Sashe 27
Inda Rai Da Rabo Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ya kai dubansa ga kujeran data zauna nan ya hangi note book d’inta ta mance kuma da alama littafi ne mai d’aukeda courses daban daban...
Murmushi ya sake a hankali kafin yaja motarsa ya wuce yasan dole ta nemeshi ko don littafinta data mance....
Daga nan waya yayiwa Sameer yaji ko yana gida su gaisa, Sameer sai mamaki yake mai yake kawo Khalid Kano akai akai, nan dai Sameer d’in ke sanar dashi bai gida yana hospital...
****
Mamy na hankalce da yanayin Nabilar, duk yanda akai wani abun na damunta...
Suna zaune gaba d’aya a parlor da magrib Mamy ke tambayarta meke damunta...
“Mamy ba komai....” Ta fad’i tana mai shan jinin jikinta...
Jinjina kai Mamy tai kana tace “Idan ya dame ki kya fad’i...”
Nabilah da Marliya suka kalli juna Marliya na k’ok’arin had’iye dariyarta....
Misalin k’arfe 10pm ta gama shirin baccinta ta d’auko wayarta da niyyan yin assignment d’inta ta nemi littafinta ta rasa...
Cikin sauri ta shiga neman layin Yusrah tana tambayarta idan littafinta na tareda ita...
“Yusrah tace “Gaskiya baya wajena ban tsammanin na wajensu Safwan ma....”
Nabilah ta dafe kanta tana fad’in “Ya Salam, toh ina na jefar...”
Yusrah tace “Hey wait... Could it be a mortar mutumin nan kika bari ba...?”
Gaban Nabila ya yanke ya fad’i, saurin rintse idanunta tai tana tunanin tabbas ta yiwu a motar tasa ta mance...Ya Salam yanzu ya zatai ta ina zata soma nemansa...
Lambar da ya kirata dashi takai kai ta tsura masa idanu na lokaci... Kaman zatai dialing sai kuma ta fasa tai jifa da wayar saman gado tana mai jin haushin kanta dama ta yarda ta shiga motar tasa...
Cikeda masifa ita kad’ai take fad’in “No wllhi bazan kiraka ba... Oh I hate you..!” Ta k’arashe sakin k’ara...
Marliya dake bacci gadonta daga can gefe bud’e idanu tai a hankali tana tambayar Nabila meke faruwa....
A dak’ile Nabila ta kalleta ba tareda tace komai ba....
Kwanciya kawai tai don bazata iya yin assignment d’inba tinda duk working d’in na cikin littafinta...
Sanin cewa Mr Edward bai bari a zauna masa a aji ba tareda ganin littafinka ba kuma kana rubutu ya sata yanke shawarin kiran d’an rainin hankalin nan...
Yana ganin wayarta murmushi ya kufce masa, shi kad’ai yana kallon screen d’in wayar a zuciyarsa yana furta “I know you’ll call...”
Saida taji kaman ta katse kiran don takaici kafin ya d’aga..
Kishingid’a ya kumayi kana yace “So why is miss Grumpy calling me now..? Did you call to give me a goodnight scold or to ask me about my wound again......?”
Fuzar da iska tai kana tace “Don’t get wrong ideas, I call because I think I left my book in your car....”
Murmushi yayi don d’an rabuwan da sukayi na wasu mintoci har yaji kewar masifarta...
Saida ya d’an d’auki lokaci kaman bazaice komai ba yana iya jiyo hucinta kana yace “Oh really... Sabida tsaban bakiso deal d’inmu ya k’are shine saida kikayi kikasan yanda kika bar book d’inki a mota ta... Alright since you insist on seeing me zan kawo miki littafinki but as you can see is pretty late now, ko babu matsala...”
Murya na rawa kaman mai shirin kuka take fad’in “Think whatever you want to think nidai ka kawo min littafina...”
Mik’ewa sosai yayi ya zauna yana mamakin canzawan muryarta kana yace “Alright fine ki karb’i littafinki gobe a makaranta..”
