← Book details Inda Rai Da Rabo Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 37 OF 198

Sashe 37

Inda Rai Da Rabo Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Ga tsananin mamakin Siyama suna shigowa garin Kano a toy store taga Khalid ya tsaya, ta juyo tana masa duban mai kuma zasuyi a nan....
Ko takanta baibi ba ya fice ya shiga store d’in, Jim kad’an ya fito da ‘yar jaka a hannunshi....
Back seat ya bud’e ya aje shopping bag d’in kana ya bud’e mazaunansa ya shige...
Ta dubesa a kufule tace “Khalid before ka shige sabganka take me to my husband first...”
“Kinga you can’t be giving me orders cos I’m not driver...”
Ta hararesa had’ida yin k’wafa kana ta juyar da fuskarta ga window dole ta shanye wulak’ancin Khalid tinda motarsa ce kuma shike driving, tasan dama kad’an yake jira akanta yayita rama duk abubuwan da take masa da kafin Daddy ya basa matsayi sosai a company....
Bata kuma tankashi ba duk hira da ya soma k’ok’arin janta dashi, idan ya kalli yanda ta had’e rai saidai ya kauda kai gefe yana murmushin mugunta....
Ganinsu a k’ofar gate d’in babbar jami’ar garin ya kuma sanyata dubansa shek’ek’e kana tace “Khalid wai yawon mai kakeyi dani ne, nace maka ka kaini wajen mijina kafin ka shiga sangan ka haba na gaji da zaman mota...”
Idan kujeran da yake bisa ya amsa shima zai amsa...
A hasale ta mik’a hannu ta danna horn tana fad’in “Khalid magana fah nake maka...”
Ya d’an dubeta a kaikaice yace “Idan kin matsu ki kira mijin naki yazo ya d’aukeki mana...”
Ta galla masa harara had’ida yin k’wafa...

Su Nabilah suna tafe zasu wuce class da wani lecturer ya masu fixing sai ganin kiranshi tai na shigo mata, fuzar da iska tai kana ta saka wayar a silent...
Wata kiran ta kuma shigowa, Yusrah da wata coursemate d’insu Faty da suke tace tare suka dubeta jin sai kiranta ake tak’i d’agawa..
Yusrah tace “Wai bazaki d’aga bane...?”
A d’an dak’ile ta dubeta kana tace “Toh kinsan wanene...?”
Yusrah ta murmusa tace”Khalid ne...”
Nabilah ta d’an rausayar da idanu tace “D’an rainin hankali zakice...”
Yusra da Faty suka dara kafin Faty ta tsaya business center karb’an handouts...

“Dan Allah ki d’aga...” Yusra ta fad’i tana dubanta...
“Na d’aga naji bak’a, kashe wayata ma zanyi...”
Murmushi Yusrah tayi kana tace “Kalan taku salon kenan, amma dai da kin d’aga bakisan mai zaice maki ba...”

Gajeren tsuka Nabilah tai kana tace “Banson nacinki na tsiya Yussy naji zan d’aga....”

A dak’ile ta d’aga wayar ba tareda tace komai ba...

Daga d’aya b’angaren yace “Bana kiran waya ya wuce d’aya ki kiyaye next time...”

Murmushin takaici tai kana tace “And who cares...”

Khalid ya shanye kana yace “Ki k’araso k’asan bishiyar dake gabanku kad’an...”

A hasale tace “And who are you to give me orders....?”

Murya a dake yace “Zan iya binki har cikin class d’in naku har gaban malamin naku ba wani abu ne idan hakan kika zab’a....” Bai jira cewarta ba ya katse kiran...

Sauk’e ajiyan zuciya tai tana duban Yusrah ba tareda tace komai ba, takai dubanta ga location d’in da ya sanar da ita, yana tsaye ya bada baya kansa na k’asa da alama wayarsa yake dannawa....
Huci kurum take tana dubansa ga wani irin yanayi data tsinta kanta ciki bayan hangosa tsaye da tayi...
Hannun Yusrah ta fincika suka nufi yanda yake...
Yusrah na tambayarta ko tsayuwa bata amsa bataiba taci gaba da fizgan hannunta....

