Sashe 20
Inda Rai Da Rabo Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Jim kad’an Abbah ya shigo ya taddasu, nan suka soma gaidashi gaba d’ayansu, Khalid sai yafi kowa zak’ewa da son suyi sabo sosai da Abbah saidai ya lura shi Abban wani irin mutum ne wanda yakeda tsananin tsarewa, harta uban gayyan wato Sameer ba wani hira suke ba da alama kawai Allah ne ya had’a jininsu...
Tray mai d’aukeda ruwan sanyi Mamy ta hanga gefen fridge da alama Marliya ta mance bata kai masu ba, Nabilah ce gefenta tana had’a tray d’in abincin Mamani nan Mamy ta umarceta ta bar abinda take takaiwasu Abbah da bak’insa ruwa...
Sam Nabila batason shiga kan mutane don tasan wani cikin bak’in ya fad’i mata ba daidai ba tana iya danna masa mummunar kallo wanda har sai sun had’a idanu bak’on ya fahimci haka idan kuwa babu Abbah wajen ta jifa masa magana tai gaba abinta....
Badon taso ba ta d’auki tray d’in ta nufi sashen Abbah, sam bata kawo zatai artabo da mutum mai irin kamanninsa ba cikin gidansu, wani wawan birki ta danna tana mai kuma k’yafta idanu alamun badai gizo yake mata ba, tabbas shi d’in ne, Innalillahi toh mai yakeyi a gidansu, mai ya kawosa gidansu harma parlorn Abbanta, wannan wane irin mutum ne tai gamo dashi, kardai yasan Abbanta ne...?
Haka tayita jerowa kanta tambayoyi babu mai amsa mata su, Khalid kuwa tamkar ance ya juya sukayi idanu hud’u da Nabilah dake tsaye wajen tamkar an dasata, murmushi ya sakar mata had’ida kashe idanu guda irin taji mamakin nan koh....
Lokaci guda tai saurin saita kanta kana ta nufi parlorn kanta a k’asa, gaisuwan jam’u ta masu don bata fatan dogon gaisuwa ya shiga tsakaninta da d’aya daga cikinsu....
Sauri sauri ta fice daga parlorn k’irjinta naci gaba da bugu....
Saida ta sami bango ta tokare take iya sauk’e numfashi mai nauyin gaske, murmushinsa kurum take hangowa wanda ya kasa b’acewa daga k’wayan idanunta, da ace bata ganshi sau biyu kafin yau ba k’ila tace kamanni sukayi don ta tabbata babu abinda ya had’a Abbanta da wannan mutumin, toh amma shid’in ne dai, toh wai waye shi ne kam.... A hankali ta lumshe idanunta domin kuwa izuwa wannan lokaci lamuran mutumin ya soma bata tsoro...
Aunty Lami ce tazo zata shige ta kafe Nabilah da idanun ganinta cikin yanayi wanda bata tab’a ganinta cikin irinta ba...
K’arasowa tayi had’ida dafata kana tace “Nabila lafiya kike....?”
Sai sannan Nabilah ta bud’e idanu tana duban Aunty Lami....
Saurin turb’une fuska tayi kana tace “Lafiya mana Aunty... Barin shige...”
Bata jira cewan Aunty Lami d’inba tai shigewarta....
Kallo Aunty Lami ta rakata dashi tana mai nazarinta, gyara mayafinta tai kana tasa kai ta nufi parlorn Abbah....
Ganin da bak’i a parlorn ya sanyata sakin fuska sosai yawa mutuniyar k’warai tana wani aza mayafi ta k’arasa tana fad’in “Bak’i ne mukayi... Sannunku da zuwa....”
A tare Shamsu da Khalid suka soma gaidata kafin Sameer ya had’iye abincin dake bakinsa shima ya d’ora da gaisuwan a lokacin da ya d’ago fuskarsa....
Wani irin mummunar fad’uwan gaba ne ya dirarwa Aunty Lami sanda tayi tozali da idanun Sameer, ta kasa amsa gaisuwan da ya mata ta kuma kasa daina kallonsa, badon a zaune take ba tabbas da jiri ya iya kayarda ita....
Abubuwan da suka faru shekaru 30 baya suka shiga dawowa kwanyarta, har saida Abbah ya furta “Lami ana gaisheki ko bakiji bane...”
