← Book details Inda Rai Da Rabo Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 192 OF 198

Sashe 192

Inda Rai Da Rabo Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Murmusawa ya kumayi k’aunarta na fizgarsa... Lokaci guda yake ci gaba da furta “You know, at first lokacinda na soma jin muryarki... I thought na fad’a soyayya da shirin da kike gudanawa ne... Daga bisani sai na zaci da muryarki na fad’a soyayya.... And now that I started to get to know you ... Sai na fahimci ba zallan muryarki bane ba kuma zallan kyaun fuskarki ko na jikinki ba... Zuciyarmu sun jima da had’uwa a wani waje na daban, basu samu damar kasancewa tare ba sai yanzu.... Zulfa’u I want you to know that I love you... So much... I’ve never felt like this for any woman before... A baya nayi zaton moment irin wannan bazai tab’a zuwa a rayuwata ba... Na karb’i k’addarata Muhibbah a matsayin matata... But as they say INDA RAI DA RABO.... Toh yau gashi ina gani, gani nan tareda matarda nakeso, nake kuma fatan na k’arashi rayuwata tareda ita... I’ll love you, take care of you and above all I’l respect you till my very last breath..!”Ya k’arashe cikin wane irin sanyin murya, Zulfa’u kam tuni hawaye sun shiga gangaro mata... She was like is this for real, shin Wai ita Zulfa’un ce yau namiji ke sanar da ita duka wad’annan, Zulfa’u da aka camfata mai Farin sawu... Zulfa’u data sha Uk’uba a rayuwar gidan aure har saida tai tinanin dik mazan duniya halinsu guda ne... Zulfa’un da tai tinanin babu sauran Farin ciki a rayuwarta nan gaba da zata tadda... Ashe irin wannan rana na zuwa da zata samu soyayya da girmamawan miji.... Tabbas ta yarda Allah shine mai canza al’amra a lokutan da yaso.... Ta kuma yarda da wannan kalma da akace INDA RAI to fah shakka babu akwai RABO... Mai rai kar ya zamto mai cire tsammani daga rahamar Ubangijinsa.... Tana fata da addu’a ga sauran ‘yanuwanta mata da suke experiencing what she went through a gidan aurenta na baya suma kar su cire Rai daga rahamar Ubangiji... Allah ya shirya mana mazajenmu ya sanya masu soyayyarmu da tausayinmu cikin zukatansu... Ya Ubangiji Allah ka zaunar damu lafiya tareda abokan rayuwarmu daka hukunta mana zama taredasu.... Ameen ya Rabbi..!

Ganin tana hawaye ya sanyashi kwantota cikin jikinsa yana lallashinta a hankali lokaci guda yana rikitata da salon k’aunarsa mai cikeda maturity....Yanayin da bazasu so wani abu ya datse masu ba, kaman daga sama wayarsa ta soma ruri... Cikeda jin nauyinsa ta kuma mak’ale kanta cikin k’irjinsa... Tana jin sanda yake amsa wayar da ko ba’a ce ba urgently ake nemansa... Jim ya d’anyi kana yace su tsammacesa nan bada jimawa ba...

Engr ya tallafo fuskarta sanda ya ida wayar kana yace “See, bazasu bar mutum ya huta ba... Wannan kafin ai swearing in a shiga office kenan... Kiyi hak’uri Zulfa’u I’ve to go, wannan shine mijin da kika aura mai hidimar Al’umma... Nasan ya kamata na ware maki lokacin ki... Amma kiyi hak’uri nai miki alk’awarin before ai swearing in lokutana gaba d’aya zan mallaka miki... Kafin na shiga aikin Office gadan gadan....”

Murmusawa ta d’anyi kana tace “I’ll always support you in everything, nasan rabin abubuwan da kake ba dan kanka kake ba... Dan jama’anka kake... Sabida haka, zaka sameni Ina mai k’arfafa maka gwiwa in sha Allah wajen ganin ka kimanta sauk’e nauyin da Allah ya d’aura maka...!”

Wani irin dad’I da sanyi ne ya lullub’e masa zuciya, ya kuma shafar fuskarta yace “What do I do without you.... Allah ya miki albarka....!”

Ta amsa da Ameen tana mai k’ok’arin mik’ewa tsaye take fad’in suje Ta Mar rakiya... Suna tafe yake fad’in gobe in sha Allah zata taimaka masa su sanar da yaransa batun mahaifiyarsu a natse yanda bazai affecting d’insu ba.. Zulfa’u ta jaddada masa idan dai wanna ne baida matsala... Har k’ofa tai masa rakiya yanda Ta hangi Akram da ‘yansandan da tuni an basa matsayinsa na governor elect sun nufi motoci a hanzarce suna k’amewa...

Akram na hangosu yai saurin sadda kansa dan harga Allah wane irin girman Zulfa’u yake ganina halin yanzu... Dole ne ma yaga girmanta a matsayinta na matar Uban gidansa...
Kai a k’asa ya k’araso harda risinawa yana gaida Zulfa’u, sai saman taji ashe ma Excellency Ma ya ambaceta da... Itakam this too formal for her Meye wani Excellency Ma, Wai ita Zulfa’un ce yau ta zama her Excellency.. Abin sai yanata mata wani banbarak’wai... Sallama suka kumayi da Engr yanda suka nufi mota shida Akram yanda Akram d’in Ke masa bayanin wasu abubuwa...

Zulfa’u kaw har yanzu wannan Excellency Ma da Akram ya ambaceta dashi bai daina mata banbarak’wai a kunne ba saima da Atika ta kirata tana ihu tana kiranta da her Excellency abin ya kuma mata bak’o
Zulfah tace “Zaki sani ne tinda ke yanzu kin zama ‘yar rashin mutunci ko ganinki ba’ayi....”

