Sashe 35
Inda Rai Da Rabo Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Siyama ta bita da kallon mamaki kana tace “But Ammi.... Ba kece mai min fad’an shan magungunan hana d’aukan ciki ba, idan ban mance ba akan na zubda ciki saida kika kwana biyu bakimin magana.... Why the sudden change of mind...?”
Hannayenta Ammi ta rik’o kana tace “I’ve my reasons Siyama, sannan ki sani duk wani dalilina don na kareki ne....”
Wannan karon da tsananin mamaki Siyama ke duban mahaifiyarta....
“Ammi you making me nervous.... Is there anything I need to know...?”
K’uri Ammi ta mata kana ta girgiza kai a hankali tace “No, babu komai.... I just feel like supporting your idea ne as my daughter.... Ki tashi ki tafi gidanki and make sure kinci gaba da shan magani....”
Jiki a sanyaye Siyama ta mik’e tana mamakin mahaifiyar tata, toh meyasa ta canza ra’ayinta, mai Momyn Sameer ta fad’i mata....?
Still tai tana murza mabud’an motarta a hankali kafin tasa kai ta fice daga gidan bata zarce ko ina ba sai gidansu Aminiyarta Laila....
***
Sultan ya dube shi a karo na biyu kana ya girgiza kai yace “Sameer ko zaka kwana kana fad’a min babu abinda ke damunka... Just tell me please maybe I can help...”
Shafe fuskarsa yayi da duka tafukan hannayensa kana yace “Sultan how does it feel ace mutanen da kafi so a rayuwarka sun maka k’arya...?”
Sultan ya gyara zama had’ida murmusawa an tab’o yanda ke masa k’aik’ayi...
Kafad’ar Sameer ya dafa kana yace “Sameer this life has never been fair, and it will never be... Ka yarda.....?”
D’ago rinannun idanunsa yai yana duban Sultan d’in kana ya jinjina kai yace “Yeah na yarda....”
“Mai Siyama ta maka...?” Sultan ya jefo masa tambayar kai tsaye, shiru ne na d’an lokaci ya gifta kana ya girgiza kai yace “It’ll be better if we don’t talk about it...”
Sultan ya masa k’uri yana nazarinsa, jin jina kai yai kana yace “Is ok if you don’t wanna talk about it... But whenever you feel like, don’t forget that I’m here bro....”
Jinjina kai Sameer yai yana mai furta “Na gode abokina...”
Sun d’an d’ibi lokaci Sultan ke jansa da fira dukda ba wani amsawa Sameer d’in keyi ba, yamma lis Sameer yayiwa Sultan sallama ya wuce...
Tafiyar Sameer da kad’an wayar Sultan ta d’auki ruri, ganin mai kiran ya sanyashi sakin murmushi kana ya d’aga yana mai furta “Kaman nasan update d’in da zaki bani...”
Shiru ya d’an biyo baya alamu magana ake daga d’aya b’angaren....
Sultan ya kuma murmusawa kana yace “Saura k’iris burina ya cika, idan kuwa ya cika kada ki manta kinada babban kyauta domin kaw kin taka muhimmiyar rawa...”
Ya kuma murmusawa yana mai mik’ewa tsaye had’ida sakala hannu guda cikin aljihu alamun yana sauraren mai magana daga d’aya b’angaren...
A hankali yake shafan sajensa kana yace “INDA RAI burina gab yakeda cika...”
Ya saki dariya mai ‘yar sauti kafin sukai sallama ya katse wayar....
***
Kano
Nabila ta d’aga appointment letter d’in tana kuma duba cikeda murna, baki har kunne take fad’in “Addah Zulfah gaskiya nai miki murna ubangiji yasanya alkhairi ya kuma sa a fara a sa’a...”
Zulfah ta murmusa tana duban ‘yar uwar tata cikeda k’auna tace “Ameen Nabyn Mamy, amma ai ba yanzu zan soma zuwa ba sai na gama iddah...”