Sannan Aunty Lami ta iya kimtsa kanta....
Murya a d’an sark’afe ta amsa murmushin yak’e bai bar saman fuskarta ba....
Sauri sauri ta fice daga parlorn ta nufi nata sashen ta d’auki wayarta babu shiri....
Hajiya na faman rabon fad’an Hafiz da Sahariyya kan tak’urawa d’iyarsa Kausar da Sahariyya keyi taji wayarta na faman ruri cikin d’aka...
Fad’i take “Ku kuka sani ku cinye kanku idan bazakuji maganata ba, wannan yarinya taka mai jinin tsiya a tareda ita gwarama kayi auren ka kaita can wajen matarka ta kular maka da ita...” Tana ida fad’in haka ta nufi d’aki tana lalumar wayarta yanda ta tadda wayar ta katse, ganin wacce tai mata kiran ya sanyata saurin sake dialing layin....
Hafiz dake mak’ure da wuyan Sahariyya fad’i yake “Wllhi kinji na rantse babu yanda zankai Kausar nan gidan zata girma tinda ku kuka tilastama uwarta barinta don haka dole ku kula da ita, kin sanni kinsan banida kyau kukan yarinyar nan na sakeji wllhi sai nayi ajalin idanunki k’wara... Shashashar banza...”
Yana ida fad’in haka yayi jifa da ita kana yayi ficewarsa sai faman fito yake hula a karkace ya nufi wajen sahibarsa Sawwama.....
Tinda Aunty Lami ta d’auki wayar Hajiya ta fahimci babu lafiya.....
“Wai meke faruwa ne ni dan Allah ki sanar dani.....” Hajiya tace hankali tashe...
Aunty Lami ta samu jikin gado ta jingina kana tace “Haule anya kin tabbata Ma’aruf ya mutu...? Haule anya Ma’aruf ya zama tarihi kaman yanda muke tunani, anya Ma’aruf bazai dawo garemu ba....?”
Dukda bugu da k’irjin Hajiya keyi bai hanata dariyar yak’e ba kana tace “Haba Lami meye kuma kike neman maida mutane baya ana ci gaba a rayuwa, wane irin Ma’aruf...? Idan dai Ma’aruf d’an gidan Usman Mailafiya ne ya jima da mutuwa saidai mai kamanninsa, kinga kima daina sak’awa zuciyarki wannan mummunar zato don Allah....” Ta k’arashe tana zama bakin gado....
Girgiza kai kurum Aunty Lami take tamkar Hajiyan na dubanta kana tace “Inaga dai baki fahimci abinda nake nufi bane Haule amma idan da hali yau d’in nan mu had’u gidan Aminiyar sirri ta fad’i mana gaskiyar abinda tayida Ma’aruf Mailafiya don wllhi yau nikam nayi tozali dashi a raye....”
Jikin Hajiya ya d’anyi sanyi, gyara zamanta tai kana tace “Shikenan Lami mu had’u gobe gidan Aminiya tinda dai yaukam kinga dare yayi, ke nake jiyewa kinsan wannan baud’edd’en mijin naki ba bari zaiyi ki fice ba ni kuwa nawa mijin dama a tafin hannuna yake... Ma had’u goben....”
Aunty Lami ta amsada “Toh shikenan Alhaji na fita Kasuwa zan fito...”
Daga haka sallama sukayi ko waccensu tana sak’e sak’e cikin zuciyarta.....
***
Washe gari haka Nabila ta tasa Mamy gaba da tambaya ko tasan bak’in Abbah...
Mamy ta umarci Marliya data kwashe dankali cikin mai kana ta dubi Nabilah dake shirya wanke wanken plates cikin drawer tace “Kici gaba da tambayata abinda bai shalleki ba kar kiyi aikin dake gabanki....”
Nabilah ta turo baki gaba tace “Kai Mamy tambaya shikenan ya zama laifi ai da Marliya ce ko Addah suka tambayeki amsasu zakiyi, Mamy Dan Allah su wayesu...?”
