Sashe 46
Inda Rai Da Rabo Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A b’angaren Zulfah kuwa yau ne zata soma ziyartan wajen aikinta sannan a jiya laraba ne take fita daga iddarta, d’an zaman da tayi waje guda babu fita har wani haske ta k’ara, sannan yanzu hankalinta ya kwanta babu tsangwaman Hafiz dana danginsa, tinanin iyayenta da d’iyarta ke d’awainiya da ita, tanaji a zuciyarta sunyi kusan kasancewa ita da d’iyarta tare, tai murmushi tana kuma daidaita zaman mayafin abaya dake bisa kanta, Aunty B ta shigo tana sakar mata murmushi ganin yanda tayi kyau tayi kumari kaman ba Zulfa’u wacce Hafiz ya lahanta mata rayuwa ba...
“D’iyata kinyi kyau...” Aunty B tace tana mai kamo hannayen Zulfah...
Murmushi Zulfah ta saki a hankali kana tace “Na gode Auntynah...”
“Muje na soma ijiyeki sai na wuce nawa wajen aikin...” Ta fad’i tana gyara zaman mayafinta tana mai kallon kanta a mirror d’in, car keys d’inta na hannunta...
Jiki a sanyaye Zulfah ta d’au handbag d’inta mai launin shud’i wanda duka Aunty B ta sai mata sabida zata fara zuwa aiki, wadatattun kaya na gayu da kwalliya ta sai mata dukda Zulfa’un ba gwanar pente pente bace a fuska, iyakaci powder ne saiko man leb’e...
Aunty B ta dubeta yanda take tafiya a sanyaye kana tace “D’iyata lafiya kuwa...?”
Murmushi Zulfah ta kuma saki kana tace “Aunty I’m a little nervous, zan had’u da mutane da dama wajen aikina.... Sannan Aunty wai ni Zulfa’u za’ake hasko muryata gidan radio...?”
Aunty B ta murmusa tace “Kowa da haka ya saba Zulfa’u, ki saki jikinki kiyi aikinki da kyau na tabbata sanda mutane suka soma sauraren dadd’an muryarki zasu k’aunaci shirye shiryenki domin kaw ba dad’in sauti da iya kalamai kawai ba harta d’abi’unki gwanin sha’awa ne abin birgewa....”
Zulfah tai murmushi cikeda k’warin gwiwa kana tace “Har kullum bazan gajiya da maki godiya ba Aunty, Ubangiji kema ya faranta miki yanda kike faranta min...”
Aunty na murmushi ta kamo hannayenta suka k’arasa mota tana mai kwab’anta da yawan gidiyan da take mata....
SameenaAleeyou📚
*INDA RAI*
_.................DA RABO_
*37*
*©Sameena Aleeyou...✍🏽*
Tsaye take kansa tanaci gaba da aika masa mummunar kallo, d’aurin kallabi a gefen kai as usual, ga taunar chewing gum da ya zamto d’abi’arta anayi ana hurashi had’ida yin k’as k’as.... Hannaye rik’eda k’ugu bata daina jijjiga ba take fad’in “Kanajina ba damuwata bace idan baka ciniki yanzu koma mai Kantin ne ya amshe kayanshi, wllhi duk yanda kaza ta shiga ta fita sai ka kawo min, ba shinkafa da tuwo aka aura maka ni kake bani ba ehe.... Yau kusan kwanaki uku kenan banci kaza ba jibi duk yanda na rame na d’aid’aice nayi bak’i, kaman ba jazir aka kawoni gidan nan ba....” Ta k’arashe tana juya idanu had’ida danna masa harara tana mai kuma hura chewing gum d’in bakinta.....
Fuzar da iska yayi hannaye bibbiyu ya rafka uban tagumi yana dubanta, ga wata uwar rama da yayi gaba d’aya kayayyakinsa wuyan sun masa yawa, idanuwansa duk sunyi kwarmi sun firfito waje, kaman ba Hafiz duk ya canza...
“Sau nawa zance maki kiyi hak’uri banida kud’in yanzu, kina gani kud’in da zan hau abin hawa zuwa kasuwa banida ita, jiya da na tari Alhaji da zancen ko amsani baiyi ba ya shige gida, wanne kikeso naji dashi Sawwama, shin ke ko tausayamin bakiyi ne....?” Ya k’arashe cikin k’asa da murya...
