← Book details Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 99 OF 211

Sashe 99

Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Are u angry?" tana haka taji ya jefo mata tambayar, juyowa tayi suka had'a ido tay shiru bata bashi amsa ba, "I'm asking you!" Ya sake fad'a, saida ta d'an had'iya miyau kafin a sanyaye tace "a'a kawai dai naji ba dad'i ne, saboda ni kazo kuma gashi kace bazaka ci Abinci bana at least ko d'an Yaya ne sai ka ci pls" d'an murmushi yay bai ce komai ba tana ta kallon shi can taji yace Ok zai ci sai taji dad'i, washe baki tay tana yar dariya sosae taji dad'in cewa da yayi zai ci don ko ba komai hakan ya nuna zata iya sashi abu, mik'ewa tayi tace suje ya taso shima ya mik'e, bayan sunje dining area d'in da kanta taja mashi kujera ya zauna, fara serving nashi tay ta zuba mashi farar shinkafar da veg soup d'in bata sa da yawa ba don tana son sauran ma yaci, a nutse ya fara ci tana zaune daga gefen shi can ya kalleta yace ita bazata ci ba tace sai ta gama Serving nashi, da kai yay mata alamar ta zauna ta ci murmushi tayi ta mik'e don ta zuba, yana kusa gama cinye shinkafar ya aje spoon d'in tana ganin haka tay saurin mikewa ta fara zuba mashi taliyar itama yar kad'an tasa ta janye plate d'in gaban shi ta tura mashi na taliyar ganin haka yasa shi d'agowa yana mata wani kallo cikin marairaicewa ta d'an langa6ar da kai tace "pls shima bai da yawa ai" cigaba da kallon ta yay yana d'an motsa baki kokarin mikewa ya fara yana fad'in bai san a ina take son ya zuba shi ba wannan ma ya gaya mata ai a k'oshe yake kawai sai ji yay ta kawo hannu ta ruk'e nashi alamar kar ya tashi ita kanta bata san ya akai ta aikata hakan ba, dakatawa yay ya kai idon shi akan farin hannunta dake a ruk'e da nashi kafin ya d'ago ya kalleta sai d'an zare ido take gabanta na faduwa, a hankali ta saki hannun nashi tare da sadda kanta k'asa bayan d'an lokaci jin shiru yasa ta d'an d'ago idanunta ta kalle shi karaf suka had'a ido yana ta kallon ta yan kame kame ta shiga yi ta kasa tsaida idon ta cikin nashi don idanun shi nada kaifi bazata juri irin kallon ba,

"Ka yi hak'uri, dama don Saboda kai ne akayi shiyasa" tana d'an kikkafta idanu ta fad'i hakan, bai ce komai ba sai gani tay ya kai hannu ya d'auki fork d'in ciki ya fara ci a nutse har bata san lokacin data saki murmushi ba ta koma ta zauna, kaman rabin wanda ta zuba mashi yaci tana ganin ya aje fork ta d'ago ya d'age mata gira yace Shikenan hakan yayi mata ya ci kai ta d'aga mashi still da d'an murmushi sai kuma tace amman da sauran wanda bai ci ba wani kallo mai kaman harara ya wurga mata tayi dariya tare da mik'ewa, pepper chicken d'in ta bud'e tasa mashi k'atuwar cinya hada tambayar shi ta k'ara yay mata shiru yana dai ta kallon ikon Allah don hakan bak'on abu ne a wurin shi yace bazai yi abu ba a matsa mashi zai iya cewa ba wanda ya ta6a mashi haka, turo plate d'in tayi gaban shi bayan ta janye na taliyar tace gashi itama ya ci don Allah ba yawa abu d'aya ne kawai, maida bayan shi yay jikin kujerar da yake zaune ba alamar zai ci sosae ta marairaice fuska tana mashi yar shagwabar ya ci daga shi shikenan, k'arshe dai saida tayi nasarar saka shi yaci cinyar rabi da kan shi ya tsiyaya ruwa a cup yasha kad'an yana k'ok'arin mik'ewa tace lemu fa ya d'an d'aga mata hannu, ganin ya tashi yasa itama ta rufe sauran abinciccikan ta biyo bayan shi, kujerar daya tashi ya koma ya zauna itama ta sake zama a gefen shi, bata dad'e da zama ba taji yace ita bata wanka ne har saida taji yar kunya tana d'an murmushi tace tana yin wanka sosae don kada ta barshi shi kad'ai ne yasa bata je ta yi ba, shiru ya d'an yi sai kuma taji yace taje tayi zasu je government House tare, har saida gaban Fauzy ya d'an fadi jin inda yace zasu je amman bata nuna komai ba tace mashi to,

