Sashe 201
Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Amman Adda Fatuu ban yi ƙarama ba da yin aure" Aysha ta faɗa da yar damuwa, Fatuu dake tsaye a gaban wardrobe ɗin bango tana ƙoƙarin za6o mata kaya ta bata amsa da "ba wata ƙarama da kikai Aysha, ke ai gara kema akan Mino, ita fa ko gama Secondary bata yi ba akayi mata aure gashi ko a jiki ma kin ɗan fita kauri lokacin" ta ƙarasa Maganar tana dawowa wurin gadon hannunta ruƙe da riga da skirt na lace kalar blue da ratsin golden brown, ita ta taimaka ma Ayshar ta shirya cikin kayan ta saka mata yan kunnan zinari da zobe sai kuma agogo golden mai kyau, yar light make up tayi mata ta ɗaura mata kallabi sai gashi ta fito tayi wani irin kyau, bayan an gama saka kayan ta yafa gyale mahadinsu haka jaka da takalmanta suma duk kalar kwalliyar lace ɗinne takalman masu dan tudu ne kadan don tana da tsawo don bata cika saka takalma masu tsini ba, lokacin da suka fito falon Na'eem din har ya gama shiryawa ya dawo suna zaune da Haisam, shima shadda ce ya saka brown wadda ta hau da kwalliyar lace ɗin jikin Ayshar sai baza ƙamshi yake, Na'eem na ganin shigarta yana murmushi yace ko daga yanayin shigar su hakan ya tabbatar da sun dace da juna duk akayi yar dariya Aysha ta sunnar da kai, har bakin galleliyar baƙar Motar Haisam da suka zo da ita suka rako su bayan sun shiga sukai masu sai sun dawo, yana driving suna hira irin ta masoya haka suka shiga zaga gidajen yan'uwan su Na'eem wanda duk mawadata ne, duk inda suka je sai ya gabatar da ita matsayin matar shi ta biyu da zai aura nan bada jimawa ba anata yabata tare da fatan alkhairi, lokacin da suka je gidan Kakarshi wadda ta haifi Mom ɗinshi shima haɗaɗɗan gidane mai girma don yana da parts da yan'uwan mahaifiyarshi maza ke zaune da matansu haka itama kakar 6angarenta daban an ƙawata shi ai kace ba sashen tsohuwa ba, lokacin daya gabatar mata da Aysha matsayin wadda zai ƙara mata cike da zolaya irinta Kaka ta yamutsa fuska tace in baya ga rigima irinta namiji mi zai ci da wannan yar ƙaramar bafullatanar bayan yana da mata ƙaƙƙarfa kamar ita, ita dai Aysha murmushi kawai take kanta a ƙasa haka shima Na'eem ɗin yar dariya yake yace ina wani ƙarfi a tare da ita, sosae ta sake ma Aysha tana ta mata tambayoyi game da ita tana bata amsa da yake tasan Haisam sosae ta yaba da al'amarin tayi Addu'ar Allah ya sanya alkhairi, duk sauran parts ɗin gidan saida ya kai ta ko ina an yi mata tarba mai kyau, daga baya bangaren Kakar suka koma sai bayan sallar La'asar ya dawo daga Masallaci yace mata zasu tafi tace ma Aysha tunda a garin take zaune ta rinƙa zuwa gaishe da ita tana kama ƙafa in tana son ta amince ta aurar mata miji in ba haka ba ita dashi saidai kallo, tana murmushi tace mata in sha Allahu zata riƙa zuwa sukai mata sallama cike da tsokana Na'eem yace tunda ita mai ƙarfi ce sai ta taso ta raka su bakin mota ko, wurga mashi harara tayi tace Allah ya kyauta tayi ma kishiyarta rakiya duk sukai dariya, bayan sun baro gidan Shopping ya wuce da ita, koda yace mata ta ɗauki duk abunda take so cikin marairaicewa tace mashi ai ita tana da komai yana mata wani kallo yace duk da haka ta ƙara so yake daga yau ta fara amfani da kayan mijinta, ba yadda ta iya haka ta fara ɗaukar yan abubuwa tana sakawa a cart da ya ɗaukko mata, ganin bata ɗaukar kayan sosae yasa shi fara za6ar mata da kanshi yana yi yana tambayar wanda take amfani dasu, bayan sun gama da wurin kayan shafa wurin dogayen riguna suka nufa tana ta roƙon ya barsu tana da su da yawa amman duk da haka saida ya daukar mata guda biyar da takalma guda ukku bayan sun gama da nan bangaren undies suka nufa duk yadda take jin kunya saida ya sakata ta ɗauka, abunda bata sani ba yana amfani da hakan ne wurin sanin size ɗinta saboda in zai yi mata lefe, saida ya cika Shopping cart ɗin taff da kaya sannan suka nufi wurin biya aka saka masu kayan a ledoji bayan an saka a Mota suka tafi.
