright kuje mota ku jiran barin duba Abbah Ina zuwa....”
Amsa mar sukai da toh kana yasa kai ya juya, sai sannan Raihanah ta d’ago ta dubesa sanda yake ficewa... Yau d’in shadda ce dakakkiyar wagambari mai ruwan sararin samaniya da akai mata d’inkin jampa jikinsa saiko hula zanna bukar mai kalan shud’i wato dark blue wanda ya dace da zarenda akai ado ma kayan dashi, yayi kyau matuk’a kaman wani sabon ango... Koda Sameer ya isa sashen Abbah bai tadda Abbah ba, dan rufe ya tadda sashen nasa, Toh Ina Abban ya tafi kuma ai yau d’in weekend ne....? Kasa samo amsar yai hakan ya sanyashi juyowa yana tinanin yanda Abbah ya tafi, daga nan sashen Mamani ya lek’a nan ma sammakal bata nan kaman yanda bak’in Kazaure ma dik sun tafi da alama wasu kuma suna b’angaren su Baffah Ado.... Ajiyan zuciya ya sauk’e a hankali kana ya nufo waje ya taddasu Raihanah, alamun bud’e mota da sukaji ya sanya Marliya saurin kaman marfin backseat ta shige abinta... Raihanah tai rau rau tana duban Marliya dake mata alama da ta shiga gaba.. Girgiza kai kurum tai dan ita yanzu ta gama gane Marliya neman magana ne da ita had’ida jin baki, haka nan ta kama marfin front seat d’in ta shige dik tana jinta wane iri... Itakam maiyasa dik sanda suka kasance tare take jin wannan yanayi...? Tambayar da ta tabbata bata da amsar sa, hakan sai ya tuna mata d’aukota daga islamiya da yai kwanakin baya, tana jin sanda ya daidaita saman driver’s seat bugun zuciyarta ya k’aru gaba d’aya a tak’ure take, Allah ya sani mugun nauyinsa takeji... Zata iya cewa har suka isa yanda zasuje a d’arare take... Tanajin sanda ya ida parking ya bud’e central lock, Marliya ta kama marfin motar ta fice yayinda itakam Raihanah ta shiga kiciniya da seatbelt dan sanda zasu wuce road safety ya umarceta ta d’aura seatbelt, gaba d’aya sai kokawan zame jikinta take daga cikin seatbelt d’in... Sameer yai mata k’uri yana duban yanda take kokawa da seatbelt... A hankali ya d’an rank’wafo had’ida kai hannu yana k’ok’arin cire mata, yanda fuskokinsu sukai dap da juna ya haifar masu da fad’uwan gaba mai tsanani, dan gaba d’ayansu bugun zuciyarsu saida ya k’aru.... Tai saurin janye fuskarta k’irjinta bai daina bugu ba, gashi ya kasa janye jikinsa saima k’ura mata idanu da yai abin har sai ya soma bata tsoro, maiyasa zai mata haka...? A iyaka saninta shid’in ba mutumin banza bane... Tana tsaka da tinanin taji ya mik’e ya daidaita zamansa saman nasa kujeran tamkar wanda ya tuno wani abin... Murya a hankali taji yana furta “Kina iya fita, be careful next time kar Ki had’a seatbelt da rigarki...”
Ita dai kai kurum ta jinjina masa dan har yanzu jikinta a mace yake, da k’yar ta iya ficewa daga cikin motar k’afafunta sai rawa suke tamkar wanda zasu gaza d’aukarta....
Shiko Sameer jingina cikin motar yai had’ida lumshe idanu... God! Wai yau shi Sameer ke jin wani abu gameda wata mace ba Siyama ba..? Ya d’an ware idanunsa kad’an yana mai murmusawa a hankali, shi kad’ai yasan zancen da yakeda zuciyarsa saiko mak’aginsa...A haka su Engr suka k’araso, Sameer yai saurin daidaita kansa kana shima ya fito daga motar tasa, kai tsaye wajensu ya nufa suna gaisawa, take Engr ya soma introducing family d’insa ma Sameer... Muhibbah dai da alama hankalinta dik bai wajen dan tin a mota Shamzy ta isheta da waya bata d’agawa saidai ta danna a silent... K’arshe Shamzy text ta turo mata cewa dik yanda za’ai su had’u anjima dan Oga Bash yace kaya masu yawa zasu fitar a satin da za’a shiga, so itama dole ana buk’atarta.... Rausayar da idanu kurum tai sanda ta ida karance sak’on, yanzu dik basa samun attention d’inta sosai tinda ta soma prioritizing zaman aurenta sama da business d’insu... She can’t afford to lose this millions dole dik yanda za’ai tasan wata hanyar da zasuke had’uwa dasu Shamzy su Bash a store d’in Bash na saida garin siminti a zahiri amma a bad’ini waje ne na hada hadan miyagun k’wayoyi...
Shi kansa Engr ya kula gaba d’aya mind d’in Muhibba was somewhere else amma baice mata komai ba saima jerawa da sukai shida Sameer suka nufi cikin gidan suna fira, Sameer d’aukeda d’iyar Engr k’arama... Basu kaiga main k’ofar shiga gidan ba Daddy da Khalid suka iso, hakan yasa Engr da Sameer dakatawa dan gaisawa dasu Daddyn.... Muhibbah dake tsaye daga can b’angaren da suka parking motarsu tana amsa waya lokaci ta ida wayar nata tana sanarda Shamzy cewa gidan biological parents d’in Engr sukazo dan ya sanar da ita dik abindake faruwa cikin mota saidai bai bata labarin auren nasa ba dan shima magana ne mai zaman kansa...