Ta sauk’e ajiyan zuciya ba tareda tace komai ba,shiru ya gifta tsakaninsu na d’an lokaci kowa da abinda yake tunani kana yace “May I know where to keep the notebook...?” Wannan karon cikin kashe murya yayi maganar...
A sanyaye tace dashi “I’ve class by 8, just come straight to auditorium....” Daga nan bata kuma cewa komai ba sai katse wayar da tai...
Kallo yabi wayar dashi murmushi saman fuskarsa kafin ya shiga tura mata sak’o
_Too bad I’m not used to waking up early..._
Girgiza kai kurum tai had’ida jifa da wayan tasan wannan baza’a tab’a abin arziki dashi ba...
Washe gari sai raba idanu take tana neman ta yanda zata hangosa gashi har Malamin ya shiga aji...
Yusra na hankalce da ita don tasan kwanan zancen....
Mr Edward ya soma going round ya hangi mutum tsaye bakin k’ofa yana taking excuse
Nabila sai raba idanu take don tasan Allah ne ya taimaketa Mr Edward bai k’araso ta wajensu ba don bawai fad’ansa take tsoro ba attendance ne kawai bataso ta rasa...
Mr Edward ya baiwa mutumin izinin shigowa, daga mazan har matan fad’in had’uwarsa suke...
Nabila kam kanta na k’asa batasan wainar da ake toyawa ba saida Yusra ta shiga jjjigata tana fad’in “Ke tashi tashi kiga waye a nan...”
Nabila na d’ago kai sukai idanu hud’uda Khalid yana maganawa Mr Edward a hankali alamun ita yake tambaya...
“Oh there she’s mr...” Ya k’arashe yana pointing d’inta da littafin...
Jinjina kai Mr Edward yayi kana ya kirawo Nabila tazo ta amshi littafinta, gaba d’aya idanu akanta ta mik’e ta nufi gaban hall, kallon kallo sukewa juna har ta amshi littafin kafin ta koma ta zauna...
Suka kuma yin sallama da Mr Edward Khalid ya fice, sai mamaki take don batayi zaton ganinshi da uwar safiyan nan ba...
Tana zama Yusrah ta shiga mintsilinta tana fad’in “I told you if you matters to him zai kawo miki... see gashi yazo, dukda dai nada jin kai amma kun dace...”
Harara kawai Nabila ta aika mata kana ta shiga bud’e littafinta da tuni ya kama k’amshin turaren Khalid...
***
A daren Daddy yayi wayawa Khalid ya sanar dashi maza ya dawo Kaduna something came up at the company ana buk’atarsa...
Wasa wasa sabo na neman shiga tsakanin Nabila da Khalid dukda cewa ko ya kirata fad’a kawai suke, duk randa bai kira ba sai taji wani iri sai taji kaman ta kirashi koda zasuyi fad’an, har yanzu cikinsu babu wanda ya yarda yanajin wani abu gameda d’an uwansa..
Bikin Hafiz ne ya taso gadan gadan don tuni an shiga satin bikin, saidai har wannan lokaci Zulfah batada labari, Aunty B ce ta kirawo Mamy tana bata baki cewa kar ta d’aga hankalinta gameda Zulfah ma zatai mata magana yanda zata fahimta...
Mamy tai mata godiya sannan ta d’an sami sauk’i cikin zuciyarta...
Hakan kuwa akayi Aunty B tai maganawa Zulfa’u cikin natsuwa da kwantar da hankali had’ida nusar da ita duk abinda Allah ya k’addarawa bawa jarabawa ne, hak’uri shine riban rayuwar zaman duniya...
Dukda tawakkali da Zulfah tai labarin auren Hafiz sosai ya d’aga mata hankali, taci kuka har ta gode Allah k’arshe ta fawwala wa Allah lamuranta...
Ranar da ake jira tazo ranar auren Sawwama da Hafiz, tun safe marok’a ke busa algaita a gidan Magajiya, banda kad’e kad’e da raye raye ba’a komai...