Nabilah ta d’an tab’e fuska tace “Oho dai at least kema zaki tsara rayuwarki yanzu babu tak’urin Yaya Hafiz balle na Hajiya da watsattsun k’annensa...”
Murmushin k’arfin hali Zulfah tai ba tareda ta furta komai ba...
Nabila ta dubeta a kaikaice tace “Kar kicemin har yanzu tunaninsa da mafarkin komawa gidansa kike..?”
Murmushin Zulfah ta sakeyi wanda da gani mai ciwo ne kana tace “Nabilah kenan, Yaya Hafiz bazan tab’a goge shi cikin tarihin rayuwata ba amma ki sani kaman yanda na ambaci tarihi tabbas ya zama tarihin, he’s already in the past, sannan koda ace babu dangantaka na zumuntan jini tsakaninmu aure ya had’a sannan kar ki mance akwai rabo tsakaninmu, Kausar ta kuma had’amu Nabilah... Hafiz Uban d’iyata ce Nabilah, we cannot change that...”
D’an rausayar da idanu Nabila tai kana tace “Haka ne amma nidai bazan daina k’irgen sauran kwanakin da suka rage aurensa ya sauk’a gaba d’aya akanki ba, Kausar kuma muddin Raiha na nan banida haufin zata kula da ita fatana dai kar yace zai d’auki d’iyarsa ya damk’a hannun wancan ‘yar tashan matar tasa ba...”
Zulfah tai shiru tana sauraren Nabila domin kaw ta tab’o mata yanda ke tsananin ciwo a gareta, duk randa ta tuna Hafiz na iya damk’ar rik’on d’iyarta hannun wata matar...
Kaman Nabilah tasan abinda take tunani ta d’an dafata ta shiga calming d’inta, a haka Aunty B ta shigo ta taddasu tana fad’in “Ga k’osai ‘yar la’asar da zafinshi yanzu Tatu ta sauk’e...” Ta k’arashe tana dire masu k’aramar parantin...
Aiko nan Nabilah ta dirk’o k’asa ta shiga cin k’osan tana dandalan barkono, Aunty B tace “Kidaici barkonon nan a hankali don zafi ne dashi...”Takai dubanta ga Zulfah tace “D’iyata zakisha kunun ne ta dama kafin ta tafi...”
Zulfah ta girgiza kai tace “A’a Aunty zan sha kunun ayan d’azu dai inaga dakwai saura a fridge..”
Ai bata gama rufe baki ba Nabilah ta mik’e ta nufi fridge tana fad’in “Su Aunty an iya waraya d’iyarki kawai kika sani, dama akwai kunun aya a gidan shine ko amin tayi toh wllhi rabona ne nasha nayi guzirin sauran..”
Aunty B tace “Eh dai so so ne amma son kai yafi, kiji na fad’a miki nafison Zulfah tah..”
Zulfah sai dariyansu take itako Nabila sai kwankwad’an kunun ayarta take tana lumshe idanu ko kulasu batai ba... Wayarta dake ringing ne ya d’auki hankalinta, ta nufo handbag d’inta a guje tana lalumen wayar take fad’in “Toh Mamyna na nemana nima, taga yamma tayi....” Aya ta sakawa kalaman nata ganin mai kiranta, tasan ba kowa bane illa bugun zuciyarta, domin kaw ganin bak’uwar lamba d’aukeda had’add’un lambobi yasa taji k’irjinta na bugawa, tasan shi kad’aine zataga kiransa taji hakan dukda bata d’aga wayar ta tabbatar da ko wanene ba..
Balcony ta shige sanda ta k’ara wayar a kunnenta su Aunty B da Zulfah suka bita da kallo ganin yanda kiran ya sanyata canzawa lokaci guda, da alama bataso suji wayan nata...
Basu kuma bi takanta ba sukaci gaba da firansu suna cin k’osan...