Kamar yadda Na'eem yace wani ƙarshen satin na zagayowa suka shirya zuwa Yola da Haisam, ranar asabar da safe suka bi jirgi zuwa Yola bayan sun isa aka tura Mota ta ɗauke su zuwa garin su Fatuu, bayan sun isa sun samu kyakkyawar tarba daga mutan gidan aka sauke su a part ɗin su Yadikko nan aka shiga zuwa gaishe da su kan kace mi an jere masu kwanonin abinci iri iri koda Yadikko tayi masu Maganar cin abinci cewa sukai a ƙoshe suke Baffa dake zaune yana murmushi yace duk da haka yakamata su ci tunda tafiya suka yo, ba wani mai yawa suka ci ba saidai sun sha fura ba laifi, bayan sun gama ne Haisam ya gabatar masu da Na'eem matsayin shine mai son auren Aysha in ta gama School, dama an riga an sanar masu game da zuwansu, sosae suka nuna farinciki da Addu'ar Allah ya sanya alkhairi bayan sun amsa Haisam ya sake cewa yana son a faɗi mashi lokacin da zasu turo a saka rana Baffa na murmushi cikin Maganar shi mai tattare da natsuwa yace ai tunda ga shi Haisam ɗin shima matsayin Mahaifi yake wurin Aysha don haka a nemi aurenta a wurinshi duk yadda ya yanke yayi lafiya lou tunda ba abu bane na kusa kada aita wahalar yin zarya, hakan ba ƙaramin daɗi yayi ma Na'eem ba shima Haisam yaji daɗin yadda ya girmamashi yay mashi godiya da Addu'ar Allah ya ƙara girma da lafiya yana murmushi ya amsa shima yay mashi godiyar abubuwan alkhairi da ake ta masu da Addu'ar Allah ya ƙara girma da arzuki duk suka amsa da Amin, shiru falon ya ɗan yi kafin Baffan yace masu bari ya kai su bangaren shi sai su huta Haisam yace ai ba daɗewa zasu yi ba zasu koma Yola anjima zasu koma Abuja Baffan yace amman zasu kai azahar ko yana son bayan an gama sallar azahar lokacin duk yan uwanshi sun haɗu sai su gaisa dasu yace to, bangarenshi ya tafi dasu don su hutan kafin ayi sallar, bayan gama yin sallar azahar a ƙopar gida a fadar dake a cikin soro inda arɗo ke zama kafin ya rasu wadda yanzu Baffa ne ke zama don shine arɗon suka shiga harda sauran yan'uwan nashi, bayan sun gaggaisa Baffa ya gabatar masu da Na'eem, duk sun nuna farinciki kan al'amarin tare da Addu'ar Allah ya sanya alkhairi, da fulatanci Baffa yay masu bayanin lokacin da Aysha zata gama Makaranta yake son ayi auren ya kuma bada izinin a nemi auren a wurin shi mijin inna wuro kada zaryar tayi yawa, gaba ɗaya dai sun nuna hakan yayi Baban altine harda cewa ai Haisam ɗin yanzu shima na gida ne kuma ga abun alkhairi da yake ta kawo masu, bayan sun gama gaisuwar kuɗi masu yawa Na'eem ya aje masu yace suyi amfani nan fa suka shiga yin godiya Haisam ma ya ƙara aje masu wasu bandir bandir ɗin zo kaga godiya da addu'o'i, bayan sun fito bangaren su Baffa suka koma yasa Yadikko ta kaisu su gaisa dasu Yaya, cikin faram faram Yaya ta tarbesu akayi masu shimfiɗa suka zauna Yadikko taje tayo ma su Mairo Magana duk suka zo nan ɗakin aka shiga gaisawa dasu da tambayar Haisam yadda su Fatuu suke fuska a sake yake amsa masu daga baya ya gabatar masu da Na'eem, duk sun nuna farincikin su suma sunyi Addu'ar Allah ya sanya alkhairi ya kuma nuna masu, nan ma saida suka aje masu kuɗi masu yawa kafin su taso, basu daɗe ba bayan sun koma falon Yadikko sukai masu sallama suma saida suka aje masu kuɗi Baffa yace don Allah su bar shi kada hidiman tayi yawa wanda suka bada sun isa Yadikko tace mashi ko can wurin su Yaya