A b’angaren Hajiya ma babu sauk’i d’anta zaiyi auren gata auren jin dad’i ba auren wahala ba irin wanda yayi a baya, basu samu sun koma wajen Malam nakan buzu ba sabida hidiman auren Hafiz da yasha kansu...
Da yammaci Magajiya ta rufo d’iyarta ta kawo don ko jiran ‘yan d’aukan amarya bata tsayayi ba kafin ‘yan d’auka suzo munafukan unguwarsu su zayyane masu wacece Sawwama a fasa aure...
Su Hajiya suna tsaka da hidima sai sautin gud’e gud’e suka soma jiyowa Sa’adu Gurmi na gefe yana kad’ada gurmi Magajiya na gaba tana taka rawa d’aurin kallabi a gefe ga mayafi a kafad’a, tana tafe tana rawa har k’asa k’awayenta na biyeda ita rik’eda Sawwama cikin lullub’i..
Kowa ya daina abinda yake yana kallon ikon Allah...
SameenaAleeyou 📚
*INDA RAI*
_...............DA RABO_
*25*
*©Sameena Aleeyou...✍🏽*
Fatan Alheri gareku🤝
Haleematu Maikeke
Sadiya Auwal Z
BabyMahe
Farida S Maina
Maman Najwa
Deejoh Omar
Fatee Beni
Maryam Mu’azu
Alherin Allah yakai maku🥰
Hajiya da kanta zaune dirshan tai tsakar gidan tana kallon ikon Allah, ita ko a fina finai bata tab’a gani ko jin yanda akace uwar amarya ta rufo d’iyarta ta kawo ba tareda anje an amshi amarya ba...
Aunty Lami ta d’an tab’a Hajiya kana tace “Haule yau ina ganin bariki tsirarta, yo ni duk zaman danayi a bariki ai ban tab’a cin karo da irin haka ba, anya kaw Haule ba ruwan dafa kanki kika d’ebo ba...?”
Hajiya ta yatsina fuska kana tace “Haba Lami ya kike magana haka kaman baki sanni ba, yo ni ai walki ce daidai da uban kowa, ke nifah duk wanda sukazo dashi toh billahillazi shi zamuyi, kinga kafin su raina mana tashi mu tayasu tik’ar rawar, don wllhi nafi kowa jin dad’in auren nan...” Ta k’arashe tana mai shan d’amara da mayafinta... Haba nan fah fili ya kuma kacamewa uwar ango da amarya sai tik’ar rawa suke kowacce tanaso ta burge, idan Magajiya tayi k’asa Hajiya tai sama haka zalika idan Hajiya tai k’asa Magajiya tai sama nan fah k’awayen ko wacce ta shiga burge abokiyarta da lik’i... Mai Gurmi kaw mai zaiyi banda yaci gaba da kad’a masu gurmi yana washe su had’ida tattaran kud’ad’ensa....
Saida suka tik’i rawa sukai lis kafin aka shige da Sawwama parlorn Hajiya aka soma bada amana....Su Sahariyya suna daga waje ana faman cashewa Yayansu yayi auren gata auren masuyi ba aure irin na Zulfah ba da aka lik’a masa jaraba....
A can gidan Aunty B kuwa Zulfah na zaune tayi jigum tana tunanin rayuwa, a kullum tunaninta da mafarkinta shine INDA RAI DA RABON aurensu ya d’ore itada Ya Hafiz, tabbas ba auren soyayya sukai ba aurene na had’i tsakanin iyaye amma har k’asan zuciyarta tanajin zafin ace ta rabu da mijinta kuma uban ‘yarta, taso ace sun rayu tare sun raini d’iyarsu tare sai dai Allah bai k’addara hakan ba, ta kuma yi imani zab’in Allah shine zab’i na k’warai... Bata tab’a kawowa Ya Hafiz bazai maidata d’akinta ba bata tunanin saidai taji labarin aurensa daga sama ba sai gashi duk hakan ne ta kasance, tabbas mutuwar aure jarabawane mai tsananin wuya koda ace baka k’aunar mijin, fatanta Ubangiji ya bata ikon cin wannan jarabawa bazata kuma ta daina addu’a wa d’iyarta ba Allah ya inganta mata rayuwarta a duk yanda zata tsinci kanta....
