Sashe 45
Cigaban Kurkukun Kaddara Takun Karshe Complete · about 8 min read
ne abunda nake hasashe tabbas Wani ya ceto rayuwar Angel ina bayan na jefata a cikin ruwa tun da gashi har rigarta ta bayyana... Ba zato ba tsammani, suka ga mutumin da suka kora ya watso da gudu ya dawo wurin rigarsu, har sun har zu a zasu fara dukanshi da sandunan su sai kuma suka fasa ganin Ya dam o rigar da danejo ta shanya kan bukka, ru e rigar yayi a hannunshi zuciyarshi na bugawa da matsanancin karfi ya soma ambaton sunan Angel Angel, Lokaci aya su bawuro da su hasiya suka kalli juna da mamaki jin yana ambaton sunan yarinyar da danejo ta tsinto a cikin ruwa, tambayar shi suka soma yi wanene shi? Ya akai yasan yarinyar? Hawaye na zuba daga idanunsa ya dago rigar yana nuna masu yace" wannan rigar ta ata ce Angel, da hannuna na jefa ta cikin ruwa, dan Allah ku fada min a ina kuka samu rigar? Ko dai kune kuka ceto rayuwarta....." kukane yaci karfinsa, gaba daya ya rikice masu, su kansu so suke son san me yake cewa don suji ko shine mutumin nan da yarinyar take nema don bazasu ta6a mantawa ba da irin kukan data dinga yi masu tana kaisu bakin ruwa donsu nemo mata daddynta tun basu fahimtar me take cewa har suka gane cewa wani nata ne take nema.. Danejo ce ka ai ta fahimci me Yake cewa, nan take ta fashe da kuka Cikin harshen fulatanci ta sanar ma sauran an uwanta abun da taj Ya ke fa i nan suka gane cewa shine mahaifin Angel, yarinyar data tsaya masu aransu, har yau har gobe basu cireta aransu ba, hakika sunyi farin ciki mara misaltuwa da ganinsa. Tsabar farin ciki yasa danejo ta watsa da gudu ta fada kan kirjinsa ta rungume shi tana kuka, ta soma tambayarshi ina Angel? Ko ya ganta"? Hankalin shi ba karamin tashi yayi ba, a ru e ya tambaye ta me take nufi? Ba su suka taimake ta ba" cikin sanyin murya danejo ta labarta mashi komai daya faru tun daga lokacin da ta tsintota a cikin ruwa har zuwa time da ta gudu daga rigar su. Wani irin jiri yaji yana shirin kwasarshi saboda kuncin dayaji, bakomai ne ya jawo mashi jinkirin da yayi ba nazuwa daukarta face loosing memory din da yayi. Zubewa yai kan gwiwowinsa zuciyarsa a hautsine tamkar zata buga, gaba aya suka kewaye shi, suna kallon shi gwanin ban tausayi, ganin yadda ya ke matsar kwalla. Saboda son da suke ma Angel yasa suka yi mashi kyakkyawar tarba, a kalla ya shafe wata a rigar su, kafin Yaji bazai iya cigaba da zama a dajin ba, kwara ya koma gida watakil idan yaje can ya sameta ta koma wurinsu Aneelerh. Ranar da taj ya shirya tafiya, zai bar rigar, ya yi masu bankwana kamar karsu rabu, yace masu zai fara zuwa wurin mutanan da suka taimake shi kafin ya wuce garin su, guzurin tafiya suka hada masa, kowa ya kawo abunda yake dashi, suka bashi sannan sukace mashi idan Allah yasa yaga yarsa angel ya fada mata sunyi kewarta, zuciyarshi cike fal da kewarsu ya kamo hanya zai bar rigarsu, harfa yayi nisa yajiyo takun gudunta sai faman kwala mashi kira takeyi, a hanzarce ya juya yana kallonta, danejo ce hannunta ru e da kullin kayanta, hankalin shi ba karamin tashi yayi ba, ganin ta biyo shi. Karasowa