Koda ta d’aga wayar bata iya cewa komai ba, sannan tunda taji shiru daga d’aya b’angaren tasan shine...
Tsuka tai zata katse kiran tana mai furta “Sai a kira mutum ayi shiru don rashin abinyi, toh ni inada abinyi...”
Khalid ya katseta da fad’in “Don’t think of doing that, no one hangs up on me, wama yace miki ke ake nema, bansan ya akai na kiraki ba amma nasan dama addu’a kike na kiraki d’in, so don’t pretend...”
Tamkar yana kallonta haka ta juya idanu kana tace “Allah kiyaye nayi fatan ka kirani ko na jira kiranka, kada ka mance da bakinka kace bakasan yaya akai ka kirani ba so kaine mai d’okin kaji daga gareni...”
Tinda ta soma magana yake murmushi yana wasada hannun had’edd’iyar shopping bag d’in dake gefensa yana imagining yanda take murgud’a baki da juya idanu...
A hankali cikin kashe murya yace “You haven’t asked about my wound..”
A hasale tace “Toh ni ina ruwana da ciwonka, wai dan Allah baka da abinyi ne sai damuna...”
“You know what your problem is....?”
Shiru tai kurum tana saurarensa sanda yaci gaba da fad’in “You don’t know much about psychological trauma, that’s a serious problem... Ko tun kafin na kuskuri bigeki da mota haka kike...?”
Kasa furta komai tai sabida tsaban takaici gashi ta kasa katse wayar mai yake nufi mahaukaciya ya d’auketa ko mai, for the first time da tai masa magana cikin tsananin raunanniyar murya “Idan ka kira ne just to insult me Dan Allah na rok’eka kada ka sake kirana...”
Khalid yayi shiru yana saurarenta ba tareda ya furta komai ba...
Su duka biyun sunyi shiru, yanajin sanda tai yunk’urin katse wayar... Yai yunk’urin dakatar da ita amma baisan mai zaice ba, hak’uri zai bata ko kuwa, ya ake bada hak’urin shine bai sani ba, tabbas ta d’auki maganarsa da tsananin zafi yana iya gano hakan a muryarta....A hankali ya lumshe idanunsa had’ida fuzar da iska yana kuma bin shopping bag d’in da kallo wanda yasan gobe akwai aiki gabansa muddin ya tunk’areta, kaman ya fasa tafiyar yaji amma b’angare na zuciyarsa tana kwad’aitar masa tafiyar more than ever, a hankali ya shiga d’an buga kansa da hannu yana tunanin maike damunshi gameda al’amarin yarinyar.....
Mik’ewa yayi yana nad’e hannayen longs sleeve d’in dake jikinsa kana ya fad’a bathroom don gwara ya fice ball ko zuciyarsa zata samu sauk’i da tunaninta....
Yesmin kaw da shigowarta kenan ta ajiye masa k’aramar plate anyi wrapping da climfilm wani dad’i ne taji ya mamaye zuciyarta hango shopping bag da tai hadd’add’e kalan mata ajiye saman gadonsa, zuciyarta ta shiga raya mata ma ita zai bada, a hankali ta sad’ad’a tana lek’a cikin ‘yar jakan, bata gama sumewa ba saida taga abinda ke ciki, ita kad’ai ta fad’a duniyar imagination tana murna harda ‘yar tsallenta, jin yana yunk’urin fitowa ya sanyata saurin barin d’akin cikeda jin dad’i...
Shiko Khalid yana fitowa ya hangi abu aje gefen bedside, ko bai tambaya ba yasan aikinta ne, yarinyar nan ta rainashi har d’akinsa take kawo mishi abinci yayi magana Ammi ta tasa shi gaba da fad’a, amma zai maganinta ta yanda ko hanyar d’akinsa aka kuma nuna mata bazatabi ba... Ya k’arashe yana mai yin k’wafa kafin ya d’auki plate d’in ya fice dashi bai dire ko ina ba sai kitchen a cikin sink, Kubura na lab’e tana ganinshi dad’i kaman ya kasheta....