Girgiza kai kurum Mamy tayi kana tace “Nabilah ban sansu ba hasalima ban shiga parlorn ba har dai suka tafi kina gani ai... Toh yaya za’ayi na sansu kin kuma san Abbanki kinsan wane irin mutum ne ba kasafai yakeso ana haurawa kansa ba musamman idan yana tareda bak’i, ballanata ma kinsan ba shigan zanyi ba idan ba shine ya buk’aci hakan ba... Wai me bak’in suka miki ne...?”
Ta k’arashe maganar tana mai jefo mata tambayar had’ida tsareta da idanu...
Girgiza kai Nabila tai cikin sauri don bataso Mamy ta fahimci wani abin kana tace “A’a basumin komai ba kawai dai na tambaya ne.....” Kan Mamy ta kuma jefo mata wata tambayar ya mik’e ta d’au markad’en kayan miya ta zuba cikin blender....
Girgiza kai kurum Mamy tai kana tace “Allah sa dai ba wani tsaurin idon kika masu ba don nasan halinki....”
Bata jira cewan Nabilar ba tai ficewarta...
Nabilah da Marliya suka kalli juna suna k’unshe dariya,Marliya tace “Mamyna case... Addah Naby kema dai Dan Allah ki daina tinzira Mamy sai kuyi zaman lafiya...”
Harara Nabila ta galla mata kana tace “Ke idan aka biyeta Mamy toh fah a gidan nan ma sai aci kashi akanmu, k’yaleta kawai haka zanci gaba da lallab’a kayana wataran zatai missing masifar nawa da taro mata magana...”
Da mamaki Marliya ke dubanta kana tace “Addah did I hear you right...? Kikace wataran Mamy zatai kewar fad’anki, uhm kodai kodai Mamy ta kusa yin sirki ne....”
Ludayin gefenta ta janyo zata kwad’awa Marliya, Marliya ta sukunya tana dariya kana tace “Kinga gaban mangyad’a nike kiyi hak’uri don Allah, nifah kawai tambaya nai.....”
K’wafa Nabilah tai kana tace “Dama baki sunkuya ba, wllhi Allah sawak’e na tsaya kula wani namiji bayan duk halinsu guda ne, ga Addah can tayi auren wahala bataji dad’i ba ga Mamy ma ba wani dad’in auren takeji ba Aunty Bara’atu mijinta kullum baya nan wayasan uwar mai yake tsinanawa a can barikin, zamana a gida gaban iyayena yafin zaman gidan wani gardi da idan yamin badaidai ba garin nan sai ya mana kad’an don wllhi da ace ni ce Ya Hafiz ke aure da tuni ya gama shiga taitayinsa...”
Sallaman Aunty Lami ne ya katsesu... Marliya ta amsa da sakin fuska yayinda Nabila ta tab’e baki taci gaba da abinda take...
Lek’owa kitchen d’in Aunty Lami tayi tana fad’in “A’a ‘yanmatan gidan ne a kitchen, iyye kaga yaran Mamy....”
Idan kayan miyan da take juyewa cikin tukunya sunyi magana itama zatai magana, Marliya ce dai gaisheta fuska fal fari’a kana tace mata Mamy na ciki...
Har saida Aunty Lami ta ambaci sunan Nabila kafin Nabilar ta juyo a tak’aice tace da ita ina kwana... Shikenan gaisuwar bata kuma cewa komai ba...
Jin muryar Aunty Lami yasa Mamy fitowa suka soma gaisawa, nan Aunty Lami d’in ke sanar da Mamy zata gidan Yayarta Rabi bataji dad’i ba....
Mamy tace “Ayya Allah ya bata lafiya, kinsan shigowar daminan nan sai a hankali yanayi ya canza sai ayiya cututtuka...”
Aunty Lami tace “Wllhi fah Mamy abin saidai addu’a...”
Mamy tace “Haka ne ki gaidata da jiki....”
Aunty Lami ta amsa da “zataji sai na dawo...”
Mamy ta amsa mata da “A dawo lafiya...”
Nabilah na kitchen tana kwaikwayon maganan Aunty Lami kana tai k’wafa tace “Salon munafunci...” Juyowa tai ta dubi Marliya dake dubanta da mamaki kana tace “Ke kuma idan ina waje kika kuma biyewa wannan munafukar matar tana wani jan mutane da wasa wllhi kema sai na daina miki magana tam...”