Murmushi ya sake a hankali kafin yaja motarsa ya wuce yasan dole ta nemeshi ko don littafinta data mance....
Daga nan waya yayiwa Sameer yaji ko yana gida su gaisa, Sameer sai mamaki yake mai yake kawo Khalid Kano akai akai, nan dai Sameer d’in ke sanar dashi bai gida yana hospital...
****
Mamy na hankalce da yanayin Nabilar, duk yanda akai wani abun na damunta...
Suna zaune gaba d’aya a parlor da magrib Mamy ke tambayarta meke damunta...
“Mamy ba komai....” Ta fad’i tana mai shan jinin jikinta...
Jinjina kai Mamy tai kana tace “Idan ya dame ki kya fad’i...”
Nabilah da Marliya suka kalli juna Marliya na k’ok’arin had’iye dariyarta....
Misalin k’arfe 10pm ta gama shirin baccinta ta d’auko wayarta da niyyan yin assignment d’inta ta nemi littafinta ta rasa...
Cikin sauri ta shiga neman layin Yusrah tana tambayarta idan littafinta na tareda ita...
“Yusrah tace “Gaskiya baya wajena ban tsammanin na wajensu Safwan ma....”
Nabilah ta dafe kanta tana fad’in “Ya Salam, toh ina na jefar...”
Yusrah tace “Hey wait... Could it be a mortar mutumin nan kika bari ba...?”
Gaban Nabila ya yanke ya fad’i, saurin rintse idanunta tai tana tunanin tabbas ta yiwu a motar tasa ta mance...Ya Salam yanzu ya zatai ta ina zata soma nemansa...
Lambar da ya kirata dashi takai kai ta tsura masa idanu na lokaci... Kaman zatai dialing sai kuma ta fasa tai jifa da wayar saman gado tana mai jin haushin kanta dama ta yarda ta shiga motar tasa...
Cikeda masifa ita kad’ai take fad’in “No wllhi bazan kiraka ba... Oh I hate you..!” Ta k’arashe sakin k’ara...
Marliya dake bacci gadonta daga can gefe bud’e idanu tai a hankali tana tambayar Nabila meke faruwa....
A dak’ile Nabila ta kalleta ba tareda tace komai ba....
Kwanciya kawai tai don bazata iya yin assignment d’inba tinda duk working d’in na cikin littafinta...
Sanin cewa Mr Edward bai bari a zauna masa a aji ba tareda ganin littafinka ba kuma kana rubutu ya sata yanke shawarin kiran d’an rainin hankalin nan...
Yana ganin wayarta murmushi ya kufce masa, shi kad’ai yana kallon screen d’in wayar a zuciyarsa yana furta “I know you’ll call...”
Saida taji kaman ta katse kiran don takaici kafin ya d’aga..
Kishingid’a ya kumayi kana yace “So why is miss Grumpy calling me now..? Did you call to give me a goodnight scold or to ask me about my wound again......?”
Fuzar da iska tai kana tace “Don’t get wrong ideas, I call because I think I left my book in your car....”
Murmushi yayi don d’an rabuwan da sukayi na wasu mintoci har yaji kewar masifarta...
Saida ya d’an d’auki lokaci kaman bazaice komai ba yana iya jiyo hucinta kana yace “Oh really... Sabida tsaban bakiso deal d’inmu ya k’are shine saida kikayi kikasan yanda kika bar book d’inki a mota ta... Alright since you insist on seeing me zan kawo miki littafinki but as you can see is pretty late now, ko babu matsala...”
Murya na rawa kaman mai shirin kuka take fad’in “Think whatever you want to think nidai ka kawo min littafina...”
Mik’ewa sosai yayi ya zauna yana mamakin canzawan muryarta kana yace “Alright fine ki karb’i littafinki gobe a makaranta..”
Ta sauk’e ajiyan zuciya ba tareda tace komai ba,shiru ya gifta tsakaninsu na d’an lokaci kowa da abinda yake tunani kana yace “May I know where to keep the notebook...?” Wannan karon cikin kashe murya yayi maganar...