***
Hannayenta Ammi ta rik’o kana tace “I’ve my reasons Siyama, sannan ki sani duk wani dalilina don na kareki ne....”
Wannan karon da tsananin mamaki Siyama ke duban mahaifiyarta....
“Ammi you making me nervous.... Is there anything I need to know...?”
K’uri Ammi ta mata kana ta girgiza kai a hankali tace “No, babu komai.... I just feel like supporting your idea ne as my daughter.... Ki tashi ki tafi gidanki and make sure kinci gaba da shan magani....”
Jiki a sanyaye Siyama ta mik’e tana mamakin mahaifiyar tata, toh meyasa ta canza ra’ayinta, mai Momyn Sameer ta fad’i mata....?
Still tai tana murza mabud’an motarta a hankali kafin tasa kai ta fice daga gidan bata zarce ko ina ba sai gidansu Aminiyarta Laila....
***
Sultan ya dube shi a karo na biyu kana ya girgiza kai yace “Sameer ko zaka kwana kana fad’a min babu abinda ke damunka... Just tell me please maybe I can help...”
Shafe fuskarsa yayi da duka tafukan hannayensa kana yace “Sultan how does it feel ace mutanen da kafi so a rayuwarka sun maka k’arya...?”
Sultan ya gyara zama had’ida murmusawa an tab’o yanda ke masa k’aik’ayi...
Kafad’ar Sameer ya dafa kana yace “Sameer this life has never been fair, and it will never be... Ka yarda.....?”
D’ago rinannun idanunsa yai yana duban Sultan d’in kana ya jinjina kai yace “Yeah na yarda....”
“Mai Siyama ta maka...?” Sultan ya jefo masa tambayar kai tsaye, shiru ne na d’an lokaci ya gifta kana ya girgiza kai yace “It’ll be better if we don’t talk about it...”
Sultan ya masa k’uri yana nazarinsa, jin jina kai yai kana yace “Is ok if you don’t wanna talk about it... But whenever you feel like, don’t forget that I’m here bro....”
Jinjina kai Sameer yai yana mai furta “Na gode abokina...”
Sun d’an d’ibi lokaci Sultan ke jansa da fira dukda ba wani amsawa Sameer d’in keyi ba, yamma lis Sameer yayiwa Sultan sallama ya wuce...
Tafiyar Sameer da kad’an wayar Sultan ta d’auki ruri, ganin mai kiran ya sanyashi sakin murmushi kana ya d’aga yana mai furta “Kaman nasan update d’in da zaki bani...”
Shiru ya d’an biyo baya alamu magana ake daga d’aya b’angaren....
Sultan ya kuma murmusawa kana yace “Saura k’iris burina ya cika, idan kuwa ya cika kada ki manta kinada babban kyauta domin kaw kin taka muhimmiyar rawa...”
Ya kuma murmusawa yana mai mik’ewa tsaye had’ida sakala hannu guda cikin aljihu alamun yana sauraren mai magana daga d’aya b’angaren...
A hankali yake shafan sajensa kana yace “INDA RAI burina gab yakeda cika...”
Ya saki dariya mai ‘yar sauti kafin sukai sallama ya katse wayar....
***
Kano
Nabila ta d’aga appointment letter d’in tana kuma duba cikeda murna, baki har kunne take fad’in “Addah Zulfah gaskiya nai miki murna ubangiji yasanya alkhairi ya kuma sa a fara a sa’a...”
Zulfah ta murmusa tana duban ‘yar uwar tata cikeda k’auna tace “Ameen Nabyn Mamy, amma ai ba yanzu zan soma zuwa ba sai na gama iddah...”
Nabilah ta d’an tab’e fuska tace “Oho dai at least kema zaki tsara rayuwarki yanzu babu tak’urin Yaya Hafiz balle na Hajiya da watsattsun k’annensa...”