Wani wawan harara ta kuma aika masa tana mai ci gaba da taunar chewing gum tace “Toh ni ina ruwana don Alhaji bai amsaka ba, Alhaji nake aure ko kai, kai nifa bara kaji na fad’a maka billahillazi babu abinda ya shalleni kaji ne dole ka nemo ka kawomin naci, kuma kasan banacin guda d’aya tak, biyu zuwa uku dole ka kawomin, idanma sata zakai kai ka sani... Malam da Allah ka tashi ka fice min na gaji da ganinka zaune cikin gida....”
Iya wuya Sawwama ta kawo Hafiz.... Ya girgiza kai yana mai tuno Zulfah wacce duk abinda ya kawo gidan da sunan abinci sai tayita masa godiya tanai masa addu’o’in da duk k’iyayyar da yake mata sai yaji natsuwa da kwanciyar hankali cikin zuciyarsa, hakan bashi zai hana ya daddana mata wulak’anci ba, ya zageta ya muzantata ya tozarta iyayenta, daidai da rana guda bata tab’a ramawa ba, wasu lokutan haka yakan barta babu abinci dukda lokacin da take gidan samunsa yafi bunk’asa haka saidai yaje waje ya kashesuwa matan banza ko shaye shayen iska wanda ko d’aya yanzu bai isa ya kwatanta ba, duk wani kayan holewa sun fice masa a rai, toh ma ko yace zaiyi ina kud’in yi d’in, gaba d’aya duniyar tana neman tai masa d’aurin goro...
A hankali ya mik’e ba tareda ya kuma tankata ba ya nufi k’ofa...
Tuni Sawwama ta tare gabansa tana mai ci gaba da fad’in “Wllhi wllhi kaji na rantse maka idan baka dawo gidan nan da k’ullin kaji ba saidai kayi kwanan waje....”
Ya dubeta idanu a raunane gashi sam bai iya mata gardama baisan dalili ba, sukuf sukuf ya fice tamkar wani gajiyayye...
Da k’yar ya samu babur d’in da ya d’aukesa zuwa gidan Abbah da sunan idan ya isa zai bawa mai babur d’in kud’insa, shima mai babur d’in saida sukayita da wajewa yana masa gargad’in kada ya gudu masa da kud’i...
Koda ya shiga gidan ya jima yana hango sashensu Mamy kaman mai tunanin wani abin, jiki a sanyaye ya shige ya nufi sashen Mamani...
Mamani na zaune saman darduma tana gyara cazbahanta da ya hargitse taji sallama kamanta jikanta Hafiz...
Ya shiga wage baki tanai masa lale....
Kallo guda tai masa ai batasan sanda ta saki ‘ya’yan cazabahan dake hannunta ba suka watse k’asa...
“Kalu innalillahi wa inna’ilaihi raji’una... Laa ilaha illahu Mahammadar Rasulillahi.... Hafizu lafiya...? Meye haka..? Ciwo ne kayi.....?” Tayi maganar hannayenta dafe a k’irji...
Banda shafa k’eya Hafiz baya komai...
“Mamani naira d’ari zaki bani na sallami mai babur.....” Ya fad’i yana tsaye kanta...
“Yo ni fah baka amsa min tambayata ba, ita shashashar matarka taka Zulfa’u bata kula dakaine kokuwa...?”
Ambato Zulfah da tai yasa ya kuma kai mata duba had’ida lumshe idanunshi... “Mamani ki bani na sallami mai babur kar ya tara min jama’a...”