Dariya kawai Marliya tai kana tace “Um naga dai matar babanki ne don haka itada Mamy matsayinsu d’aya, besides Aunty Lami battada matsala tun tasowarmu haka muka gansu zaune lafiya da Mamy....”
Tray mai d’aukeda ruwan sanyi Mamy ta hanga gefen fridge da alama Marliya ta mance bata kai masu ba, Nabilah ce gefenta tana had’a tray d’in abincin Mamani nan Mamy ta umarceta ta bar abinda take takaiwasu Abbah da bak’insa ruwa...
Sam Nabila batason shiga kan mutane don tasan wani cikin bak’in ya fad’i mata ba daidai ba tana iya danna masa mummunar kallo wanda har sai sun had’a idanu bak’on ya fahimci haka idan kuwa babu Abbah wajen ta jifa masa magana tai gaba abinta....
Badon taso ba ta d’auki tray d’in ta nufi sashen Abbah, sam bata kawo zatai artabo da mutum mai irin kamanninsa ba cikin gidansu, wani wawan birki ta danna tana mai kuma k’yafta idanu alamun badai gizo yake mata ba, tabbas shi d’in ne, Innalillahi toh mai yakeyi a gidansu, mai ya kawosa gidansu harma parlorn Abbanta, wannan wane irin mutum ne tai gamo dashi, kardai yasan Abbanta ne...?
Haka tayita jerowa kanta tambayoyi babu mai amsa mata su, Khalid kuwa tamkar ance ya juya sukayi idanu hud’u da Nabilah dake tsaye wajen tamkar an dasata, murmushi ya sakar mata had’ida kashe idanu guda irin taji mamakin nan koh....
Lokaci guda tai saurin saita kanta kana ta nufi parlorn kanta a k’asa, gaisuwan jam’u ta masu don bata fatan dogon gaisuwa ya shiga tsakaninta da d’aya daga cikinsu....
Sauri sauri ta fice daga parlorn k’irjinta naci gaba da bugu....
Saida ta sami bango ta tokare take iya sauk’e numfashi mai nauyin gaske, murmushinsa kurum take hangowa wanda ya kasa b’acewa daga k’wayan idanunta, da ace bata ganshi sau biyu kafin yau ba k’ila tace kamanni sukayi don ta tabbata babu abinda ya had’a Abbanta da wannan mutumin, toh amma shid’in ne dai, toh wai waye shi ne kam.... A hankali ta lumshe idanunta domin kuwa izuwa wannan lokaci lamuran mutumin ya soma bata tsoro...
Aunty Lami ce tazo zata shige ta kafe Nabilah da idanun ganinta cikin yanayi wanda bata tab’a ganinta cikin irinta ba...
K’arasowa tayi had’ida dafata kana tace “Nabila lafiya kike....?”
Sai sannan Nabilah ta bud’e idanu tana duban Aunty Lami....
Saurin turb’une fuska tayi kana tace “Lafiya mana Aunty... Barin shige...”
Bata jira cewan Aunty Lami d’inba tai shigewarta....
Kallo Aunty Lami ta rakata dashi tana mai nazarinta, gyara mayafinta tai kana tasa kai ta nufi parlorn Abbah....
Ganin da bak’i a parlorn ya sanyata sakin fuska sosai yawa mutuniyar k’warai tana wani aza mayafi ta k’arasa tana fad’in “Bak’i ne mukayi... Sannunku da zuwa....”
A tare Shamsu da Khalid suka soma gaidata kafin Sameer ya had’iye abincin dake bakinsa shima ya d’ora da gaisuwan a lokacin da ya d’ago fuskarsa....
Wani irin mummunar fad’uwan gaba ne ya dirarwa Aunty Lami sanda tayi tozali da idanun Sameer, ta kasa amsa gaisuwan da ya mata ta kuma kasa daina kallonsa, badon a zaune take ba tabbas da jiri ya iya kayarda ita....
Abubuwan da suka faru shekaru 30 baya suka shiga dawowa kwanyarta, har saida Abbah ya furta “Lami ana gaisheki ko bakiji bane...”
Sannan Aunty Lami ta iya kimtsa kanta....
Murya a d’an sark’afe ta amsa murmushin yak’e bai bar saman fuskarta ba....