Murmushin k’arfin hali Zulfah tai ba tareda ta furta komai ba...
Nabila ta dubeta a kaikaice tace “Kar kicemin har yanzu tunaninsa da mafarkin komawa gidansa kike..?”
Murmushin Zulfah ta sakeyi wanda da gani mai ciwo ne kana tace “Nabilah kenan, Yaya Hafiz bazan tab’a goge shi cikin tarihin rayuwata ba amma ki sani kaman yanda na ambaci tarihi tabbas ya zama tarihin, he’s already in the past, sannan koda ace babu dangantaka na zumuntan jini tsakaninmu aure ya had’a sannan kar ki mance akwai rabo tsakaninmu, Kausar ta kuma had’amu Nabilah... Hafiz Uban d’iyata ce Nabilah, we cannot change that...”
D’an rausayar da idanu Nabila tai kana tace “Haka ne amma nidai bazan daina k’irgen sauran kwanakin da suka rage aurensa ya sauk’a gaba d’aya akanki ba, Kausar kuma muddin Raiha na nan banida haufin zata kula da ita fatana dai kar yace zai d’auki d’iyarsa ya damk’a hannun wancan ‘yar tashan matar tasa ba...”
Zulfah tai shiru tana sauraren Nabila domin kaw ta tab’o mata yanda ke tsananin ciwo a gareta, duk randa ta tuna Hafiz na iya damk’ar rik’on d’iyarta hannun wata matar...
Kaman Nabilah tasan abinda take tunani ta d’an dafata ta shiga calming d’inta, a haka Aunty B ta shigo ta taddasu tana fad’in “Ga k’osai ‘yar la’asar da zafinshi yanzu Tatu ta sauk’e...” Ta k’arashe tana dire masu k’aramar parantin...
Aiko nan Nabilah ta dirk’o k’asa ta shiga cin k’osan tana dandalan barkono, Aunty B tace “Kidaici barkonon nan a hankali don zafi ne dashi...”Takai dubanta ga Zulfah tace “D’iyata zakisha kunun ne ta dama kafin ta tafi...”
Zulfah ta girgiza kai tace “A’a Aunty zan sha kunun ayan d’azu dai inaga dakwai saura a fridge..”
Ai bata gama rufe baki ba Nabilah ta mik’e ta nufi fridge tana fad’in “Su Aunty an iya waraya d’iyarki kawai kika sani, dama akwai kunun aya a gidan shine ko amin tayi toh wllhi rabona ne nasha nayi guzirin sauran..”
Aunty B tace “Eh dai so so ne amma son kai yafi, kiji na fad’a miki nafison Zulfah tah..”
Zulfah sai dariyansu take itako Nabila sai kwankwad’an kunun ayarta take tana lumshe idanu ko kulasu batai ba... Wayarta dake ringing ne ya d’auki hankalinta, ta nufo handbag d’inta a guje tana lalumen wayar take fad’in “Toh Mamyna na nemana nima, taga yamma tayi....” Aya ta sakawa kalaman nata ganin mai kiranta, tasan ba kowa bane illa bugun zuciyarta, domin kaw ganin bak’uwar lamba d’aukeda had’add’un lambobi yasa taji k’irjinta na bugawa, tasan shi kad’aine zataga kiransa taji hakan dukda bata d’aga wayar ta tabbatar da ko wanene ba..
Balcony ta shige sanda ta k’ara wayar a kunnenta su Aunty B da Zulfah suka bita da kallo ganin yanda kiran ya sanyata canzawa lokaci guda, da alama bataso suji wayan nata...
Basu kuma bi takanta ba sukaci gaba da firansu suna cin k’osan...
Koda ta d’aga wayar bata iya cewa komai ba, sannan tunda taji shiru daga d’aya b’angaren tasan shine...
