Sashe 199
Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 6 min read
"In kin ganshi yayi maki zaki amince?" shiru tayi tana ta kikkafta idanu, ɗage mata gira yay yace ita yake sauraro a sanyaye ta ɗaga mashi kai alamar eh, bin ta yay da wani irin kallo ta ƙara maida kanta tana wasa da yatsunta, tana haka taji muryarshi yace "Aysha ni ne na ganki naji ina son ki kuma auren ki nike son yi in kin gama School amman sai in nayi maki nima" da sauri ta ɗago ta kalleshi idanunta a ware fuskarta ta nuna tsananin mamakin Maganar shi yana murmushi ya ɗan lumshe mata ido, ƙirjinta ne ya fara bugu da sauri da sauri ta maida idonta ƙasa,
"Sunana Na'eem, ni abokin Yayinki Haisam ne, inada mata da yara biyu sannan ina aiki da Central Bank, ban san ko na ta6a ganinki ba kafin yanzu tunda muna yawan kasancewa da Haisam duk wata hidima data danganci Family ɗin su ina zuwa saidai a wurina yau na fara ganinki zuwan mu nan, kuma cikin ikon Allah ina ganinki naji na kamu da son ki abunda bature ke cewa, Love at first sight, nayi ma shi yayan naki magana kan haka shine yace to in nemi soyayyar ki idan Allah yasa kinga nayi maki to zan aure ki da kin gama School sannan zan barki kici gaba da Karatun ki in sha Allahu" shiru bata ce komai ba bata kuma ɗago ba abun ya ɗaure mata kai sosae don bata yi tunanin zai mata wannan Maganar ba, ganin taƙi tace komai yasa shi kiran sunanta ta amsa ba tare data ɗago ba yace tayi shiru bata ce komai ba still taƙi cewa komai ɗin,
"Ayshat" amsa mashi tayi ba tare data ɗago ba yace "Look at me" saida tay ɗan jimm kafin a hankali ta ɗago idanunta suka sauka akan kyakkyawar doguwar fuskarshi mai ɗauke da kwantaccen saje, yanayin fatarshi ba za'a ce mashi fari ba kuma ba baƙi bane yafi kama da a kira shi da wankan tarwaɗa, sosae yanayin hutu ya bayyana a jikin fatar ta shi yana da kyawun fuska wadda take a cike ɗauke da dogon hanci da kuma madaidaicin baki mai dauke da jerarrun fararen haƙora harda yar wushirya, a bangaren yanayin jiki sam ba gajere bane don da kaɗan Haisam ya ɗara shi tsawo sannan kuma ba siriri bane yana da cikar jiki, ganin tanata kallonshi yasa shi ce mata kada taji komai in taji bata son shi ta faɗi mashi bazai ji komai ba kuma ko Yayanta bazai faɗi ma yadda sukai da ita ba, motsa baki ta fara da ƙyar tace mashi shikenan idan Yaya Haisam ya amince to ta yarda, ɗan girgiza mata kai yayi yace mata aure ba abu bane da wani zai amince maka tunda bashine zai zauna maka ba sannan aure ana yin shi in ana son juna don haka ita zata amince mashi in taji tana son shi, shiru tayi tana yi tana maida idonta ƙasa ya ɗan ɗage mata gira yana murmushi, sai faman yan kame kame take don taji itama yayi mata don Na'eem ba irin mazan da suke furta ma mace so taƙi amincewa bane kawai dai abun ne taji yayi mata girma ba kamar da yake wannan ne karo na farko da tayi Magana irin haka da Namiji,
"Amman...ita Matarka to zata amince ka aure ni ne?" da ƙyar ta furta mashi hakan, gyara zama yay kafin yace "Ayshat ba kowace mace bace ke son a ƙara mata abokiyar zama ba saidai inada kyakkyawar fahimta da mata na nasan zata amince koda hakan bai mata dadi ba amman tasan inada ikon ƙara wata matar kuma dama ban ta6a mata alƙawarin zan kasance da ita kaɗai ba don haka nasan bazata bani matsala ba in kin amince zaki aure ni" kai ta ɗaga mashi kafin tace shikenan,
