Sashe 51
Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Bayan fitowar su ganin Laila yasa Mom tambayar ya akai ta taho Hajiya ta fad'i masu yadda sukai da gwaggon Dad yace amman dai Laila din yakamata ta kwana Hajiyar tace mashi su je kawae ko gwaggon ta koma gidan ba bacci zata iya yi ba yar lelen ta na kwance a gadon Asibiti, yar dariya Dad yay yace ai ba ita kad'ai ce yau bazata iya yin baccin ba tana da d'an uwa yay Maganar idon shi akan Haisam duk akayi dariya, sallama su Najeeb da Na'eem sukai masu don wucewa zasu yi duk akayi masu godiya da Addu'ar Allah ya bar zumunci sukai ma Haisam Allah ya bata lafiya shima yayi masu godiya bayan sun shige Motocin su Senator yace ma Haisam suje shida Abbas su samo masu Abinci don tana iya tashi da yunwa yace Ok, a tare duk suka shiga cikin Motoci suka tafi.
Lokacin da suka isa gidan tuni wanda suke cikin gidan sunyi nisa a baccin su, a gaban Entry Hall duk suka parker Motocin aka firfito, bayan sun shiga main parlor anan sukai ma juna sai da Safe Senator ya nufi part d'in shi haka ma Mom da Hajiya da Laila, Fauzy tare da Mino suka nufi hanyar baya har sun d'an yi nisa Nameer dake tsaye yana jiran su Mom d'in shi su shige ya kira sunan ta, juyowa tay yayi mata alamar ta zo ta juyo ta nufo shi, daga gaban shi ta tsaya suka sakar ma juna murmushi yace "Hankali ya kwanta ko Adda d'inki bata mutu ba" dariya tayi tasa hannu ta rufe fuska kafin ta cire, wani irin kallon love yake mata sai murmushi take a hankali ya furta "in muka yi aure I don't want you to get pregnant da wuri sai mun gama shan love sosae tukun" da sauri ta kai hannu ta rufe fuskarta ta juyar da fuskar wata irin kunya ce ta kama ta, ce mata yay miye abun wani kunya tunda auren zasu yi kuma ma bai son a d'auki time don ya yanke zai sanar da Hajiya sai ayi magana da parents d'in ta kafin su tafi, jin haka yasa ta juyo a sanyaye ta kalle shi, ya lura da canjin fuskar tata hakan yasa yace koda wani abu ba sun gama magana ba kuma ta amince zata aure shi, da d'an yanayin damuwa tace mashi eh kawai tana tsoron kar a k'i amince mashi ya aure ta, wani kalar murmushi yay yace "to akan mi za'a k'i amince man tunda ni nace ina so kuma in hakane shima Big bro ai da an k'i amince mashi" shiru yay ya d'age gira ya sake cewa "We are meant for each other shiyasa muna had'uwa muka fad'a son Junan mu so Don't Worry babe you will soon be Mrs Nameer Ali Zakee" k'ayataccen murmushi Mino tayi tace "Promise me bazaka dawo ka canza ra'ayi ba" wani kalan lumshe mata ido yay ya furta "I promise u My yar fillo" dariya Mino tayi shima yar dariya yay yace mata yana bala'en son yaji tana magana shiru tay tana ta murmushi bashi kad'ai ba ko a school haka ake cewa ba kamar in tana yin karatu, d'an juyawa tay ta hango Fauzy tsaye tana jiranta tace mashi bari taje ana jiranta, lumshe ido yay yace Ok amman tayi mashi abunda zai ta tunawa yay bacci mai dad'i, had'e lips d'inta tay tana murmushi a hankali tace "like what" rolling eyes d'in shi yay k'asa k'asa yace "blow me a kiss" sai da ta waiga taga Fauzy bata kallon su sannan ta d'aga hannu ta hura mashi kiss d'in ya bud'e hannu kafin ya rungume su ya wani lumshe ido dariya Mino tay ta juya da gudu ta bar wurin ya bita da kallo yana dariya, yana d'aya daga abunda ke k'ara burge shi da ita ta cika kunya, daina gudun tay data kusa zuwa wurin Fauzy, bayan taje inda take tsaye hak'uri ta bata tace ta sa tana ta jira Fauzyn ta d'an yi murmushi idonta a kanta tace "tsuntsayen love na lura dai ba k'aramar soyayya kuke sha ba da zafi zafi" rufe fuska Mino tay tana dariya suka tafi, bayan sun fito bayan sun tunkari part d'in Fauzy na murmushi tace inama su Aunty Mareeya basu yi bacci ba su ji abun farinciki Mino tace wllh itama tayi farinciki Fauzy tace sai fatan Allah ya inganta ya raba su lafiya wayaga su Zarah an haihu tayi Maganar had'i da sa dariya Mino ma yar dariyar take Lokacin suka iso part d'in suka shige.