Sauri sauri ta fice daga parlorn ta nufi nata sashen ta d’auki wayarta babu shiri....
Hajiya na faman rabon fad’an Hafiz da Sahariyya kan tak’urawa d’iyarsa Kausar da Sahariyya keyi taji wayarta na faman ruri cikin d’aka...
Fad’i take “Ku kuka sani ku cinye kanku idan bazakuji maganata ba, wannan yarinya taka mai jinin tsiya a tareda ita gwarama kayi auren ka kaita can wajen matarka ta kular maka da ita...” Tana ida fad’in haka ta nufi d’aki tana lalumar wayarta yanda ta tadda wayar ta katse, ganin wacce tai mata kiran ya sanyata saurin sake dialing layin....
Hafiz dake mak’ure da wuyan Sahariyya fad’i yake “Wllhi kinji na rantse babu yanda zankai Kausar nan gidan zata girma tinda ku kuka tilastama uwarta barinta don haka dole ku kula da ita, kin sanni kinsan banida kyau kukan yarinyar nan na sakeji wllhi sai nayi ajalin idanunki k’wara... Shashashar banza...”
Yana ida fad’in haka yayi jifa da ita kana yayi ficewarsa sai faman fito yake hula a karkace ya nufi wajen sahibarsa Sawwama.....
Tinda Aunty Lami ta d’auki wayar Hajiya ta fahimci babu lafiya.....
“Wai meke faruwa ne ni dan Allah ki sanar dani.....” Hajiya tace hankali tashe...
Aunty Lami ta samu jikin gado ta jingina kana tace “Haule anya kin tabbata Ma’aruf ya mutu...? Haule anya Ma’aruf ya zama tarihi kaman yanda muke tunani, anya Ma’aruf bazai dawo garemu ba....?”
Dukda bugu da k’irjin Hajiya keyi bai hanata dariyar yak’e ba kana tace “Haba Lami meye kuma kike neman maida mutane baya ana ci gaba a rayuwa, wane irin Ma’aruf...? Idan dai Ma’aruf d’an gidan Usman Mailafiya ne ya jima da mutuwa saidai mai kamanninsa, kinga kima daina sak’awa zuciyarki wannan mummunar zato don Allah....” Ta k’arashe tana zama bakin gado....
Girgiza kai kurum Aunty Lami take tamkar Hajiyan na dubanta kana tace “Inaga dai baki fahimci abinda nake nufi bane Haule amma idan da hali yau d’in nan mu had’u gidan Aminiyar sirri ta fad’i mana gaskiyar abinda tayida Ma’aruf Mailafiya don wllhi yau nikam nayi tozali dashi a raye....”
Jikin Hajiya ya d’anyi sanyi, gyara zamanta tai kana tace “Shikenan Lami mu had’u gobe gidan Aminiya tinda dai yaukam kinga dare yayi, ke nake jiyewa kinsan wannan baud’edd’en mijin naki ba bari zaiyi ki fice ba ni kuwa nawa mijin dama a tafin hannuna yake... Ma had’u goben....”
Aunty Lami ta amsada “Toh shikenan Alhaji na fita Kasuwa zan fito...”
Daga haka sallama sukayi ko waccensu tana sak’e sak’e cikin zuciyarta.....
***
Washe gari haka Nabila ta tasa Mamy gaba da tambaya ko tasan bak’in Abbah...
Mamy ta umarci Marliya data kwashe dankali cikin mai kana ta dubi Nabilah dake shirya wanke wanken plates cikin drawer tace “Kici gaba da tambayata abinda bai shalleki ba kar kiyi aikin dake gabanki....”
Nabilah ta turo baki gaba tace “Kai Mamy tambaya shikenan ya zama laifi ai da Marliya ce ko Addah suka tambayeki amsasu zakiyi, Mamy Dan Allah su wayesu...?”
Girgiza kai kurum Mamy tayi kana tace “Nabilah ban sansu ba hasalima ban shiga parlorn ba har dai suka tafi kina gani ai... Toh yaya za’ayi na sansu kin kuma san Abbanki kinsan wane irin mutum ne ba kasafai yakeso ana haurawa kansa ba musamman idan yana tareda bak’i, ballanata ma kinsan ba shigan zanyi ba idan ba shine ya buk’aci hakan ba... Wai me bak’in suka miki ne...?”