Da dafe dafe ta mik’e tanaci gaba da salallami tana tambayarsa ko jinya yayi, can wajen ajiyarta a uwar d’aki ta lalumosa ‘yan hamsin guda biyu ta bashi
“Ungo nan jeka biyashi ka dawo ka sanar dani uwar mai Zulfa’u keyi da ta bari ka lalace irin haka, kahurar yarinya mai halin uwarta, wato bari ta kasheka ta huta, kai wannan yarinya sam babu alheri tattareda ita, tsaban ta shahara ma ni ko a gidan nan na daina ganinta... Toh wllhi har yanda take zanje na sameta naci mata mutunci, haihuwarta yayi sanadiyar salwantar min da Ma’aruf d’ina gashi yanzu tana neman kaima ta aika lahira, toh ahir d’inta saidai ita ta mutu bakai ba, kai wannan yarinya gubarta yafi k’arfin annoba... Ni tin tana k’arama nacewa Manu babu alheri tattareda ita ya kaita bakin kogi aljanai su d’auka yak’i toh yanzu ga irinta waye ya sanima koda maita aka haifota ta lashe Ma’aruf gashi yanzu zata lashe Hafizu... Ohni Halimatu Manu ya haifo mana annoba a dangi....”
Har Hafiz ya sallami mai adaidaita ya dawo Mamani bata daina d’ibewa Zulfa’u albarka ba...
K’uri kurum ya mata don ko k’arfin magana baida ita, kwanuka dake gefe ya janyo ya shiga bud’ewa sauran karin kumallon safiya tuni ya shiga tura soyayyar doyar bakinsa yana had’iya yana muzurai...
Mamani ta rafka uban tagumi ta sanyashi gaba tana kallo, tsabagen tsanan Zulfah ya tsaya mata a rai tama mance kwanakin baya ance mata Hafiz d’in ya kuma aure....
Ta mik’e da k’yar ta kawo masa ruwa tana tambayarsa ko shayine za’a had’a masa, ko amsata bai iya yi ba sai girgiza mata kai kurum da yake alamun a’a...
Bayan ya ida tura sank’ararriyar doyar ne ya kora da ruwa nan yake fad’iwa Mamani wasu ‘yan kud’ad’e yazo ta bashi...
Babu musu ta d’ebo masa cikin bandir d’in ‘yan d’ari bibbiyu da kwanaki Haladu yaron Kirki ya bata...
Ta tasashi gaba tana tambayarshi meke faruwa....
Bai iya amsata ba ya mik’e yana fad’in zai kuma dawowa dama kud’in yazo ta d’an bashi sabida wasu ‘yan matsaloli da suka kunno masa....
Gaba d’aya kaman ba Hafizu mai son gayu da tirare ba, kaman wanda aka canza shi haka ya koma, ko d’an irin hira da yake zama suyi da Mamani yanzu ta lura baima zuwa ita idanba ta fara mantuwa irinta tsofi ba sai tace rabonta da ta skashi a idanunta ya doshi watanni, sam bai zuwa yanzu kaman da, gashi ita ta k’udiri niyyan bazata taka yanda Zulfa’u annoba take ba, amma yanzu kam ya zama dole taje gidan Hafizu tacima Zulfa’u mutunci taji dalilin da yasa ta bar mata jika ya d’aid’aice haka ba, haka tanaji tana gani Hafiz ya fice cikin sauri kaman zai kifa k’asa don d’an doyar da ya samu yaci yasa ya sami kuzari....
***
A gidan Radio Kafar ‘Yanci 96.8 kuwa sosai Zulfah ta sami karb’uwa daga wajen ma’aikatan gidan radion a karonta na farko taredasu, wata budurwa wacce Zulfah zata d’ara mata a shekaru da kad’an mai suna Atika ita taita nunawa Zulfah yanda shirye shiryen nasu ke wakana, ta kuma sanar da ita cewa itace take shirin nan na MU ZAB’I CANCANTA shirin da ake tattaunawa da kuma fashin bak’i gameda jagorancin da ‘yan siyasa suke a k’asar...
Zulfa’u ta zaro idanu waje cikeda jin dad’i tana fad’in “Dama kece Atika Shu’aib dake gudanar da shirin Mu zab’i Cancanta, kai don dai bakisan yanda nake matuk’ar son sauraren shirin nan bane, sam bai wuceni musamman da yanzu zab’e ya kunno kai sosai..”
Atika ta murmusa tace “Gashi yau kin had’u dani kuma nima naji dad’in had’uwa dake gashi Allah ya had’amu wajen aiki guda, ina fata Allah ya dafa mana cikin sana’armu...”