tayi tana haki tace"dan Allah ka tafi dani inason ganin Angel" Girgiza mata kai yayi"kiyi hakuri bazan iya tafiya dake ba, meyasa kika yarda dani har haka? ki yi hakuri ki koma wurin an uwanki" fashewa tayi da kuka. Ana cikin haka, yajiyo sautin takalman yan uwanta kusan gaba dayansu ne suka biyota. Fuskokinsu babu walwala, ru o hannunta kakansu yayi tare da mika ma taj, da mamaki yake kallonshi don bai fahimci me yake nufi ba, har saida yayi mashi da kurmanci Ya nuna mashi cewa ya tafi da ita, sun bar mashi ita, saboda tace in har basu bari tabi shi ba, to zata kashe kanta ne, shiyasa suka yanke shawarar kwara su bar mashi ita, don ko sun barta ba lallai su iya shawo kanta ba. Babu yadda taj baiyi da su ba akan subar yarsu, hankalinsu sai yafi kwanciya idan tana akusa da su amma suka sanya kafiya akan dole ya tafi da ita, ganin ya turje ne yasa suka fada mashi cewa marainiyace, tun kafin ta mallaki hankalin ta iyayenta suka rasu, bata ta6a neman wani abu daga gare su tarasa ba, don haka sun bashi amanarta, yaji tsoron Allah ya rike masu ita amana su je can su yi aure, hawaye ne suka wanke fuskarshi, jiki asanyaye yasa hannu ya ru o hannun danejo,yayi masu alkawarin bazai ta6a bari ta nemi wani abu ta rasa ba, zai dauki dukkan wani nauyi nata zai bata kulawa, sunji dadin abunda ya fada masu a karshe sukayi bankwana da junansu, yaja hannun danejo suka nufi rigarsu Habu. har sun fidda rai da sake ganin shi, tsawon kwanakin da yayi a rigarsu danejo kusan kullum sai sunzo neman shi a yar bukkarsa, sunyi mamakin ganin ya dawo masu tare da yar matashiyar budurwa, cikin harshen fulatanci danejo tayi masu bayanin komai dangane da taj...." labarin tajudden da Angel ya ta6a zuciyoyinsu, har hawaye suka zubda masa saboda tsananin tausayin shi da suka ji, bayan komai ya lafa ya sanar da su zancen tafiyar shi, ba don sunso ba sukayi mashi fatan alkhairi da addu'ar Allah yasa yaga yarinyarsa, kafin tafiyarsa saida suka hada mashi shatara na arziki, bayan haka suka yi masu rakiya har zuwa bakin titi, ba su tafi ba sai da sukaga ya samu motar hayar da zata shigar da shi cikin garin joss tukunna sukayi mashi bankwana. Tun da suka shiga motar, danejo ta kankameshi, kamar wani yace zai kwace mata shi, wani irin mugun tsoron mutane take ji, mutun ayane ta yarda dashi ta kuma damka amanarta agareshi saboda tasanyawa ranta cewa bazai ta6a cutar da ita ba. Kafin su karasa cikin garin, tuni bacci yayi awon gaba da ita, a yayin da kanta ke asaman kirjinsa, hankalin taj sam ba akwance yake ba, saboda fargaban kada miyagun da suka kai mashi farmaki su gansu, yasan muddin sukasan cewa bai mutuba, to kuwa zasu nemi hanyar da zasu kashe shi ne kamar yadda suka kashe dan uwansa uzair, mutuwar da tayi matu ar girgiza shi, dabara ce ta fado mashi da sauri ya sanya hannu ya cire gyalen danejo da take daure qugunta da shi, ya lullu6e fuskarsa, Idanunsa ne kadai suke a bude. Bayan isarsu joss, motar ta sauke su a tasha, driver yace ina kudin mota, sai lokacin ya tuna da baida ko sisi, sai dai kayan da fulanin nan suka bashi, hakuri ya bashi ya hada