A sanyaye tace dashi “I’ve class by 8, just come straight to auditorium....” Daga nan bata kuma cewa komai ba sai katse wayar da tai...
Kallo yabi wayar dashi murmushi saman fuskarsa kafin ya shiga tura mata sak’o
_Too bad I’m not used to waking up early..._
Girgiza kai kurum tai had’ida jifa da wayan tasan wannan baza’a tab’a abin arziki dashi ba...
Washe gari sai raba idanu take tana neman ta yanda zata hangosa gashi har Malamin ya shiga aji...
Yusra na hankalce da ita don tasan kwanan zancen....
Mr Edward ya soma going round ya hangi mutum tsaye bakin k’ofa yana taking excuse
Nabila sai raba idanu take don tasan Allah ne ya taimaketa Mr Edward bai k’araso ta wajensu ba don bawai fad’ansa take tsoro ba attendance ne kawai bataso ta rasa...
Mr Edward ya baiwa mutumin izinin shigowa, daga mazan har matan fad’in had’uwarsa suke...
Nabila kam kanta na k’asa batasan wainar da ake toyawa ba saida Yusra ta shiga jjjigata tana fad’in “Ke tashi tashi kiga waye a nan...”
Nabila na d’ago kai sukai idanu hud’uda Khalid yana maganawa Mr Edward a hankali alamun ita yake tambaya...
“Oh there she’s mr...” Ya k’arashe yana pointing d’inta da littafin...
Jinjina kai Mr Edward yayi kana ya kirawo Nabila tazo ta amshi littafinta, gaba d’aya idanu akanta ta mik’e ta nufi gaban hall, kallon kallo sukewa juna har ta amshi littafin kafin ta koma ta zauna...
Suka kuma yin sallama da Mr Edward Khalid ya fice, sai mamaki take don batayi zaton ganinshi da uwar safiyan nan ba...
Tana zama Yusrah ta shiga mintsilinta tana fad’in “I told you if you matters to him zai kawo miki... see gashi yazo, dukda dai nada jin kai amma kun dace...”
Harara kawai Nabila ta aika mata kana ta shiga bud’e littafinta da tuni ya kama k’amshin turaren Khalid...
***
A daren Daddy yayi wayawa Khalid ya sanar dashi maza ya dawo Kaduna something came up at the company ana buk’atarsa...
Wasa wasa sabo na neman shiga tsakanin Nabila da Khalid dukda cewa ko ya kirata fad’a kawai suke, duk randa bai kira ba sai taji wani iri sai taji kaman ta kirashi koda zasuyi fad’an, har yanzu cikinsu babu wanda ya yarda yanajin wani abu gameda d’an uwansa..
Bikin Hafiz ne ya taso gadan gadan don tuni an shiga satin bikin, saidai har wannan lokaci Zulfah batada labari, Aunty B ce ta kirawo Mamy tana bata baki cewa kar ta d’aga hankalinta gameda Zulfah ma zatai mata magana yanda zata fahimta...
Mamy tai mata godiya sannan ta d’an sami sauk’i cikin zuciyarta...
Hakan kuwa akayi Aunty B tai maganawa Zulfa’u cikin natsuwa da kwantar da hankali had’ida nusar da ita duk abinda Allah ya k’addarawa bawa jarabawa ne, hak’uri shine riban rayuwar zaman duniya...
Dukda tawakkali da Zulfah tai labarin auren Hafiz sosai ya d’aga mata hankali, taci kuka har ta gode Allah k’arshe ta fawwala wa Allah lamuranta...
Ranar da ake jira tazo ranar auren Sawwama da Hafiz, tun safe marok’a ke busa algaita a gidan Magajiya, banda kad’e kad’e da raye raye ba’a komai...
A b’angaren Hajiya ma babu sauk’i d’anta zaiyi auren gata auren jin dad’i ba auren wahala ba irin wanda yayi a baya, basu samu sun koma wajen Malam nakan buzu ba sabida hidiman auren Hafiz da yasha kansu...
