← Book details Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 92 OF 211

Sashe 92

Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Bayan Fauzy ta gama komai ta kwanta ta fad'a duniyar tunanin Sameer, a yanzu ta gane tana son shi don da kafin suji bayani game dashi fargabar kada ace yana da wani mummuna hali ce ta kamata amman yanzu tunda taji bayanin da Haisam d'in yay take jin wani irin farinciki a cikin ranta sai faman yawo Sameer d'in yake mata a rai tun ma Fatuu na nan, hannu ta kai gefen filon data d'aura kanta ta d'aukko wayarta, bayan ta bud'e gallery ta shiga ta bud'o hoton shi ta k'ura ido tana kallo, zuciyar ta ce ta shiga raya mata in dai ta aure shi tabbas ba K'aramin dace da sa'a tayi ba wllh don ta ko ina Sameer yafi k'arfinta nesa ba kusa ba, shiru tayi tana cigaba da kallon hoton fuskar ta da d'an murmushi a zuciyarta ta shiga fad'in "da gaske kana sona ko kuwa matsayin taimakona zaka Aure ni" shiru tay don bata da amsar da zata ba kanta, tana ta faman zooming hoton tana k'are mashi kallo ji take kaman ta kira shi don sai taji tana son jin muryar shi, a ranta ta raya to in ma ta kira shi d'in tace mashi mi wata zuciyar tace ta gaishe dashi kamar yadda take yi, kokonton kiran nashi ta shiga yi k'arshe ta yanke bazata kira shi ba gaskiya kada yay tunanin ko don Saboda Maganar neman auren nata ne yasa ta kira, "to kuma in ba ki kiran nashi taya zai sake maki har ku saba tunda dai shi ga irin halin shi, kamata yay ki fara k'ok'arin jawo shi a jiki yadda zai sake maki har kiyi abunda Ya Haisam yace na raba shi da matan dake bibiyar shi" zuciyar tace ta raya mata hakan tay shiru tana ta d'an cizon k'umbar babban yatsanta gani take kaman hakan ba abu bane mai sauk'i can dai ta fita daga cikin gallery d'in ta koma phone bayan ta nemo number d'in shi saida tay d'an jimm kafin tay dialing nan take ta shiga, duk bugu d'aya tare yake da fad'uwar gabanta sosae fargabar kiran shi ta kamata yau ba kamar sauran lokuttan da ta kikkira shi ba a baya, har ta yanke bai d'aga ba sam bata ji komai ba don dama duk in ta kira bai d'auka sai daga baya ya biyo kiran, tun tana saka ran zai kira har ta fara fiddawa ta shiga sak'a ko bai son yin magana da ita ne ko kuma k'ilan wani uzurin yake k'arshe kuma ta yanke k'ilan ma yayi bacci ne, rufe idanunta tayi da niyyar yin bacci bayan ta gama Addu'a bata dad'e da rufe idanun ba wayarta ta fara ringing har saida gaban ta ya fad'i da sauri ta bud'e idanun, k'ura ma screen d'in ido tay bayan ta d'aukko wayar tana kallon sunan Sameer daya bayyana kaman bazata d'auka ba can dai a d'arare tay picking ta kai wayar kunnanta, shiru tayi shima kuma bai tanka ba can murya k'asa k'asa tace mashi ina wuni taji ya amsa da "lafiya" d'an murmushi ta saki jin voice d'in shi, tambayarta yay mi take bata yi bacci ba cikin daidaita natsuwa ta bashi amsa da ai ta kwanta baccin ne dai bai zo ba, bai ce komai ba suka d'an yi shiru can ya sake tambayar tana ina ne ta bashi amsa da tana gidan Sister d'inta tazo weekend k'asa k'asa taji ya furta Ok,

"Kai ma kayi baccin ne?" da k'yar ta tambaya harda d'an cize baki, amsa ya bata da eh acikin baccin ne suke magana nan take ta gane Magana ya gaya mata ta saki yar dariya da har saida yaji sautin ta tace "ai ina nufin ko kayi bacci ne na tashe ka,

"No, ina wurin Dad ena" d'an waro ido tay bata ce komai ba suka k'ara yin shiru, "akwae wani abu?" bayan d'an wani lokaci taji ya tambaya da sauri tace "a'a, dama na kira in gaida ka ne",

"Sai kin ga dama kike wannan kenan" ba zato taji yace haka ta d'an waro ido a ranta tace kaji shi ma ba sai ya ga dama yake kirana ba a fili kuma sai tace "a'a, ba haka bane, ina son in rink'a kiran to kuma ban san ko kana cikin aiki ba kada in takura maka,

"You can call whenever you want, in ina free zamu yi magana" bayan ya d'an yi shiru taji ya fad'i hakan wani irin dad'i taji tana murmushi tace mashi to,

"Yaushe zaki gama School?" d'an jimm tay alamar tunani kafin tace "nan da Kusan 7 Months masu zuwa" shiru ya d'an yi sai kuma taji yace Kusan ko kuma ya kai da sauri tace eh zasu yi good 7 Months kafin su gama ya furta Ok, shiru suka k'ara yi Fauzy sai faman sakin k'ayataccen murmushi take don wani irin dad'i take ji da suna wayar duk da ba wata Magana suke ba, bayan wani lokaci taji yace mata ta kwanta yadda zata tashi da wuri tace ai gobe ba School ya furta Ok ya manta,