"Kin amince zaki aure ni kenan?" kai ta ƙara ɗaga mashi ya sake cewa "ina fata dai ba saboda wani dalili ko don ni abokin yayanki bane yasa kika amince man, nafi son ki amince man don kema kinji kina sona" kai ta jinjina mashi yana mata wani kallo yace "nayi maki kina so na?" kan dai ta sake ɗaga mashi,
"Ok in dai da gaske kike kema kamata yay ki faɗi man da bakinki kamar yadda na faɗa maki" ɗan murmushi ta shiga yi tana motsa baki ya ɗage mata gira alamar ta bashi amsa, da kyar ta furta "nima ina son...ka" tana yin Maganar da sauri tasa duka hannuwanta masu ɗauke da dogayen yatsu ta rufe fuskarta Na'eem ɗin ya shiga yin yar dariya, da yake wayayye ne sai gashi yasa ta saki dashi sun shiga yin firar soyayya, suna haka Hajiya Fatuu ta shigo cikin falon tana sanye da riga da skirt na lace da suka amshi jikinta tare da gyale mahadinsu, tana nan yadda take bata ƙara ƙiba ba saidai ta ƙara cikowa tay dumdum fatar nan tata har wani sheki take hutu ya zauna mata sosae, ƙafafunta na sanye da wasu takalma masu tsini mai ɗan gwa6i har yanzu halinta nason takalma masu tudu nan, ta bangaren hips dinta kuwa abun saidai ace tubarkalla don suna nan sai ma ƙara cika da sukai duk da gyalen jikinta babba ne amman kana kallonta zaka san tana dasu, hannunta na hagu na rataye da yar babbar jaka da take ɗauke da kayan karatunta sai kuma ɗayan hannunta na hagu ta ruƙo Lab coat dashi, tana ganin Na'eem ta fara yin murmushi hakan ya bayyanar sa fararen haƙoranta kamar auduga masu ɗauke da haƙorin makka daya ƙara ƙawata fuskar tata, cikin falon ta nufa sam bata yi mamakin ganin Na'eem ɗin ba don da sukayi waya da Haisam ya sanar mata tare suka zo, a saman kujera dake gefen wadda suke ta zauna Na'eem daya maido idonshi kanta yana murmushi shima yay mata sannu da dawowa ta amsa tare da gaishe dashi da yi mashi anzo lafiya, bayan ya amsa ya tambayi karatunta tace mashi Alhamdulillah itama ta tambayi matar shi Fadeela da yaransu duk yace mata lafiya lou suke, saida suka gama gaisawa sannan Aysha tayi mata sannu da zuwa ta maida idonta kanta tana murmushi ta amsa ta tambayi ya School tace mata lafiya lou, yar hira sukai da Na'eem kafin ta miƙe tace bari ta ɗan shiga ciki yace Ok. Sai bayan sallar Magrib sun dawo daga masallaci suka zauna cin abinci gaba ɗayan su Na'eem da Aysha sai satar kallon juna suke suna murmushi, bayan sun dawo daga sallar isha gaba daya a falo suka zauna suna kallo, wuraren ƙarfe tara Haisam ya miƙe yace ma Na'eem bacci yake ji ya taso suje ya kai shi ɗakin da zai kwanta yana murmushi yace shi da Aysha basu gama yin kallon ba yace Ok yazo suje ya nuna mashi in ya gama sai yaje ya kwanta ya miƙe, bayan tafiyar su ne Fatuu ma ta miƙe tayi ma Ayshar saida safe dama duk in Haisam yazo a ɗayan bedroom ɗin dake part ɗin Fatuu take kwana tare da mai aikin su Asabe, bada jimawa ba Na'eem ya dawo a saman kujera mai mazaunin mutum ukku ya zauna yace ma Aysha ta dawo nan, a can gefe kamar ɗazu ta zauna ya jingina kanshi da jikin kujerar ya shiga sakar mata kallon love da alama dai shima gwani ne ta bangaren soyayya, hirar soyayyarsu suka shiga yi ba laifi ta saki jiki sun ɗan ɗauki lokaci wurin ƙarfe goma saura yace bari ya barta taje tayi bacci kadda ya gajiyar da amaryarshi tayi dariya suka miƙe a tare.