Bayan tafiyar su Hajiya wurin gadon da Fatuu take kwance gwaggo taje ta tsaya tana kallonta Fuskar ta d'auke da Murmushi, har bata san ina zata kai farinciki ba rayuwarta ta kasance fin yadda take mata mafarki, sai murmushi take tana haka fuskar Mahaifiyar Fatun ta rink'a dawo mata, girgiza kai ta shiga yi a ranta ta furta Allah kenan ya d'auke wata ya bata wata, a fili ta shiga yi ma mahaifiyar Fatuu Addu'a itama ta rok'a mata lafiya da kuma inganta abunda take d'auke da shi, juyawa tayi ta nufi kopar dake cikin d'akin wanda tasan toilet ne, Alwala ta dauro ta dawo cikin d'akin tunanin abunda zata shimfid'a tayi sallar tayi k'arshe ta yanke ta shimfid'a kallabinta kawai, bayan ta gama sallar Nafilar sosae tayi ma Fatuu Addu'a bayan ta shafa zama tayi taci gaba da tasbihi, tana haka aka k'wank'wasa kopar ta gyara zamanta tace a shigo, Abbas ne ya shigo da sallama hannuwan shi ruk'e da katan d'in ruwa da lemu bayan shi Haisam ne ruk'e da k'atuwar leda, sannu da zuwa gwaggo tayi masu suka amsa acan gaban gefen gadon suka aje kayan kafin suka juya suna gaishe da gwaggon da fara'a ta amsa tayi masu sannu, mik'ewa tayi ta d'auki kallabin tana ruk'e da shi ta nufi hanyar k'opa ta fita, tsaye sukai suna kallon fuskar Fatun gaba d'ayan su fuskokin su d'auke da Murmushi, wata irin sabuwar k'aunarta Haisam ke ji na ratsa zuciyar shi,
"Allah kenan gwanin hikima masanin sirrin 6oye, wato a duk lokacin da na kalli Mom Zarah sai na tuno farkon gani na da ita a kopar gidan Hajiya ranar an aiketa ta d'ebo ruwa" Abbas ne yay Maganar idon shi akan Fatuu, Murmushi ne akan fuskar Haisam don bai mance da ranar ba, Abbas yaci gaba "lokacin har ta tambaye ka bak'o kayi na bata amsa da ba bak'o bane d'an uwan ka ne nace mata Mom d'in mu d'aya aikuwa ta buga k'afa tace ita bata yarda ba yo ya zata ga wake da shinkafa kuma in ce gidan mu d'aya, duk na tuna Maganar nan sai nayi dariya, lokacin dana fad'i mata inada mata da yaro ne tayi man magana k'asa k'asa wai kai to ya kai bakai auren ba, ina niyyar bata amsa ka d'ago kayi mata magana gashi tana tsoron ka hakan yasa ta tafi, k'ilan dana fad'i mata da sa rana akan ka da bata kamu da son ka ba" murmushi Haisam kawai yake yana tuna komai a lokacin,
"Mom Zarah an yi kuruciya mai saka nishad'i ina rok'on Allah ya baku D'iya mai irin halinta sai kuyi ta tunawa da tata kuruciyar" yar dariya Haisam d'in yayi, Abbas ne yace mashi suje ko gwaggo ta komo ciki yace Ok ya sake cewa gashi ma ya gan tana salla asaman kallabi yakamata ace akwae prayer mat Haisam d'in yace zai zo da wuri sai ya taho dashi, matsawa yay wurin gadon ya sunkuya ya manna ma Fatuu kiss a saman goshinta Abbas nata sakin murmushi, gwaggo na zaune ta d'age kanta suka fito, sauke kan tayi ganin su yasa ta mik'e sukai mata saida safe ta koma ciki.