shi da katon dawon fura, mai motar baiyi gardama ba ya kar6a, ruko hannun danejo yayi suka soma tafiya atare har ya sama masu abun hawan da zai kaisu unguwar da su ke, kafin isar su tuni dare ya ritsa da su. Da farin cikinsa Ya zo unguwar, amma lokacin dayaga gidajensu a kulle, nan take murnar ta koma ciki, tunkafin ma yaji abunda ya faru hankalinsa yai mugun tashi, baisan ina zai tsoma kanshi ba, ga yar mutane da yake ta yawo da ita, harta fara yi mashi kukan yunwa take ji, tausayinta ne ya kama shi, da ya san hakan zata faru dabai yi kuskuran tafowa da ita ba.. A bun hawa ya kuma tsaida masu, suka nufi gidan uncle abdalla da ita don ya ga ko sun dawo daga south korea, tunkafin me abun hawan da ya kawo su ya sauke shi ya hango gate din gidan a kulle alamar basa nan, tamkar ya daura hannu aka ya fasa ihu haka yaji. Tunawa da amininsa muhsin wanda Angel ta ta6a sace ma matarsa waren takalmi yasa shi yanke shawarar zuwa gidan shi tare da danejo, yasan acanne zai ji komai daya faru bayan 6acewarsu Basu sha wahala ba, cikin sa'a suka same shi agida, tare da matar shi, lokacin dayaji sallamar taj a firgi ce ya mike zaune yana kallon kofar shigowa falon, bai gane shi ba har saida ya cire mayafin danejo dake akan fuskarsa tukunna ya shaida shi, muryarshi na rawa yace taj! Dama kana araye? Tsawon lokaci muna ta neman ku babu kai ba uzair duka an nemi ku an rasa"? A rude yake jefa mashi tambayoyin, matarshi da sauri ta nufi danejo ta ruko hannunta suka zauna kan sofa, kafin ta mike ta shiga ciki ta kawo masu abinci da ruwan shi. "Dan Allah abban muhsin kabarshi Ya huta, bakasan daga ina yake ba, sannan bakasan meya faru dashi! Idan har bai samu nutsuwa ba tayaya zai iya fayyace mana abunda ya faru da su"? Fuskarta a yamutse tayi maganar, jinjina kai yayi fuskarsa da tsantsar al'ajabi yace da taj su shiga ciki yayi wanka ya canza kayan jikin shi, yaga duk sun jigata kamar na almajirai, Bayan sun huta, sunci sun koshi, har bacci yayi itama danejo ta dan runtsa, wuraren karfe shabiyu na dare yafarka ya taras da muhsin ya zabga uban tagumi yana kallon shi, mamakine yacika shi. "Ka yi hakuri taj, kada kaga na takura maka, wallahi na damu da rashin ku, hankalina bazai ta6a kwanciya ba har sai ka fadamin meya faru da ku da har kuka gudu aka neme ku aka rasa......" Mikewa zaune taj yayi, kafin a tsanake ya labarta masa komai daya faru, wani irin matsanancin kuka mai cin rai muhsin ya fashe dashi, bakomai ya firgita shi ba ya kuma bashi tsoro face mutuwar amininsu uzair ta yi matu ar girgiza shi, cikin shesshekar kuka ya ke fadin"taj dama abunda ya faru daku kenan? Inna lillahi wa'inna ilaihirraji'un wannan wata irin masiface, Uzair ya mutu, Angel ta 6ace, rana aya an tarwatsa farin cikin zuri'arku, in sha Allah sai Allah ya saka maku wannan zaluncin da akayi maku....."muhsin ya yi kuka tamkar ransa zai fita, Lallashinshi taj ya somayi yana fadin yayi hakuri komai ya riga daya wuce, yanzu shi damuwarshi ina aneelerh take matar uzair"? yar muhsin Ya samu nutsuwa, ya fara mashi labarin abunda Ya faru bayan 6acewarsu, Yaji dadin jin cewa