ma saida suka bada masu yawa, duk yadda sukai dasu kan su barshi basu ɗauka ba dole sukai masu godiya, har bakin mota duk aka rakosu su suka yi bankwana dasu kafin suka tafi, a kan hanya ne Na'eem ke yabon Baffan su Fatuu yace ya burge shi wllh sosae kai kace ba mutumin ruga ba yana da natsuwa da wayewa in ba don haka ba bazai sake masu ba matsayin su na surukai Haisam yay murmushi yace haka yake ya fita daban a cikin su. Gab da sallar Magrib suka dawo Abuja sosae Na'eem yayi ma Haisam godiya da zasu rabu, saboda tafiyar da su Haisam ɗin sukai yasa wannan Weekend ɗin Fatuu ce tazo Abuja, da daddare bayan sun kwanta ne Haisam ke ce mata mi zai hana Baffansu ya baro ƙauye ya dawo ko Katsina tunda gasu Gwaggo sai ya siya mashi gida su zauna, itama Fatuu ta nuna tana son hakan tace zata tuntu6eshi kan hakan, Washe gari da safe ta kira Baffan bayan sun gaisa ne take mashi Maganar, farko shiru yayi kafin yace mata zai so hakan saidai barin ruga yanzu ba abu bane mai yuwuwa a wurinshi don arɗo ya bar mashi amanar gidan yace kada ya bari kan iyalin ya tarwatse yanzu in yace ya tafi yasan za'a iya samun 6araka kuma shi kan shi yafi sabawa da nan tunda anan ya taso yace taba Haisam haƙuri kuma tayi mashi godiya kan kudirin nashi tace to, koda ta sanar ma Haisam ɗin ya fahimci Baffan ya nuna mata bakomai, da yamma ta shirya komawa Zaria ta jirgi Esha ta saka rigimar sai ta bita Fanan ta shiga rarrashinta tace ta bari in akayi hutun School sai suje mata hutu kamar yadda suke yi sannan ta haƙura suka yi mata rakiya gaba ɗayansu harda Haisam Airport tabi charter flight zuwa Kaduna daga can driver zai wuce da ita Zaria.
Kamar yadda Na'eem yace wani ƙarshen satin na zagayowa suka shirya zuwa Yola da Haisam, ranar asabar da safe suka bi jirgi zuwa Yola bayan sun isa aka tura Mota ta ɗauke su zuwa garin su Fatuu, bayan sun isa sun samu kyakkyawar tarba daga mutan gidan aka sauke su a part ɗin su Yadikko nan aka shiga zuwa gaishe da su kan kace mi an jere masu kwanonin abinci iri iri koda Yadikko tayi masu Maganar cin abinci cewa sukai a ƙoshe suke Baffa dake zaune yana murmushi yace duk da haka yakamata su ci tunda tafiya suka yo, ba wani mai yawa suka ci ba saidai sun sha fura ba laifi, bayan sun gama ne Haisam ya gabatar masu da Na'eem matsayin shine mai son auren Aysha in ta gama School, dama an riga an sanar masu game da zuwansu, sosae suka nuna farinciki da Addu'ar Allah ya sanya alkhairi bayan sun amsa Haisam ya sake cewa yana son a faɗi mashi lokacin da zasu turo a saka rana Baffa na murmushi cikin Maganar shi mai tattare da natsuwa yace ai tunda ga shi Haisam ɗin shima matsayin Mahaifi yake wurin Aysha don haka a nemi aurenta a wurinshi duk yadda ya yanke yayi lafiya lou tunda ba abu bane na kusa kada aita wahalar yin zarya, hakan ba ƙaramin daɗi yayi ma Na'eem ba shima Haisam yaji daɗin yadda ya girmamashi yay mashi godiya da Addu'ar Allah ya ƙara girma da lafiya yana murmushi ya amsa shima yay mashi godiyar abubuwan alkhairi da ake ta masu da Addu'ar Allah ya ƙara girma da arzuki duk suka amsa da Amin, shiru falon ya ɗan yi kafin Baffan yace masu bari ya kai su bangaren shi sai su huta Haisam yace ai ba daɗewa zasu yi ba zasu koma Yola anjima zasu koma Abuja Baffan yace amman zasu kai azahar ko yana son bayan an gama