Zulfah ta amsa da amin cikeda nuna jin dad’inta itama, kafin Atika tace “Muje ai inaga Manager ya iso yanzu za’a sake mana lokutan shirye shirye musamman sabida an d’ibi sabbin ma’aikata.....”
Zulfah ta jinjina kai murmushi kwance saman fuskarta tana biye da Atika suka nufi babban d’akin gudanar da shirye shiryensu yanda a nan zasu gana da manager gaba d’aya ma’aikatan gidan Radio d’in....
***
“D’iyata kinyi kyau...” Aunty B tace tana mai kamo hannayen Zulfah...
Murmushi Zulfah ta saki a hankali kana tace “Na gode Auntynah...”
“Muje na soma ijiyeki sai na wuce nawa wajen aikin...” Ta fad’i tana gyara zaman mayafinta tana mai kallon kanta a mirror d’in, car keys d’inta na hannunta...
Jiki a sanyaye Zulfah ta d’au handbag d’inta mai launin shud’i wanda duka Aunty B ta sai mata sabida zata fara zuwa aiki, wadatattun kaya na gayu da kwalliya ta sai mata dukda Zulfa’un ba gwanar pente pente bace a fuska, iyakaci powder ne saiko man leb’e...
Aunty B ta dubeta yanda take tafiya a sanyaye kana tace “D’iyata lafiya kuwa...?”
Murmushi Zulfah ta kuma saki kana tace “Aunty I’m a little nervous, zan had’u da mutane da dama wajen aikina.... Sannan Aunty wai ni Zulfa’u za’ake hasko muryata gidan radio...?”
Aunty B ta murmusa tace “Kowa da haka ya saba Zulfa’u, ki saki jikinki kiyi aikinki da kyau na tabbata sanda mutane suka soma sauraren dadd’an muryarki zasu k’aunaci shirye shiryenki domin kaw ba dad’in sauti da iya kalamai kawai ba harta d’abi’unki gwanin sha’awa ne abin birgewa....”
Zulfah tai murmushi cikeda k’warin gwiwa kana tace “Har kullum bazan gajiya da maki godiya ba Aunty, Ubangiji kema ya faranta miki yanda kike faranta min...”
Aunty na murmushi ta kamo hannayenta suka k’arasa mota tana mai kwab’anta da yawan gidiyan da take mata....
SameenaAleeyou📚
*INDA RAI*
_.................DA RABO_
*37*
*©Sameena Aleeyou...✍🏽*
Tsaye take kansa tanaci gaba da aika masa mummunar kallo, d’aurin kallabi a gefen kai as usual, ga taunar chewing gum da ya zamto d’abi’arta anayi ana hurashi had’ida yin k’as k’as.... Hannaye rik’eda k’ugu bata daina jijjiga ba take fad’in “Kanajina ba damuwata bace idan baka ciniki yanzu koma mai Kantin ne ya amshe kayanshi, wllhi duk yanda kaza ta shiga ta fita sai ka kawo min, ba shinkafa da tuwo aka aura maka ni kake bani ba ehe.... Yau kusan kwanaki uku kenan banci kaza ba jibi duk yanda na rame na d’aid’aice nayi bak’i, kaman ba jazir aka kawoni gidan nan ba....” Ta k’arashe tana juya idanu had’ida danna masa harara tana mai kuma hura chewing gum d’in bakinta.....
Fuzar da iska yayi hannaye bibbiyu ya rafka uban tagumi yana dubanta, ga wata uwar rama da yayi gaba d’aya kayayyakinsa wuyan sun masa yawa, idanuwansa duk sunyi kwarmi sun firfito waje, kaman ba Hafiz duk ya canza...
“Sau nawa zance maki kiyi hak’uri banida kud’in yanzu, kina gani kud’in da zan hau abin hawa zuwa kasuwa banida ita, jiya da na tari Alhaji da zancen ko amsani baiyi ba ya shige gida, wanne kikeso naji dashi Sawwama, shin ke ko tausayamin bakiyi ne....?” Ya k’arashe cikin k’asa da murya...