SameenaAleeyou 📚
*INDA RAI*
_................DA RABO_

*31*

*©Sameena Aleeyou...✍🏽*

Yana nan tsaye yanda ta hangesa yana ci gaba da shafa wayarsa, sarai yaji k’arasowarsu amma yayi biris yaci gaba da abinda yake, tsaban haushi Nabila taji kaman ta kwab’e takalmin k’afarta ta jefi k’eyarsa dashi, ita kuwa Yusrah shan jinin jikinta tai had’ida matsawa gefe ta basu waje....
Bud’e bakinta kenan da niyyan magana ya juyo yana dubanta, idanunsu suka had’e waje guda, Nabilah ce ta soma kauda nata fuskar kafin Khalid yai murmushi da gefen bakinsa...
“Baki iya sallama bane..?”
Ya fad’i yana takowa kad’an zuwa kusanta...
A kaikaice ta watsa wani kallo da gefen idanu kana “Meyasa bazaka fice a rayuwata completely ba....?”
K’uri ya mata ganin yanzu ta daina masa magana da tsiwa ba kaman farkon had’uwarsu ba....
Gyara tsayuwarsa ya d’anyi gamida hard’e hannayensa ta baya waje guda kana yace “Is that really what you want... You want me out of your life... Kin tabbata daga zuciyarki kike fad’in haka...?”

Saurin d’agowa tai tana dubansa jin tambayoyin da ya jero mata lokaci guda.... Ta kasa furta komai saima k’irjinta dake ci gaba da lugude...
Khalid ya d’an murmusa ganin yanayinta yanda ya canza lokaci guda, gyaran murya ya d’anyi kana yace “Ina saurarenki....”

Murya a raunane tace “Yes abinda nake so kenan, just stay away from me na tsani ganinka....” Ta k’arashe muryarta na sark’ewa...
Khalid ya mata k’uri yana maimaita kalmar na tsani ganinka....
Lokaci guda ya jinjina kai kana yace “Alright, if that’s what you want...”
Shopping bag d’in dake gefe ya d’auko ya mik’a mata ba tareda yace komai ba...
Tabi jakan da kallo cikeda mamaki kana ta d’ago tana dubansa, wannan karon yanayin da bata tab’a ganin k’wayar idanunsa ciki ba ta gani... Jikinta yai wani irin mugun sanyi, a hankali ta shiga girgiza masa kai kana tace banaso bazan karb’a kayi hak’uri....”
“I insist please... be nice for once....” Ya k’arashe yanai mata wani irin duba mai cikeda ma’anoni wanda yasa ta kasa daina dubansa, ganin tunaninta na neman gushewa ya sanyata saurin saita kanta ta koma Nabilarta, cikin hayaniya tace dashi “Nace maka banaso ko ana dole ne....!”

Dariya ya kusa kufcewa Khalid mai hali da hali bazai canza ba Nabila kenan...

Ya d’an gimtse yace “I’m pretty sure zaki so kyautana sabida abinda mata sukafi so ne ciki... Just take it....” Ya k’arashe yana kuma mik’o mata...

Murmushi tai wanda za’a kirasa yak’e kai tsaye, kana ta kuma gimtse fuska tace “And who told you ni kuma inason duk abinda mata ke so.... Nace banaso bazan karb’a, if you may excuse me zan koma class...” Ta k’arashe tana d’aura hannu a kunkumi...

D’an d’aga gira sama yayi kana yace “Oh really.... I’m also surprised that you don’t wear makeup...” Yai maganar yana tab’e baki...

A hasale tace “Are you a fashion credit now....?!!”

Surrender yai da hannayensa kana yace “Easy... you don’t need to yell... Besides I’m not saying you’re ugly, all I’m saying is that ya kamata ki amshi kyutana....”