sallar azahar lokacin duk yan uwanshi sun haɗu sai su gaisa dasu yace to, bangarenshi ya tafi dasu don su hutan kafin ayi sallar, bayan gama yin sallar azahar a ƙopar gida a fadar dake a cikin soro inda arɗo ke zama kafin ya rasu wadda yanzu Baffa ne ke zama don shine arɗon suka shiga harda sauran yan'uwan nashi, bayan sun gaggaisa Baffa ya gabatar masu da Na'eem, duk sun nuna farinciki kan al'amarin tare da Addu'ar Allah ya sanya alkhairi, da fulatanci Baffa yay masu bayanin lokacin da Aysha zata gama Makaranta yake son ayi auren ya kuma bada izinin a nemi auren a wurin shi mijin inna wuro kada zaryar tayi yawa, gaba ɗaya dai sun nuna hakan yayi Baban altine harda cewa ai Haisam ɗin yanzu shima na gida ne kuma ga abun alkhairi da yake ta kawo masu, bayan sun gama gaisuwar kuɗi masu yawa Na'eem ya aje masu yace suyi amfani nan fa suka shiga yin godiya Haisam ma ya ƙara aje masu wasu bandir bandir ɗin zo kaga godiya da addu'o'i, bayan sun fito bangaren su Baffa suka koma yasa Yadikko ta kaisu su gaisa dasu Yaya, cikin faram faram Yaya ta tarbesu akayi masu shimfiɗa suka zauna Yadikko taje tayo ma su Mairo Magana duk suka zo nan ɗakin aka shiga gaisawa dasu da tambayar Haisam yadda su Fatuu suke fuska a sake yake amsa masu daga baya ya gabatar masu da Na'eem, duk sun nuna farincikin su suma sunyi Addu'ar Allah ya sanya alkhairi ya kuma nuna masu, nan ma saida suka aje masu kuɗi masu yawa kafin su taso, basu daɗe ba bayan sun koma falon Yadikko sukai masu sallama suma saida suka aje masu kuɗi Baffa yace don Allah su bar shi kada hidiman tayi yawa wanda suka bada sun isa Yadikko tace mashi ko can wurin su Yaya ma saida suka bada masu yawa, duk yadda sukai dasu kan su barshi basu ɗauka ba dole sukai masu godiya, har bakin mota duk aka rakosu su suka yi bankwana dasu kafin suka tafi, a kan hanya ne Na'eem ke yabon Baffan su Fatuu yace ya burge shi wllh sosae kai kace ba mutumin ruga ba yana da natsuwa da wayewa in ba don haka ba bazai sake masu ba matsayin su na surukai Haisam yay murmushi yace haka yake ya fita daban a cikin su. Gab da sallar Magrib suka dawo Abuja sosae Na'eem yayi ma Haisam godiya da zasu rabu, saboda tafiyar da su Haisam ɗin sukai yasa wannan Weekend ɗin Fatuu ce tazo Abuja, da daddare bayan sun kwanta ne Haisam ke ce mata mi zai hana Baffansu ya baro ƙauye ya dawo ko Katsina tunda gasu Gwaggo sai ya siya mashi gida su zauna, itama Fatuu ta nuna tana son hakan tace zata tuntu6eshi kan hakan, Washe gari da safe ta kira Baffan bayan sun gaisa ne take mashi Maganar, farko shiru yayi kafin yace mata zai so hakan saidai barin ruga yanzu ba abu bane mai yuwuwa a wurinshi don arɗo ya bar mashi amanar gidan yace kada ya bari kan iyalin ya tarwatse yanzu in yace ya tafi yasan za'a iya samun 6araka kuma shi kan shi yafi sabawa da nan tunda anan ya taso yace taba Haisam haƙuri kuma tayi mashi godiya kan kudirin nashi tace to, koda ta sanar ma Haisam ɗin ya fahimci Baffan ya nuna mata bakomai, da yamma ta shirya komawa Zaria ta jirgi Esha ta saka rigimar sai ta bita Fanan ta shiga rarrashinta tace ta bari in akayi hutun School sai suje mata hutu kamar yadda suke yi sannan ta haƙura suka yi mata rakiya gaba ɗayansu harda Haisam Airport tabi charter flight zuwa Kaduna daga can driver zai wuce da ita Zaria.