Sashe 62
Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Bayan su Nameer sun tafi Senator yay ma Alhaji Ibrahim Maganar bada kud'in neman Aure, daga cikin Aljihun jallabiyar shi ya ciro kud'in bandir d'in yan dubu guda biyu wato 200k ya ba Alhaji Ibrahim d'in, mik'ewa yay ya nufi su Ard'o da sauri Baban Altine ya mik'e shima ya tare shi ya bashi kud'in, bayan duk sun koma sun zauna aka yi Addu'oi aka shafa. Bayan tafiyar su Senator Baffan Altine ya bud'e ledar daya basu nan suka ga shaddoji ne guda shidda wato kowa kala biyu, sam bakunan su sun kasa rufuwa tsabar farinciki sai yabon kirkin su Senator suke, mik'ewa sukai don suje su k'arasa shiryawa kowanne su bakin shi a washe, tsayawa Baffan Fatuu yay bayan sun tafi ya fara k'ok'arin kiran Yadikko, lokacin da kiran ya shiga tana cikin d'aki suna shiryawa Kusan ma sun gama kimtsawa, bayan ta d'auka cikin ladabi ta gaishe dashi ya amsa, tambayarta yay sun gama shiryawa tace mashi eh, d'an shiru yay kafin kuma yace Albishirinta tana Jin hakan da sauri ta bashi amsa da goro fari Kal, yadda tay Maganar har saida ta d'an bashi dariya yace mata wani abun Alkhairin ne ya same su yanzun nan, cike da k'aguwa ta tambayi miye, fad'i mata zancen neman Auren Mino dasu Senator suka zo yanzu yay harda shaddoji daya basu da kuma kud'in neman Auren, tun kafin ya gama fad'i mata ta mik'e tsaye don da a zaune take a bakin gado, gaba d'aya mamaki ne ya kamata ta kai hannu ta rufe baki shi kuma sai murmushi yake don ya fahimci taji Al'ajabin Maganar, muryarta na rawa tace "Yanzun Mino itama yaron gidan nan zata aura, to yaushe suka san juna haka mu bamu da Labari" fad'i mata yay a wurin bikin nan kuma an kira shi a gaban su ya tabbatar yana son ta zai aureta, wani irin farinciki ne ya lullube yadikko wanda tunda take bata ta6a jin irin shi ba a rayuwar ta gaba d'aya ta kasa rufe baki su Aysha da suka zuba mata ido ganin yadda take farinciki yasa suma suka shiga washe bakin haka innar su Altine ma dake zaune a cikin d'akin idon ta na akan ta, bayan sun gama wayar da sauri ta tambayeta ya akai taga tana ta farinciki ne nan take sanar mata, itama tsananin mamaki ne ya kamata ta waro ido can kuma sai ta mik'e zumbur ta nufa hanyar fita, d'akin su Yaya ta nufa duk sun shirya suma suna zaune a bakin gado suna had'a jakunkunan kayan su ta fad'o kamar an jefo ta duk suka d'ago kai suka kallo ta, Yaya ce ta d'an 6ata fuska tace lafiya zata fad'o masu haka ba sallama, hak'uri ta basu tay tsaye tanata zare ido ta ma rasa ta ina zata fara, ganin yanayin ta yasa Yaya tambayar ta lafiya, ai kaman tana jira ta hau fad'i masu zancen an nemi auran Mino itama zata auri yaron gidan nan, wani kallon mamaki gaba d'ayan su suka bita dashi Yaya ta maimaita Maganar cikin d'aurewar kai Babar su Altine tace wllh yanzun nan mahaifin su ya kira innar su yana fad'i mata, hannu Yaya ta kai ta ruk'e ha6a tana jinjina kai ita kuwa kishiyar tata murmushi ta shiga yi tana fad'in "kaga ikon Allah, ashe da rabon zamu k'ara zuwa gidan nan shan wani bikin, lallai iyalin Muhammadu masu jinin sa'a ne....." A dak'ile Yaya ta katseta da fad'in "Uhmm wai jinin sa'a, ai ni gaba d'aya sai yanzun ma na fahimci komai, wannan sa'ar ba ta Allah da Annabi bace, wato da suka ga ita ta farkon ta samu mai Arziki shine itama wannan sukai kulle kullen su suka tura ta binni, kai da ganin wannan kasan aikin asiri ne ace yana ganin ta ya fara sonta har an tsaida magana, ita kadae ce yarinya a wurin bikin ba ga yan mata nan