Tsuka tai zata katse kiran tana mai furta “Sai a kira mutum ayi shiru don rashin abinyi, toh ni inada abinyi...”
Khalid ya katseta da fad’in “Don’t think of doing that, no one hangs up on me, wama yace miki ke ake nema, bansan ya akai na kiraki ba amma nasan dama addu’a kike na kiraki d’in, so don’t pretend...”
Tamkar yana kallonta haka ta juya idanu kana tace “Allah kiyaye nayi fatan ka kirani ko na jira kiranka, kada ka mance da bakinka kace bakasan yaya akai ka kirani ba so kaine mai d’okin kaji daga gareni...”
Tinda ta soma magana yake murmushi yana wasada hannun had’edd’iyar shopping bag d’in dake gefensa yana imagining yanda take murgud’a baki da juya idanu...
A hankali cikin kashe murya yace “You haven’t asked about my wound..”
A hasale tace “Toh ni ina ruwana da ciwonka, wai dan Allah baka da abinyi ne sai damuna...”
“You know what your problem is....?”
Shiru tai kurum tana saurarensa sanda yaci gaba da fad’in “You don’t know much about psychological trauma, that’s a serious problem... Ko tun kafin na kuskuri bigeki da mota haka kike...?”
Kasa furta komai tai sabida tsaban takaici gashi ta kasa katse wayar mai yake nufi mahaukaciya ya d’auketa ko mai, for the first time da tai masa magana cikin tsananin raunanniyar murya “Idan ka kira ne just to insult me Dan Allah na rok’eka kada ka sake kirana...”
Khalid yayi shiru yana saurarenta ba tareda ya furta komai ba...
Su duka biyun sunyi shiru, yanajin sanda tai yunk’urin katse wayar... Yai yunk’urin dakatar da ita amma baisan mai zaice ba, hak’uri zai bata ko kuwa, ya ake bada hak’urin shine bai sani ba, tabbas ta d’auki maganarsa da tsananin zafi yana iya gano hakan a muryarta....A hankali ya lumshe idanunsa had’ida fuzar da iska yana kuma bin shopping bag d’in da kallo wanda yasan gobe akwai aiki gabansa muddin ya tunk’areta, kaman ya fasa tafiyar yaji amma b’angare na zuciyarsa tana kwad’aitar masa tafiyar more than ever, a hankali ya shiga d’an buga kansa da hannu yana tunanin maike damunshi gameda al’amarin yarinyar.....
Mik’ewa yayi yana nad’e hannayen longs sleeve d’in dake jikinsa kana ya fad’a bathroom don gwara ya fice ball ko zuciyarsa zata samu sauk’i da tunaninta....
Yesmin kaw da shigowarta kenan ta ajiye masa k’aramar plate anyi wrapping da climfilm wani dad’i ne taji ya mamaye zuciyarta hango shopping bag da tai hadd’add’e kalan mata ajiye saman gadonsa, zuciyarta ta shiga raya mata ma ita zai bada, a hankali ta sad’ad’a tana lek’a cikin ‘yar jakan, bata gama sumewa ba saida taga abinda ke ciki, ita kad’ai ta fad’a duniyar imagination tana murna harda ‘yar tsallenta, jin yana yunk’urin fitowa ya sanyata saurin barin d’akin cikeda jin dad’i...
Shiko Khalid yana fitowa ya hangi abu aje gefen bedside, ko bai tambaya ba yasan aikinta ne, yarinyar nan ta rainashi har d’akinsa take kawo mishi abinci yayi magana Ammi ta tasa shi gaba da fad’a, amma zai maganinta ta yanda ko hanyar d’akinsa aka kuma nuna mata bazatabi ba... Ya k’arashe yana mai yin k’wafa kafin ya d’auki plate d’in ya fice dashi bai dire ko ina ba sai kitchen a cikin sink, Kubura na lab’e tana ganinshi dad’i kaman ya kasheta....
***