Ta k’arashe maganar tana mai jefo mata tambayar had’ida tsareta da idanu...
Girgiza kai Nabila tai cikin sauri don bataso Mamy ta fahimci wani abin kana tace “A’a basumin komai ba kawai dai na tambaya ne.....” Kan Mamy ta kuma jefo mata wata tambayar ya mik’e ta d’au markad’en kayan miya ta zuba cikin blender....
Girgiza kai kurum Mamy tai kana tace “Allah sa dai ba wani tsaurin idon kika masu ba don nasan halinki....”
Bata jira cewan Nabilar ba tai ficewarta...
Nabilah da Marliya suka kalli juna suna k’unshe dariya,Marliya tace “Mamyna case... Addah Naby kema dai Dan Allah ki daina tinzira Mamy sai kuyi zaman lafiya...”
Harara Nabila ta galla mata kana tace “Ke idan aka biyeta Mamy toh fah a gidan nan ma sai aci kashi akanmu, k’yaleta kawai haka zanci gaba da lallab’a kayana wataran zatai missing masifar nawa da taro mata magana...”
Da mamaki Marliya ke dubanta kana tace “Addah did I hear you right...? Kikace wataran Mamy zatai kewar fad’anki, uhm kodai kodai Mamy ta kusa yin sirki ne....”
Ludayin gefenta ta janyo zata kwad’awa Marliya, Marliya ta sukunya tana dariya kana tace “Kinga gaban mangyad’a nike kiyi hak’uri don Allah, nifah kawai tambaya nai.....”
K’wafa Nabilah tai kana tace “Dama baki sunkuya ba, wllhi Allah sawak’e na tsaya kula wani namiji bayan duk halinsu guda ne, ga Addah can tayi auren wahala bataji dad’i ba ga Mamy ma ba wani dad’in auren takeji ba Aunty Bara’atu mijinta kullum baya nan wayasan uwar mai yake tsinanawa a can barikin, zamana a gida gaban iyayena yafin zaman gidan wani gardi da idan yamin badaidai ba garin nan sai ya mana kad’an don wllhi da ace ni ce Ya Hafiz ke aure da tuni ya gama shiga taitayinsa...”
Sallaman Aunty Lami ne ya katsesu... Marliya ta amsa da sakin fuska yayinda Nabila ta tab’e baki taci gaba da abinda take...
Lek’owa kitchen d’in Aunty Lami tayi tana fad’in “A’a ‘yanmatan gidan ne a kitchen, iyye kaga yaran Mamy....”
Idan kayan miyan da take juyewa cikin tukunya sunyi magana itama zatai magana, Marliya ce dai gaisheta fuska fal fari’a kana tace mata Mamy na ciki...
Har saida Aunty Lami ta ambaci sunan Nabila kafin Nabilar ta juyo a tak’aice tace da ita ina kwana... Shikenan gaisuwar bata kuma cewa komai ba...
Jin muryar Aunty Lami yasa Mamy fitowa suka soma gaisawa, nan Aunty Lami d’in ke sanar da Mamy zata gidan Yayarta Rabi bataji dad’i ba....
Mamy tace “Ayya Allah ya bata lafiya, kinsan shigowar daminan nan sai a hankali yanayi ya canza sai ayiya cututtuka...”
Aunty Lami tace “Wllhi fah Mamy abin saidai addu’a...”
Mamy tace “Haka ne ki gaidata da jiki....”
Aunty Lami ta amsa da “zataji sai na dawo...”
Mamy ta amsa mata da “A dawo lafiya...”
Nabilah na kitchen tana kwaikwayon maganan Aunty Lami kana tai k’wafa tace “Salon munafunci...” Juyowa tai ta dubi Marliya dake dubanta da mamaki kana tace “Ke kuma idan ina waje kika kuma biyewa wannan munafukar matar tana wani jan mutane da wasa wllhi kema sai na daina miki magana tam...”
Dariya kawai Marliya tai kana tace “Um naga dai matar babanki ne don haka itada Mamy matsayinsu d’aya, besides Aunty Lami battada matsala tun tasowarmu haka muka gansu zaune lafiya da Mamy....”