Misalin k'arfe biyu da yan mintuna Fatuu ta fara motsi, a hankali ta fara bud'e idanunta har ta ware su gaba d'aya, k'ura ma saman d'akin ido tay tana kikkafta idanu, hannu ta d'ago ta ta6a mask d'in hancin ta nan take ta gane inda take, cire mask d'in tayi ta juya kanta idanunta suka sauka akan gwaggo dake kishingid'e akan kujera idanunta a rufe, bin ta da kallo Fatuu tay fuskarta da d'an murmushi, motsi gwaggon ta fara yi dama tana cikin yin tasbih baccin ya kwashe ta, kokarin gyara kwanciya ta fara cikin disasshiyar murya Fatuu ta ambaci sunanta, bud'e ido gwaggon tayi suka had'a ido, da sauri ta tashi zaune kafin ta mik'e ta nufi gadon, zama tay bakin gadon suna kallon juna da murmushi tace mata ta tashi ta d'aga mata kai, sannu tayi mata nan ma kai ta d'aga mata suka d'an yi shiru,
Lokacin da suka isa gidan tuni wanda suke cikin gidan sunyi nisa a baccin su, a gaban Entry Hall duk suka parker Motocin aka firfito, bayan sun shiga main parlor anan sukai ma juna sai da Safe Senator ya nufi part d'in shi haka ma Mom da Hajiya da Laila, Fauzy tare da Mino suka nufi hanyar baya har sun d'an yi nisa Nameer dake tsaye yana jiran su Mom d'in shi su shige ya kira sunan ta, juyowa tay yayi mata alamar ta zo ta juyo ta nufo shi, daga gaban shi ta tsaya suka sakar ma juna murmushi yace "Hankali ya kwanta ko Adda d'inki bata mutu ba" dariya tayi tasa hannu ta rufe fuska kafin ta cire, wani irin kallon love yake mata sai murmushi take a hankali ya furta "in muka yi aure I don't want you to get pregnant da wuri sai mun gama shan love sosae tukun" da sauri ta kai hannu ta rufe fuskarta ta juyar da fuskar wata irin kunya ce ta kama ta, ce mata yay miye abun wani kunya tunda auren zasu yi kuma ma bai son a d'auki time don ya yanke zai sanar da Hajiya sai ayi magana da parents d'in ta kafin su tafi, jin haka yasa ta juyo a sanyaye ta kalle shi, ya lura da canjin fuskar tata hakan yasa yace koda wani abu ba sun gama magana ba kuma ta amince zata aure shi, da d'an yanayin damuwa tace mashi eh kawai tana tsoron kar a k'i amince mashi ya aure ta, wani kalar murmushi yay yace "to akan mi za'a k'i amince man tunda ni nace ina so kuma in hakane shima Big bro ai da an k'i amince mashi" shiru yay ya d'age gira ya sake cewa "We are meant for each other shiyasa muna had'uwa muka fad'a son Junan mu so Don't Worry babe you will soon be Mrs Nameer Ali Zakee" k'ayataccen murmushi Mino tayi tace "Promise me bazaka dawo ka canza ra'ayi ba" wani kalan lumshe mata ido yay ya furta "I promise u My yar fillo" dariya Mino tayi shima yar dariya yay yace mata yana bala'en son yaji tana magana shiru tay tana ta murmushi bashi kad'ai ba ko a school haka ake cewa ba kamar in tana yin karatu, d'an juyawa tay ta hango Fauzy tsaye tana jiranta tace mashi bari taje ana jiranta, lumshe ido yay yace Ok amman tayi mashi abunda zai ta tunawa yay bacci mai dad'i, had'e lips d'inta tay tana murmushi a hankali tace "like what" rolling eyes d'in shi yay k'asa k'asa yace "blow me a kiss" sai da ta waiga taga Fauzy bata kallon su sannan ta d'aga hannu ta hura mashi kiss d'in ya bud'e hannu kafin ya rungume su ya wani lumshe ido dariya Mino tay ta juya da gudu ta bar wurin ya bita da kallo yana dariya, yana d'aya daga abunda ke k'ara burge shi da ita ta cika kunya, daina gudun tay data kusa zuwa wurin Fauzy, bayan taje inda take tsaye hak'uri ta bata tace ta sa tana ta jira Fauzyn ta d'an yi murmushi idonta a kanta tace "tsuntsayen love na lura dai ba k'aramar soyayya kuke sha ba da zafi zafi" rufe fuska Mino tay tana dariya suka tafi, bayan sun fito bayan sun tunkari part d'in Fauzy na murmushi tace inama su Aunty Mareeya basu yi bacci ba su ji abun farinciki Mino tace wllh itama tayi farinciki Fauzy tace sai fatan Allah ya inganta ya raba su lafiya wayaga su Zarah an haihu tayi Maganar had'i da sa dariya Mino ma yar dariyar take Lokacin suka iso part d'in suka shige.