Da yammaci Magajiya ta rufo d’iyarta ta kawo don ko jiran ‘yan d’aukan amarya bata tsayayi ba kafin ‘yan d’auka suzo munafukan unguwarsu su zayyane masu wacece Sawwama a fasa aure...
Su Hajiya suna tsaka da hidima sai sautin gud’e gud’e suka soma jiyowa Sa’adu Gurmi na gefe yana kad’ada gurmi Magajiya na gaba tana taka rawa d’aurin kallabi a gefe ga mayafi a kafad’a, tana tafe tana rawa har k’asa k’awayenta na biyeda ita rik’eda Sawwama cikin lullub’i..
Kowa ya daina abinda yake yana kallon ikon Allah...
SameenaAleeyou 📚
*INDA RAI*
_...............DA RABO_
*25*
*©Sameena Aleeyou...✍🏽*
Fatan Alheri gareku🤝
Haleematu Maikeke
Sadiya Auwal Z
BabyMahe
Farida S Maina
Maman Najwa
Deejoh Omar
Fatee Beni
Maryam Mu’azu
Alherin Allah yakai maku🥰
Hajiya da kanta zaune dirshan tai tsakar gidan tana kallon ikon Allah, ita ko a fina finai bata tab’a gani ko jin yanda akace uwar amarya ta rufo d’iyarta ta kawo ba tareda anje an amshi amarya ba...
Aunty Lami ta d’an tab’a Hajiya kana tace “Haule yau ina ganin bariki tsirarta, yo ni duk zaman danayi a bariki ai ban tab’a cin karo da irin haka ba, anya kaw Haule ba ruwan dafa kanki kika d’ebo ba...?”
Hajiya ta yatsina fuska kana tace “Haba Lami ya kike magana haka kaman baki sanni ba, yo ni ai walki ce daidai da uban kowa, ke nifah duk wanda sukazo dashi toh billahillazi shi zamuyi, kinga kafin su raina mana tashi mu tayasu tik’ar rawar, don wllhi nafi kowa jin dad’in auren nan...” Ta k’arashe tana mai shan d’amara da mayafinta... Haba nan fah fili ya kuma kacamewa uwar ango da amarya sai tik’ar rawa suke kowacce tanaso ta burge, idan Magajiya tayi k’asa Hajiya tai sama haka zalika idan Hajiya tai k’asa Magajiya tai sama nan fah k’awayen ko wacce ta shiga burge abokiyarta da lik’i... Mai Gurmi kaw mai zaiyi banda yaci gaba da kad’a masu gurmi yana washe su had’ida tattaran kud’ad’ensa....
Saida suka tik’i rawa sukai lis kafin aka shige da Sawwama parlorn Hajiya aka soma bada amana....Su Sahariyya suna daga waje ana faman cashewa Yayansu yayi auren gata auren masuyi ba aure irin na Zulfah ba da aka lik’a masa jaraba....
A can gidan Aunty B kuwa Zulfah na zaune tayi jigum tana tunanin rayuwa, a kullum tunaninta da mafarkinta shine INDA RAI DA RABON aurensu ya d’ore itada Ya Hafiz, tabbas ba auren soyayya sukai ba aurene na had’i tsakanin iyaye amma har k’asan zuciyarta tanajin zafin ace ta rabu da mijinta kuma uban ‘yarta, taso ace sun rayu tare sun raini d’iyarsu tare sai dai Allah bai k’addara hakan ba, ta kuma yi imani zab’in Allah shine zab’i na k’warai... Bata tab’a kawowa Ya Hafiz bazai maidata d’akinta ba bata tunanin saidai taji labarin aurensa daga sama ba sai gashi duk hakan ne ta kasance, tabbas mutuwar aure jarabawane mai tsananin wuya koda ace baka k’aunar mijin, fatanta Ubangiji ya bata ikon cin wannan jarabawa bazata kuma ta daina addu’a wa d’iyarta ba Allah ya inganta mata rayuwarta a duk yanda zata tsinci kanta....