"Sunana Na'eem, ni abokin Yayinki Haisam ne, inada mata da yara biyu sannan ina aiki da Central Bank, ban san ko na ta6a ganinki ba kafin yanzu tunda muna yawan kasancewa da Haisam duk wata hidima data danganci Family ɗin su ina zuwa saidai a wurina yau na fara ganinki zuwan mu nan, kuma cikin ikon Allah ina ganinki naji na kamu da son ki abunda bature ke cewa, Love at first sight, nayi ma shi yayan naki magana kan haka shine yace to in nemi soyayyar ki idan Allah yasa kinga nayi maki to zan aure ki da kin gama School sannan zan barki kici gaba da Karatun ki in sha Allahu" shiru bata ce komai ba bata kuma ɗago ba abun ya ɗaure mata kai sosae don bata yi tunanin zai mata wannan Maganar ba, ganin taƙi tace komai yasa shi kiran sunanta ta amsa ba tare data ɗago ba yace tayi shiru bata ce komai ba still taƙi cewa komai ɗin,
"Ayshat" amsa mashi tayi ba tare data ɗago ba yace "Look at me" saida tay ɗan jimm kafin a hankali ta ɗago idanunta suka sauka akan kyakkyawar doguwar fuskarshi mai ɗauke da kwantaccen saje, yanayin fatarshi ba za'a ce mashi fari ba kuma ba baƙi bane yafi kama da a kira shi da wankan tarwaɗa, sosae yanayin hutu ya bayyana a jikin fatar ta shi yana da kyawun fuska wadda take a cike ɗauke da dogon hanci da kuma madaidaicin baki mai dauke da jerarrun fararen haƙora harda yar wushirya, a bangaren yanayin jiki sam ba gajere bane don da kaɗan Haisam ya ɗara shi tsawo sannan kuma ba siriri bane yana da cikar jiki, ganin tanata kallonshi yasa shi ce mata kada taji komai in taji bata son shi ta faɗi mashi bazai ji komai ba kuma ko Yayanta bazai faɗi ma yadda sukai da ita ba, motsa baki ta fara da ƙyar tace mashi shikenan idan Yaya Haisam ya amince to ta yarda, ɗan girgiza mata kai yayi yace mata aure ba abu bane da wani zai amince maka tunda bashine zai zauna maka ba sannan aure ana yin shi in ana son juna don haka ita zata amince mashi in taji tana son shi, shiru tayi tana yi tana maida idonta ƙasa ya ɗan ɗage mata gira yana murmushi, sai faman yan kame kame take don taji itama yayi mata don Na'eem ba irin mazan da suke furta ma mace so taƙi amincewa bane kawai dai abun ne taji yayi mata girma ba kamar da yake wannan ne karo na farko da tayi Magana irin haka da Namiji,
"Amman...ita Matarka to zata amince ka aure ni ne?" da ƙyar ta furta mashi hakan, gyara zama yay kafin yace "Ayshat ba kowace mace bace ke son a ƙara mata abokiyar zama ba saidai inada kyakkyawar fahimta da mata na nasan zata amince koda hakan bai mata dadi ba amman tasan inada ikon ƙara wata matar kuma dama ban ta6a mata alƙawarin zan kasance da ita kaɗai ba don haka nasan bazata bani matsala ba in kin amince zaki aure ni" kai ta ɗaga mashi kafin tace shikenan,
"Kin amince zaki aure ni kenan?" kai ta ƙara ɗaga mashi ya sake cewa "ina fata dai ba saboda wani dalili ko don ni abokin yayanki bane yasa kika amince man, nafi son ki amince man don kema kinji kina sona" kai ta jinjina mashi yana mata wani kallo yace "nayi maki kina so na?" kan dai ta sake ɗaga mashi,