Atika tace “Allah huci ran her Excellency, zuwa ya zaman min dole ni da zanzo a bani komishina Ta mata...”
Sukai dariya a tare Zulfah na fad’in mai hali bai fasawa... Nan dai suka ci gaba da hiransu Zulfah na tambayarta labarin station d’insu... Gaskiya tayi kewarsu gaba d’aya...
Atika tace zasu hallaro suzo suyi masu murna.... Haka dai sukaci gaba da zance har dai daga bisani sukai sallama...

***

Bayan kwanaki biyu akai zaman kotun su Muhibbah yanda aka yanke masu shekaru goma sha biyar a gidan yari... Allah sarki abin akwai tausayi kam amma wannan shine sakamakon ayyukansu... Sanda za’a wuce da ita prison Engr ya k’araso ya buk’aci a barsu su gana.... Muhibbah ta d’ago idanunta masu zuban hawaye tana dubansa lokaci guda take furta “Ma’aruf ka yafe min... Ka yafe min dik abubuwan da nai maka a baya... Gidan yari shi ya kamaceni bayan rayukan mutane da dama da nayi ruining... Hak’ik’a shan miyagun k’wayoyi bazaikai d’an Adam ga komai ba face tab’ewa... Ta’ammudi da miyagun k’wayoyi ya taka rawa wajen sauya min kwanya da tinani har takaiga na ballagazantar da aure na da kuma ‘ya’ya na.... Nayi watsi da rufin asirin da Ubangijina yai min... Yau ga halinda na tsinci kaina ciki... Ina rok’on Allah yasa hakan ya zama wa’azi ga masu hali irin nawa... Ma’aruf yau ina rok’onka gafara dan Allah ka yafe min...!” Ta k’arashe tana mai had’e hannayenta biyu dake d’aure cikin handcuff waje guda alamun rok’o....

Girgiza kai yake hawayen da yake mak’alewa suna kuma gangaro masa lokaci guda ya kamo hannayen nata yana furta “Muhibbah na yafeki duniya da lahira... And about our children zan kula dasu da dikkan iyawata... Fatana shine Allah yasa wannan ya zamto sanadin shiriryarki Muhibbah... Zan dinga kawo miki yaranmu lokaci zuwa lokaci suna kawo miki ziyara... This is a promise... Na fad’a miki bazan abandoning d’inki ba sabida dukanmu ‘yanadam ne masu kure... We will face this together..”

Murmushi ta d’anyi kana tace “Na gode Excellency na....Na manta ban congratulating d’inka ba... Congratulations Allah ya tayaka rik’o dama kai d’in na Al’umma ne... May Allah guide you through...!”

Engr ya amsada Ameen kana yace “You take care of yourself....!”
Jinjina masa kai tai tana murmushi lokaci guda tana share hawayen da suka zubo mata daidai sanda ganduroba mace ta janyota suka shige....

Washe gari akai zaman nasu Baba Alhaji ma yanda Hafiz da ba’ai tsammani ba yaje shi ya bada shaida... Zo Kaga yanda Baba Alhaji yake kuka yana murna, haka ya rungumi Hafiz su duka biyu suna hawaye... Abbah na waje na jiransa, Baba Alhaji yana hango Abbah ya tafi ya rungumesa su duka biyun suna hawaye gwanin ban tausayi... Lokaci ne na yafewa juna... Komai yai tsanani yana tareda sauk’i.... Rahamar Ubangiji ya lullub’esu.... ‘Yan uwan da suka taso cikin sab’ani da juna yau gasu nan k’ark’ashin inuwa guda... Zumunci al’amari ne mai girman gaske... ‘Yan uwa kada muyi wasa da zumunci... Musaka sharri da Alkhairi, mu kuma zamto masu yad’a alkhairi da yafiya had’ida soyayyan junanmu a tsakani....

Haka suka d’unguma suka nufi gida cikeda Farin ciki, k’annensu su Baffah Ado da Baffah Wada suna hango ‘yan uwan nasu suka tafi suka rungumesu suna masu nuna Farin cikinsu, haka Baba Alhaji yaita godiya wa Abbah yana fad’in ya basa girman, kuma ya yarda Allah shike d’aukaka wanda yaso a cikin Al’umma... A gida guda sai Allah ya d’aga k’arami Daga cikinku ya bashi wani mulki ko arziki ba don komai ba sai dan hakan ne yaso ta kasance...

Abbah kaw cewa yai har gobe Baba Alhaji shine dai gaba dashi babban yayansu... Suna nan a haka a k’ofar gidan Baffah Ado da ya ida waya ya k’araso masu da labari mai dad’i cewa an sami Mamani....

SameenaAleeyou📚

*INDA RAI*
_............... DA RABO_

*112*

*©️Sameena Aleeyou...*

Daga Abbah har Baba Alhaji har suna had’e baki wajen tambayar Baffah Ado ina Mamanin take... Baffah Ado ya labarta masu yanda akai, ashe gidan d’iyar k’awarta Hajiya Marka ta tafi dashike Ita d’iyar k’awar tata k’awar Matar Baffah Ado ne, kuma Mamani ta rok’esu kan cewa kada su sanar da yaranta ga yanda take ita kaw d’iyar Hajiya Marka taga kullum wannan tsohuwa cikin damuwa da kuka take ga shekaru da suka ja, hakan ba daidai ne ga lafiyarta ba, wannan dalili yasa ta yanke shawarin sanar da yaranta...
Chapter 192 · 0% Book details