"Amman lafiya lou a barka kai kad'ai ko in ma Auntynah magana?" ta fad'a bayan ta mik'e da bud'ar bakin shi sai cewa yay tayi mashi mi tace wai ko ta taya shi hira, d'an yamutsa fuska yay ya fara k'ok'arin mik'ewa bayan ya tashi tsaye yace zai jira ta a Mota amman kar tay keeping nashi bai hakurin haka ta d'aga mashi kai ya nufi hanyar fita daga parlon tabi bayan shi da ido har ya fuce, wani k'ayataccen murmushi ta saki tana jin son shi na ratsa mata zuciya tabbas tasan indai ta aure shi ba k'aramar mai sa'a bace ita, da sauri ta nufi hanyar Bedroom d'inta tana zuwa direct toilet ta nufa a can ta cire Uniform d'in jikinta, after some few minutes ta fito d'aure da towel a kirji ta nufi gaban dressing mirror, shaf shaf ta d'an yi yar light makeup bayan ta gama ta nufi wurin kayanta dake a cikin Wardrobe d'in bango, bata tsaya ruwan ido ba ta yanke ta saka jallabiyar da Fatuu ta bata dama sau d'aya ta ta6a saka ta da zasu je shopping dasu Hanif, bayan ta saka gaban mirror ta koma cikin sauri ta gyara fakin din gashinta sannan ta shiga nad'a gyalen rigar, sosae tayi mata kyau dama itama tasan tana mata kyaun shiyasa ta saka ta, takalma half cover da yar karamar side bag duk bak'ak'e ta saka saida ta gama shiryawa ta tuna bata fad'i ma Aunty zancen fitar ba, wayarta ta fiddo don ta kirata sanin Abban Hanif na nan, a cikin parlor suka had'e da ita bayan ta sanar mata ta waya tana ganinta ta hau yin murmushi tana fad'in kaga Matar d'an Governor, tambayar ta tayi amman dai yaci Abincin ko tace eh kowanne saida tasa ya ci duk da bada yawa ya ci ba Auntyn tace "yayi kyau hakan ma lafiya lou tunda dai ya ci kwalliya ta biya kudin sabulu, yanzu sai government House kenan your excellency?" Yar dariya Fauzy tay tace mata eh haka yace tace Ok sai sun dawo, saida ta rakota har bakin kopar parlon tana k'ara koya mata yadda zata rink'a mashi tace ta gaida mata da iyalan Governor, yana a d'an kishingid'e idanunshi a lumshe ta shigo cikin Motar bayan driver ya bud'e mata, slowly ya bud'e idon nashi ya sauke su akanta da murmushi tayi mashi sannu tace Allah yasa dai bata bar shi yana ta jira ba shiru kaman bazai tanka mata ba can ya d'an gyara zama yace kaman haka, saida driver d'in ya tambayi umarni kafin yaja Motar, suna cikin tafiyar idon Fauzy a gefe ba zato taji ya kawo hannu ya kamo nata hannun wani irin d'umi taji ya ratsa nata hannun taushin hannun shi kuwa ba sai an fad'a ba, kallon shi tay idanun shi na akanta da kai yay mata alama ta matso, shiru tay kaman bazata matsa ba sai kuma ta d'an matsa da kanshi ya k'ara matso da ita ya rungumeta ta gefe wani iri Fauzy ta ji don tasan hakan bai dace ba tunda ba d'aura masu aure akai ba bai kamata suna had'a jiki ba, shiru tay kanta na a saman kafad'ar shi haka hannunta guda daya fara ruk'owa har lokacin yana a ruk'e dashi tay lamo ta kasa yin wani yunk'uri na raba jikinta da nashi, bayan sun isa Government House d'in baza ido Fauzy tay tana k'are ma ko ina kallo ta yadda baza'a ga k'auyancin ta ba, lokacin data ganta gata ga first lady wadda k'awar Mom d'in Sameer ce mamaki da dad'i ne suka cikata don abu ne da bata taba zaton zai faru ba a rayuwar ta, cikin faram faram ta tarbeta bayan sun gama gaisawa fuska a sake ta d'an yi mata tambayoyi da suka shafeta Fauzyn na amsa mata Sameer na zaune akan d'aya daga cikin lafiyayyun kujerun da suke zaune daga baya ya mik'e ya nufi ciki Fauzyn na kallon shi har ya 6ace ma ganinta tayin Abinci First Lady tayi mata tace gashi can a table tana murmushi tace mata wllh a koshe take ta gyad'a kai, d'akin yaranta ta kai Fauzyn wai tafi sakewa yan mata biyu ne ta gani a d'akin d'aya zata yi sa'ar ta d'ayar kuma zata d'an girme ta, gaba d'ayan su daka kallesu zaka gane hutu ya zauna masu a jikinsu ga fatar su har wani shek'i take duk da ba farare bane can amman kuma baza'a kira su da bak'ak'e ba gaba d'aya k'ananun kaya ne a jikin su, sosae suka sake ma Fauzy babbar na d'an tambayar ta game da ita da yadda suka had'u da Sameer muryarta gwanin dad'i a gayance take magana, tun dai Fauzy bata saki jiki ba har ta saki suka shiga yin hira sosae anan ita babbar take ce mata gaskiya tayi dacen miji don Sameer k'arshe ne a komai amman ita bazata iya auren shi ba har saida Fauzy ta d'an ji mamaki ta kasa hak'uri ta tambayi dalili cikin yamutsa fuska Ammah tace mata ego d'in shi yayi mata yawa dole matar shi ba k'aramar dawainiya zatayi da shi ba ita kuma hakan ke bata iyawa, shiru Fauzy tayi tana d'an murmushi tasan ba k'arya tayi ba a ranta ta raya to dama Mulki ya had'u da Mulki taya d'aya zai dawainiya da d'aya.
Chapter 99 · 0% Book details