"Ok in dai da gaske kike kema kamata yay ki faɗi man da bakinki kamar yadda na faɗa maki" ɗan murmushi ta shiga yi tana motsa baki ya ɗage mata gira alamar ta bashi amsa, da kyar ta furta "nima ina son...ka" tana yin Maganar da sauri tasa duka hannuwanta masu ɗauke da dogayen yatsu ta rufe fuskarta Na'eem ɗin ya shiga yin yar dariya, da yake wayayye ne sai gashi yasa ta saki dashi sun shiga yin firar soyayya, suna haka Hajiya Fatuu ta shigo cikin falon tana sanye da riga da skirt na lace da suka amshi jikinta tare da gyale mahadinsu, tana nan yadda take bata ƙara ƙiba ba saidai ta ƙara cikowa tay dumdum fatar nan tata har wani sheki take hutu ya zauna mata sosae, ƙafafunta na sanye da wasu takalma masu tsini mai ɗan gwa6i har yanzu halinta nason takalma masu tudu nan, ta bangaren hips dinta kuwa abun saidai ace tubarkalla don suna nan sai ma ƙara cika da sukai duk da gyalen jikinta babba ne amman kana kallonta zaka san tana dasu, hannunta na hagu na rataye da yar babbar jaka da take ɗauke da kayan karatunta sai kuma ɗayan hannunta na hagu ta ruƙo Lab coat dashi, tana ganin Na'eem ta fara yin murmushi hakan ya bayyanar sa fararen haƙoranta kamar auduga masu ɗauke da haƙorin makka daya ƙara ƙawata fuskar tata, cikin falon ta nufa sam bata yi mamakin ganin Na'eem ɗin ba don da sukayi waya da Haisam ya sanar mata tare suka zo, a saman kujera dake gefen wadda suke ta zauna Na'eem daya maido idonshi kanta yana murmushi shima yay mata sannu da dawowa ta amsa tare da gaishe dashi da yi mashi anzo lafiya, bayan ya amsa ya tambayi karatunta tace mashi Alhamdulillah itama ta tambayi matar shi Fadeela da yaransu duk yace mata lafiya lou suke, saida suka gama gaisawa sannan Aysha tayi mata sannu da zuwa ta maida idonta kanta tana murmushi ta amsa ta tambayi ya School tace mata lafiya lou, yar hira sukai da Na'eem kafin ta miƙe tace bari ta ɗan shiga ciki yace Ok. Sai bayan sallar Magrib sun dawo daga masallaci suka zauna cin abinci gaba ɗayan su Na'eem da Aysha sai satar kallon juna suke suna murmushi, bayan sun dawo daga sallar isha gaba daya a falo suka zauna suna kallo, wuraren ƙarfe tara Haisam ya miƙe yace ma Na'eem bacci yake ji ya taso suje ya kai shi ɗakin da zai kwanta yana murmushi yace shi da Aysha basu gama yin kallon ba yace Ok yazo suje ya nuna mashi in ya gama sai yaje ya kwanta ya miƙe, bayan tafiyar su ne Fatuu ma ta miƙe tayi ma Ayshar saida safe dama duk in Haisam yazo a ɗayan bedroom ɗin dake part ɗin Fatuu take kwana tare da mai aikin su Asabe, bada jimawa ba Na'eem ya dawo a saman kujera mai mazaunin mutum ukku ya zauna yace ma Aysha ta dawo nan, a can gefe kamar ɗazu ta zauna ya jingina kanshi da jikin kujerar ya shiga sakar mata kallon love da alama dai shima gwani ne ta bangaren soyayya, hirar soyayyarsu suka shiga yi ba laifi ta saki jiki sun ɗan ɗauki lokaci wurin ƙarfe goma saura yace bari ya barta taje tayi bacci kadda ya gajiyar da amaryarshi tayi dariya suka miƙe a tare.