Banda mugun kallo bata aika masa komai, da fari ya soma acting kaman wani nice guy lokaci guda ya koma Khalid d’insa dama tasan bazai iya minti guda bai nuna halinsa ba....
A hasale tace dashi “You know, why not take that to your girlfriend... I don’t need it....”

Murmushi yai mai bayyan hak’wara for the first time kana yace “I don’t have one...”

Yanda yai maganar ya sanyata d’agowa tanai masa duban mamaki, lokaci guda Khalid yaci gaba da fad’in “Although a lot of girls are after me....”

Nan ma murmushin yak’e tai kana ta kuma gimtsewa tace “Why not go date one of them and leave me alone... Ka tak’ura ma rayuwata...”

“You not sure about that....?” Yayi maganar yana kashe mata idanu had’ida k’ura matasu wanda ya sanyata shiga wani yanayi... Su duka biyu sunyi nisa cikin duban juna dai dai lokacinda Yusra ta k’araso tana fad’iwa Nabilah malaminsu ya shiga aji tuntuni zai iya rufe k’ofa kuma don yanzu Safwan ya kirata...
Nabilah tai saurin saita kanta kana tace “Muje Yusrah...”

Yusrah dake k’ok’arin gaida Khalid Nabilah na janyeta Khalid ya mik’a mata bag d’in yace na Nabila ne....
Nabilah tai k’ok’arin wafcewa zata aje masa abinshi Yusrah tak’i sake mata, a daidai lokacin Siyama da ta gaji da jiranshi ta k’araso wajen tana mitan ta gaji da jiranshi, hango ‘yanmata guda biyu da tai ya sanyata sakin baki tana kallon ikon Allah, ashe kam ga abinda ke kawo Khalid Kano, ita bama wannan ba duk had’uwar Khalid daji da kansa bata zaci a irin wad’annan yaran zai tsaya ba, chabd’i lallai dole Ammi taji wannan batu, sauri ta k’ara don ta samu ta cimmasu saidai tun ‘yammatan sun wuce don da alama su basuma ganta ba, shiko Khalid baibar wajenba har saida yaga shigewarsu zauren karatu...
Siyama ta k’araso wajen da sauri tana raka bayansu da kallon k’ask’anci ta maido da dubanta ga Khalid tana masa duban mamaki kana tace “Wannan shine aikin....?”

Mugun kallo ya aika mata kana yace “So, meye naki a ciki...?”

Siyama ta murmusa kana tace “The whole Khalid Masanawa ashe a nan zai k’are.... Dama akan wannan ne kake wulak’anta Yesmin...?”

Ya kuma danna mata harara had’ida jan garejen tsaki kana ya nufi mota...

Siyama tabisa tanaci gaba da maganganu, saidai sam Khalid bai amsata ba saima bada himma am driving da yayi...
A haka suka iso unguwar da Sameer yake, ta d’ago tana duban Khalid d’in kaman zatai magana sai kuma ta fasa don tasan kad’an da aikinsa ne ya mata banza, Khalid yaja yai parking a k’ofar gate d’in had’ida yin relax cikin kujera alamun yana jira ta fita..
Ta d’ago da dubeshi a dak’ile kana tace “Miye haka, kaja kayi parking... What does this mean...?”

“It means kina iya fita, gidan dake gabanki shine gidan, and kiyi sauri ki fice zan k’arasa masauk’i na huta....”

Siyama tai k’wafa had’ida jinjina kai tace “Wllhi Daddy da Ammi sunji batun nan an gama kuma zigasu zanyi a saka bikinka cikin kwanaki....”
Ya watso mata mugun kallo a kaikaice kana yace “Kiyi fin haka, ni dan Allah ki fice min a mota...”

K’wafa ta kumayi tana watsa mashi mugun kallo kafin ta finciki marfin motar ta fice tana fad’in ya bud’e trunk ta d’auki kayanta.....
Chapter 37 · 0% Book details