yan binni ba, ke ita kanta babbar ma ni yanzu ban yadda hakanan mijin nata ya aure ta ba tun farko k'ulla soyayyar ta su akai shiyasa ta tashi hankalin ta da taji Ard'o ya bayar da ita, gaba d'aya sai yanzu na gano komai, ita ce ta kitsa ma Yarinyar ta gudu ta koma bayan tayi shiri sosae kan shi mai kud'in da shi Alhaji Lawan d'in shine ta zo har tayi nasarar sa shi janye Maganar aka kawo ta wanccan" Fuska a hautsine take Maganar cikin harshen fulatanci duk sun zuba mata ido, mik'ewa tay ta cize baki idon ta a kan su rai 6ace tace "gaba d'aya sai yanzu na gane komai daya faru mak'ark'ashiya akai, shima Ard'o harda shi aka ma Asiri shiyasa ya yarda aka fasa da wanccan ya kafe kan sai anyi da wanda ta Auran" jinjina kai innar su Altine ta hau yi fuskarta a yamutse gaba d'aya wata irin hassada ce ta mamaye mata zuciya, kai da kawowa Yaya ta shiga yi ta k'ank'ance idanunta ta shiga zurfin tunani,
"in dai ina raye to bazan bari Yaron ya auri Mino ba, tunda abun hakane nima zan yi abunda suka yin in sa a maida Auran kan d'aya daga cikin jikokina tunda ai ba fina iyawa su kai ba, ba abunda nike bari ya sha man kai, itama uwar Muhammadun da ta nemi zame man matsala ai ba k'aramar uk'ubata tasha ba kafin Allah ya d'auke abun sa, suma jikokin nata ban ta6a zaton haka abun zai kasance ba da tun wuri na d'auki mataki a kan su amman duk da haka lokaci ai bai k'ure man ba ko ya k'ure ba abunda zai gagara, har ita ta farkon sun ja bazan k'yaleta ba sai na raba Auran nata nasa ta dawo ruga anan zatai Aure......
86
...........bata samu k'arasa Maganar tata ba sakamakon buga katifa da d'ayar Matar Ardon mai suna Mero dake a zaune tayi fuska a matuk'ar d'aure ta fara magana "Sam bazan bari ki aikata hakan a gare su ba matuk'ar ina numfashi, duk abubuwan da kike yi mana k'yale ki kawae nike ba wai don ina tsoron ki bane, to yanzu an zo ga6ar da bazan zuba maki ido ba wllh sai in da k'arfi na ya k'are" gaba d'aya Al'ajabi ne ya kama su ganin yadda take maida mata martani ba tare da nuna shakkar ta ba kamar yadda suke yi tana juya su, hannu Yaya ta kai ta nuna kanta tace ita take gaya ma magana haka ta manta wacece ita,
"Ban manta ba, ke Mutum ce kamar ni saidai muna da bambanci sosae, ke mushirika ce wadda bata yarda da Allah ba ni kuma na Yarda da Allah ban yarda da shirka ba, don haka a wannan karon na d'aura d'amarar yin yak'i da shirka za kuma muga wanda zai yi nasara tsakanin k'arya da gaskiya, hakanan Saboda tsabar mugunta da rashin tsoron Mahallici mi Mutanen nan sukai maki da kika d'au karan tsana kika d'aura masu, in don mahaifiyar shi da take kishiyar ki ai ta bar maki duniyar ko, in kuma don kina ganin Ardo yafi ji dashi ne ai don yafi sauran yaran nashi gaskiya ne da ruk'on Amana, wato don kina aikata shirka shine kike ganin ita kowa ma ke yi, to tsaya kiji sirrin, matuk'ar mutum zai tawakalli ya dogara ga Allah ya mik'a mashi dukkan lamuransa to zai ta samun cigaba a rayuwar shi wannan dalilin ne yasa kika ga a komai Muhammadu da iyalan sa suke nasara koda kuwa kin aikata masu wani abu ina mai tabbatar maki bazaki yi nasara ba da iznin ubangiji, Idan kuwa ya baki sa'a don wani lokacin yana tara bawa ne kafin ya d'au mataki akan shi in har kika aikata wani abu da yay sanadiyyar fasa yin auren nan to sai na tona maki Asiri kowa yasan ke kika aikata masu wani abu kuma kinsan Mutanan binni bazasu ta6a kyale ki ba kotu za'a kai ki daga can sai gidan yari kuma na tabbatar d'aurin rai za'a maki don sai na fad'a cewa kina da sa hannu wurin mutuwar Innar Muhammadun k'ilan ma harda matar shi innar su inna wuro, a yanzu zan zuba maki ido ne amman zan sanar da Muhammadu da matarsa harda su yaran da Kakar su akan su dage da Addu'a dama dai kinsan ai su ba daga baya ba wurin ruk'o da Addini to har nima zan taya su zamu ga tsakanin mu da ke wanda zai yi nasara" rai a tsananin 6ace tana huci ta k'arasa Maganar dama can tara Yayar take, sototo sukai suna bin ta da ido,