Bayan tafiyar su Hajiya wurin gadon da Fatuu take kwance gwaggo taje ta tsaya tana kallonta Fuskar ta d'auke da Murmushi, har bata san ina zata kai farinciki ba rayuwarta ta kasance fin yadda take mata mafarki, sai murmushi take tana haka fuskar Mahaifiyar Fatun ta rink'a dawo mata, girgiza kai ta shiga yi a ranta ta furta Allah kenan ya d'auke wata ya bata wata, a fili ta shiga yi ma mahaifiyar Fatuu Addu'a itama ta rok'a mata lafiya da kuma inganta abunda take d'auke da shi, juyawa tayi ta nufi kopar dake cikin d'akin wanda tasan toilet ne, Alwala ta dauro ta dawo cikin d'akin tunanin abunda zata shimfid'a tayi sallar tayi k'arshe ta yanke ta shimfid'a kallabinta kawai, bayan ta gama sallar Nafilar sosae tayi ma Fatuu Addu'a bayan ta shafa zama tayi taci gaba da tasbihi, tana haka aka k'wank'wasa kopar ta gyara zamanta tace a shigo, Abbas ne ya shigo da sallama hannuwan shi ruk'e da katan d'in ruwa da lemu bayan shi Haisam ne ruk'e da k'atuwar leda, sannu da zuwa gwaggo tayi masu suka amsa acan gaban gefen gadon suka aje kayan kafin suka juya suna gaishe da gwaggon da fara'a ta amsa tayi masu sannu, mik'ewa tayi ta d'auki kallabin tana ruk'e da shi ta nufi hanyar k'opa ta fita, tsaye sukai suna kallon fuskar Fatun gaba d'ayan su fuskokin su d'auke da Murmushi, wata irin sabuwar k'aunarta Haisam ke ji na ratsa zuciyar shi,
"Allah kenan gwanin hikima masanin sirrin 6oye, wato a duk lokacin da na kalli Mom Zarah sai na tuno farkon gani na da ita a kopar gidan Hajiya ranar an aiketa ta d'ebo ruwa" Abbas ne yay Maganar idon shi akan Fatuu, Murmushi ne akan fuskar Haisam don bai mance da ranar ba, Abbas yaci gaba "lokacin har ta tambaye ka bak'o kayi na bata amsa da ba bak'o bane d'an uwan ka ne nace mata Mom d'in mu d'aya aikuwa ta buga k'afa tace ita bata yarda ba yo ya zata ga wake da shinkafa kuma in ce gidan mu d'aya, duk na tuna Maganar nan sai nayi dariya, lokacin dana fad'i mata inada mata da yaro ne tayi man magana k'asa k'asa wai kai to ya kai bakai auren ba, ina niyyar bata amsa ka d'ago kayi mata magana gashi tana tsoron ka hakan yasa ta tafi, k'ilan dana fad'i mata da sa rana akan ka da bata kamu da son ka ba" murmushi Haisam kawai yake yana tuna komai a lokacin,
"Mom Zarah an yi kuruciya mai saka nishad'i ina rok'on Allah ya baku D'iya mai irin halinta sai kuyi ta tunawa da tata kuruciyar" yar dariya Haisam d'in yayi, Abbas ne yace mashi suje ko gwaggo ta komo ciki yace Ok ya sake cewa gashi ma ya gan tana salla asaman kallabi yakamata ace akwae prayer mat Haisam d'in yace zai zo da wuri sai ya taho dashi, matsawa yay wurin gadon ya sunkuya ya manna ma Fatuu kiss a saman goshinta Abbas nata sakin murmushi, gwaggo na zaune ta d'age kanta suka fito, sauke kan tayi ganin su yasa ta mik'e sukai mata saida safe ta koma ciki.
Misalin k'arfe biyu da yan mintuna Fatuu ta fara motsi, a hankali ta fara bud'e idanunta har ta ware su gaba d'aya, k'ura ma saman d'akin ido tay tana kikkafta idanu, hannu ta d'ago ta ta6a mask d'in hancin ta nan take ta gane inda take, cire mask d'in tayi ta juya kanta idanunta suka sauka akan gwaggo dake kishingid'e akan kujera idanunta a rufe, bin ta da kallo Fatuu tay fuskarta da d'an murmushi, motsi gwaggon ta fara yi dama tana cikin yin tasbih baccin ya kwashe ta, kokarin gyara kwanciya ta fara cikin disasshiyar murya Fatuu ta ambaci sunanta, bud'e ido gwaggon tayi suka had'a ido, da sauri ta tashi zaune kafin ta mik'e ta nufi gadon, zama tay bakin gadon suna kallon juna da murmushi tace mata ta tashi ta d'aga mata kai, sannu tayi mata nan ma kai ta d'aga mata suka d'an yi shiru,