Wani wawan harara ta kuma aika masa tana mai ci gaba da taunar chewing gum tace “Toh ni ina ruwana don Alhaji bai amsaka ba, Alhaji nake aure ko kai, kai nifa bara kaji na fad’a maka billahillazi babu abinda ya shalleni kaji ne dole ka nemo ka kawomin naci, kuma kasan banacin guda d’aya tak, biyu zuwa uku dole ka kawomin, idanma sata zakai kai ka sani... Malam da Allah ka tashi ka fice min na gaji da ganinka zaune cikin gida....”
Iya wuya Sawwama ta kawo Hafiz.... Ya girgiza kai yana mai tuno Zulfah wacce duk abinda ya kawo gidan da sunan abinci sai tayita masa godiya tanai masa addu’o’in da duk k’iyayyar da yake mata sai yaji natsuwa da kwanciyar hankali cikin zuciyarsa, hakan bashi zai hana ya daddana mata wulak’anci ba, ya zageta ya muzantata ya tozarta iyayenta, daidai da rana guda bata tab’a ramawa ba, wasu lokutan haka yakan barta babu abinci dukda lokacin da take gidan samunsa yafi bunk’asa haka saidai yaje waje ya kashesuwa matan banza ko shaye shayen iska wanda ko d’aya yanzu bai isa ya kwatanta ba, duk wani kayan holewa sun fice masa a rai, toh ma ko yace zaiyi ina kud’in yi d’in, gaba d’aya duniyar tana neman tai masa d’aurin goro...
A hankali ya mik’e ba tareda ya kuma tankata ba ya nufi k’ofa...
Tuni Sawwama ta tare gabansa tana mai ci gaba da fad’in “Wllhi wllhi kaji na rantse maka idan baka dawo gidan nan da k’ullin kaji ba saidai kayi kwanan waje....”
Ya dubeta idanu a raunane gashi sam bai iya mata gardama baisan dalili ba, sukuf sukuf ya fice tamkar wani gajiyayye...
Da k’yar ya samu babur d’in da ya d’aukesa zuwa gidan Abbah da sunan idan ya isa zai bawa mai babur d’in kud’insa, shima mai babur d’in saida sukayita da wajewa yana masa gargad’in kada ya gudu masa da kud’i...
Koda ya shiga gidan ya jima yana hango sashensu Mamy kaman mai tunanin wani abin, jiki a sanyaye ya shige ya nufi sashen Mamani...
Mamani na zaune saman darduma tana gyara cazbahanta da ya hargitse taji sallama kamanta jikanta Hafiz...
Ya shiga wage baki tanai masa lale....
Kallo guda tai masa ai batasan sanda ta saki ‘ya’yan cazabahan dake hannunta ba suka watse k’asa...
“Kalu innalillahi wa inna’ilaihi raji’una... Laa ilaha illahu Mahammadar Rasulillahi.... Hafizu lafiya...? Meye haka..? Ciwo ne kayi.....?” Tayi maganar hannayenta dafe a k’irji...
Banda shafa k’eya Hafiz baya komai...
“Mamani naira d’ari zaki bani na sallami mai babur.....” Ya fad’i yana tsaye kanta...
“Yo ni fah baka amsa min tambayata ba, ita shashashar matarka taka Zulfa’u bata kula dakaine kokuwa...?”
Ambato Zulfah da tai yasa ya kuma kai mata duba had’ida lumshe idanunshi... “Mamani ki bani na sallami mai babur kar ya tara min jama’a...”
Da dafe dafe ta mik’e tanaci gaba da salallami tana tambayarsa ko jinya yayi, can wajen ajiyarta a uwar d’aki ta lalumosa ‘yan hamsin guda biyu ta bashi
“Ungo nan jeka biyashi ka dawo ka sanar dani uwar mai Zulfa’u keyi da ta bari ka lalace irin haka, kahurar yarinya mai halin uwarta, wato bari ta kasheka ta huta, kai wannan yarinya sam babu alheri tattareda ita, tsaban ta shahara ma ni ko a gidan nan na daina ganinta... Toh wllhi har yanda take zanje na sameta naci mata mutunci, haihuwarta yayi sanadiyar salwantar min da Ma’aruf d’ina gashi yanzu tana neman kaima ta aika lahira, toh ahir d’inta saidai ita ta mutu bakai ba, kai wannan yarinya gubarta yafi k’arfin annoba... Ni tin tana k’arama nacewa Manu babu alheri tattareda ita ya kaita bakin kogi aljanai su d’auka yak’i toh yanzu ga irinta waye ya sanima koda maita aka haifota ta lashe Ma’aruf gashi yanzu zata lashe Hafizu... Ohni Halimatu Manu ya haifo mana annoba a dangi....”