"Yaushe zaka koma UK wurin aikin ka?" kawai sai ji tayi ta furta hakan da bud'ar bakin shi sai ce mata yay ya akai tasan a can yake aiki, waro ido tay ta bud'e baki don sai lokacin ta ankare da tayi 6aram6arama da ta fad'i hakan yanzu ya zata ce mashi yadda akai ta sanin tunda bai yuwuwa tace a wurin Haisam, tana haka taji yace yana jiran ta bashi amsa ta shiga yan kame kame can zuciyarta ta tuna mata da hoton shi data gani a Dp tare da turawa kuma akwae rubutu a k'asan dp d'in duk da bazata iya tuna mi aka rubuta ba, cikin yar rawar murya tace "d..dama a profile d'in ka ne naga hakan" tana yin Maganar gabanta ya hau fad'uwa gudun kada ace ba hakan a profile d'in, cikin ikon Allah kuwa a business profile d'in shi akwae bayani akan Company d'in nasu hakan yasa ya furta "Ok" wani sanyi taji a ranta ta d'an yi farfar da idanu alamar ta sha, ce mata yay zai koma soon,
"Allah ya kaimu ya kai ka lafiya" slowly ya furta "Ameen", shiru suka d'an k'ara yi taji yace yana son yin bacci ya gaji ya za'ai da sauri tace "to, gud night" shima hakan ya furta mata ta ciro wayar ta kashe kiran, mirginawa tay ta koma kallon sama tana ta murmushi sosae abun ke bata mamaki wai ace wannan mutumin data gani a d'akin Ya Haisam taita kallon shi har ya Harare ta ne wannan kuma ma wai aure zasu yi, jinjina kai ta hau yi still da murmushi akan fuskar ta a fili ta furta "ikon Allah kenan!" komawa tay tunanin to wai bai iya soyayya bane ko mi ace wai a haka soyayya suke tayi ma tunanin zai mata Maganar neman Auren nata amman bai ce komai game da hakan ba, wata zuciyar ce ta raya mata k'ilan kuma izzar ce ta sa haka kaman yadda Aunty tace ko kuma bai sake mata ne suyi soyayyar don kada ta raina shi, yar dariya tay ta raya in hakane kuma zai aureta, tunanin to su matan da akace yana ta6awa ba soyayya suke ba can kuma ta raya koda yake ai ance yawanci sune ke lik'e mashi, yin wannan tunanin yasa taji ranta ya 6aci ta d'aure fuska a fili ta furta "zanyi iya bakin kokarina inga na hanaka aikata hakan in sha Allahu" ta kai Maganar tana d'an jinjina kai, wayarta ce tay k'ara ta juya ta kai hannu ta daukko, sak'o ne aka turo mata bayan ta bud'e bin alert d'in tay da kallo na 200k daga Sameer, d'an murmushi tayi ta fita daga wurin tasan ko ta kira ba d'auka zai yi ba hakan yasa ta shiga WhatsApp ta tura mashi sak'on godiya, tunanin ko Aunty Mareeya tayi bacci ta shiga yi sai kuma ta raya bari ta jaraba kiran ta, wayar na fara ringing ta d'auka tare da tambayar Fauzyn miye tace "ashe baki yi bacci ba, dama zan sanar maki ne yanzu muka yi waya da Sameer" tana rufe baki tace "da gaske...,ya kira kenan?" Shiru Fauzy ta d'an yi kafin tace mata a'a itace ta kira ta gaishe shi,

"Ya yi kyau hakan kin kyauta dama bai kamata ki biye ma halin shi ba ta hakane zaki rink'a jawo shi jiki har ya sake maki kuma ki cire duk wani tunanin wai ko zai aure ki ne don ya taimaka maki da sauran su in bai son ki ba yadda za'ai ya aure ki tunda aure fa ba abun wasa bane da zai tsallake tarin yan mata ya za6e ki don taimako ba gama misali nan akan Zarah ba haka mukai ta nuna mata mijin nata na son ta shiyasa ya amince ya aure ta kuma sai gashi hakan ne" jinjina kai Fauzy tay tace to,

"ya yi maki Maganar zuwa neman Auren naki ne" da sauri tace "a'a wllh bai ce man komai ba game da hakan kawai waya mukai nace na kira in gaishe shi ne shine har yace wai sai naga dama nike hakan nace ai don kada in rink'a takura mashi ne shine yace zan iya kiran shi duk in ina so in dai yana free zamu yi magana",

Aunty ta furta da kyau ko wannan ma ai alama ce ta yana son ta, cigaba Fauzy tay tace mata ya tambayi lokacin da zata gama Makaranta ma, a d'okance Aunty tace "ina jin Saboda ranar da za'a saka maku ne ya tambayi wannan to",

da sauri Fauzy tace mata eh itama tayi tunanin hakan don dama data kira bai d'auka ba sai daga baya shine yace mata yana wurin Dad d'in shi ne, "Ma sha Allah abu dai nata tabbata" Aunty ta fad'a tana washe baki, fad'i mata zancen kud'in daya turo yanzu tayi Auntyn tace "wato shi soyayyar bada kud'i ya iya bata kalamai ba kenan, hakan yayi kyau yayi ta turo su muna mashi godiya don yanzu ba zamu rink'a mamaki ba tunda mun fahimci kud'in ne har sun mashi yawa" Fauzy na dariya ta furta "kai Aunty...",
Chapter 92 · 0% Book details