"in dai ina raye to bazan bari Yaron ya auri Mino ba, tunda abun hakane nima zan yi abunda suka yin in sa a maida Auran kan d'aya daga cikin jikokina tunda ai ba fina iyawa su kai ba, ba abunda nike bari ya sha man kai, itama uwar Muhammadun da ta nemi zame man matsala ai ba k'aramar uk'ubata tasha ba kafin Allah ya d'auke abun sa, suma jikokin nata ban ta6a zaton haka abun zai kasance ba da tun wuri na d'auki mataki a kan su amman duk da haka lokaci ai bai k'ure man ba ko ya k'ure ba abunda zai gagara, har ita ta farkon sun ja bazan k'yaleta ba sai na raba Auran nata nasa ta dawo ruga anan zatai Aure......
86
...........bata samu k'arasa Maganar tata ba sakamakon buga katifa da d'ayar Matar Ardon mai suna Mero dake a zaune tayi fuska a matuk'ar d'aure ta fara magana "Sam bazan bari ki aikata hakan a gare su ba matuk'ar ina numfashi, duk abubuwan da kike yi mana k'yale ki kawae nike ba wai don ina tsoron ki bane, to yanzu an zo ga6ar da bazan zuba maki ido ba wllh sai in da k'arfi na ya k'are" gaba d'aya Al'ajabi ne ya kama su ganin yadda take maida mata martani ba tare da nuna shakkar ta ba kamar yadda suke yi tana juya su, hannu Yaya ta kai ta nuna kanta tace ita take gaya ma magana haka ta manta wacece ita,
"Ban manta ba, ke Mutum ce kamar ni saidai muna da bambanci sosae, ke mushirika ce wadda bata yarda da Allah ba ni kuma na Yarda da Allah ban yarda da shirka ba, don haka a wannan karon na d'aura d'amarar yin yak'i da shirka za kuma muga wanda zai yi nasara tsakanin k'arya da gaskiya, hakanan Saboda tsabar mugunta da rashin tsoron Mahallici mi Mutanen nan sukai maki da kika d'au karan tsana kika d'aura masu, in don mahaifiyar shi da take kishiyar ki ai ta bar maki duniyar ko, in kuma don kina ganin Ardo yafi ji dashi ne ai don yafi sauran yaran nashi gaskiya ne da ruk'on Amana, wato don kina aikata shirka shine kike ganin ita kowa ma ke yi, to tsaya kiji sirrin, matuk'ar mutum zai tawakalli ya dogara ga Allah ya mik'a mashi dukkan lamuransa to zai ta samun cigaba a rayuwar shi wannan dalilin ne yasa kika ga a komai Muhammadu da iyalan sa suke nasara koda kuwa kin aikata masu wani abu ina mai tabbatar maki bazaki yi nasara ba da iznin ubangiji, Idan kuwa ya baki sa'a don wani lokacin yana tara bawa ne kafin ya d'au mataki akan shi in har kika aikata wani abu da yay sanadiyyar fasa yin auren nan to sai na tona maki Asiri kowa yasan ke kika aikata masu wani abu kuma kinsan Mutanan binni bazasu ta6a kyale ki ba kotu za'a kai ki daga can sai gidan yari kuma na tabbatar d'aurin rai za'a maki don sai na fad'a cewa kina da sa hannu wurin mutuwar Innar Muhammadun k'ilan ma harda matar shi innar su inna wuro, a yanzu zan zuba maki ido ne amman zan sanar da Muhammadu da matarsa harda su yaran da Kakar su akan su dage da Addu'a dama dai kinsan ai su ba daga baya ba wurin ruk'o da Addini to har nima zan taya su zamu ga tsakanin mu da ke wanda zai yi nasara" rai a tsananin 6ace tana huci ta k'arasa Maganar dama can tara Yayar take, sototo sukai suna bin ta da ido,