Har Hafiz ya sallami mai adaidaita ya dawo Mamani bata daina d’ibewa Zulfa’u albarka ba...
K’uri kurum ya mata don ko k’arfin magana baida ita, kwanuka dake gefe ya janyo ya shiga bud’ewa sauran karin kumallon safiya tuni ya shiga tura soyayyar doyar bakinsa yana had’iya yana muzurai...
Mamani ta rafka uban tagumi ta sanyashi gaba tana kallo, tsabagen tsanan Zulfah ya tsaya mata a rai tama mance kwanakin baya ance mata Hafiz d’in ya kuma aure....
Ta mik’e da k’yar ta kawo masa ruwa tana tambayarsa ko shayine za’a had’a masa, ko amsata bai iya yi ba sai girgiza mata kai kurum da yake alamun a’a...
Bayan ya ida tura sank’ararriyar doyar ne ya kora da ruwa nan yake fad’iwa Mamani wasu ‘yan kud’ad’e yazo ta bashi...
Babu musu ta d’ebo masa cikin bandir d’in ‘yan d’ari bibbiyu da kwanaki Haladu yaron Kirki ya bata...
Ta tasashi gaba tana tambayarshi meke faruwa....
Bai iya amsata ba ya mik’e yana fad’in zai kuma dawowa dama kud’in yazo ta d’an bashi sabida wasu ‘yan matsaloli da suka kunno masa....
Gaba d’aya kaman ba Hafizu mai son gayu da tirare ba, kaman wanda aka canza shi haka ya koma, ko d’an irin hira da yake zama suyi da Mamani yanzu ta lura baima zuwa ita idanba ta fara mantuwa irinta tsofi ba sai tace rabonta da ta skashi a idanunta ya doshi watanni, sam bai zuwa yanzu kaman da, gashi ita ta k’udiri niyyan bazata taka yanda Zulfa’u annoba take ba, amma yanzu kam ya zama dole taje gidan Hafizu tacima Zulfa’u mutunci taji dalilin da yasa ta bar mata jika ya d’aid’aice haka ba, haka tanaji tana gani Hafiz ya fice cikin sauri kaman zai kifa k’asa don d’an doyar da ya samu yaci yasa ya sami kuzari....
***
A gidan Radio Kafar ‘Yanci 96.8 kuwa sosai Zulfah ta sami karb’uwa daga wajen ma’aikatan gidan radion a karonta na farko taredasu, wata budurwa wacce Zulfah zata d’ara mata a shekaru da kad’an mai suna Atika ita taita nunawa Zulfah yanda shirye shiryen nasu ke wakana, ta kuma sanar da ita cewa itace take shirin nan na MU ZAB’I CANCANTA shirin da ake tattaunawa da kuma fashin bak’i gameda jagorancin da ‘yan siyasa suke a k’asar...
Zulfa’u ta zaro idanu waje cikeda jin dad’i tana fad’in “Dama kece Atika Shu’aib dake gudanar da shirin Mu zab’i Cancanta, kai don dai bakisan yanda nake matuk’ar son sauraren shirin nan bane, sam bai wuceni musamman da yanzu zab’e ya kunno kai sosai..”
Atika ta murmusa tace “Gashi yau kin had’u dani kuma nima naji dad’in had’uwa dake gashi Allah ya had’amu wajen aiki guda, ina fata Allah ya dafa mana cikin sana’armu...”
Zulfah ta amsa da amin cikeda nuna jin dad’inta itama, kafin Atika tace “Muje ai inaga Manager ya iso yanzu za’a sake mana lokutan shirye shirye musamman sabida an d’ibi sabbin ma’aikata.....”
Zulfah ta jinjina kai murmushi kwance saman fuskarta tana biye da Atika suka nufi babban d’akin gudanar da shirye shiryensu yanda a nan zasu gana da manager gaba d’aya ma’aikatan gidan Radio d’in....
***