← Book details Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 67 OF 211

Sashe 67

Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"To, to da kyau, sannun ku da aiki" kaman daga sama suka ji an fad'i hakan gaba d'aya sai da suka d'an firgita da sauri Fatuu ta janye jikinta daga nashi a tare suka juya don ganin mai Maganar, Hajiya ce ta shigo tana dogara sandar ta jikinta sanye da kaftan ta atamfa tayi d'aurin kallabi irin nasu na manya idanunta sanye cikin glasses, wata irin kunya ce ta rufe Fatuu da sauri ta sunnar da kanta duk da bata san ko taga abunda suke ba don sun ba kopar shigowar baya to amman gaba d'aya tana a jikin shi ya tallabe ta a ranta ta raya da k'yar in bata ga abunda yake matan ba, idon Haisam a kanta har ta k'araso ciki ta tsaya daga gaban su ta d'aure Fuska, murmushi yay ya gaishe da ita ta wurga mashi harara tace "Yanzu miye wannan d'in, kasan halin da yarinyar nan take ciki amman shine bazaka iya hak'uri ka bari tabi dokar likita ba ta samu hutun da take buk'ata saboda tsabar jaraba, anya Haisam!" ta k'arasa Maganar ta d'an 6ata rai, still Murmushi yake ya d'an d'age mata gira yace "Yanzu nayi wani laifi ne" a fusace tace bata sani ba, yar dariya yay yace in dai hutu ne ai gashi tana hutawa ko, kwabe fuska tay ta jinjina kai tace eh tabbas ta gani hutawa take, maida idon ta tay kan Fatuu da tai tsumu tsumu kanta a k'asa ji take kaman ta nutse a wurin, ce mata tay ta tashi ta gama hutun anan don ba barin ta za'ai tayi yadda ya kamata ba, zuru da k'afafun ta tay still bata kalli Hajiyar ba ta mik'e, da sandarta tayi mata nuni da hanya tace su je, har zata tafi sai kuma ta dakata Hajiya ta tambayi ya akai k'asa k'asa tace zata d'auki kayanta ne, tambayar ta tay suna ina da k'yar ta d'an d'ago tay mata nuni da inda trolley d'in ta yake, nufar wurin tay tana dogara sandar, jawo shi ta shiga kokarin yi Haisam dake zaune yay yar dariya ya mik'e, wurin ta yaje yace ta kawo ya taimaka mata fuska a d'aure ta kalle shi tace bata so, hannu ya kai ya amshi akwatin ya fara ja Hajiyar ma ta fara tafiya da sauri Fatuu ta juya ta nufi k'opa sumi sumi,

Sun rigata zuwa bakin part d'in nata cikin d'an d'aga murya tace ma Haisam ya aje akwatin nan kar ya shigar mata d'aki ya kama gaban shi murmushi kawae yake ya shige dama ita Fatuu tuni ta shiga, tsaye tay a parlor yana shigowa suka had'a ido a tare suka saki yar dariya suna haka Hajiyar ta shigo da sauri Fatuu ta juyar da kanta, tambayar ta yay a ina za'a aje akwatin tace bata sani ba ya aje a duk inda ya ga dama tunda dai ya raina ta ai saida tace kar ya shigo amman ya shigo, shiru yay can kuma yace mata to tayi hak'uri don ya rage mata aiki ne kawai ba wani abu ba, kaman bazata tanka mashi ba sai kuma tace to ta gode yaje kar kuma ya sake ta k'ara ganin k'afafun shi a part d'in ta, yana dariya yace ai wannan dole ne ya zata d'aukko mashi mata tace kuma kar yazo ai dole yazo ko don ya duba tafiyarta ko, hararar shi tay tace ko don fitina dai, maida idonta tay kan Fatuu dake kallon gefe tace ta wuce ta shiga cikin daki ta nufi hanyar shiga d'akin ba tare data kalle su ba, hannu Haisam ya kai zai d'auki akwatin yana fad'in bari ya shigar mata da shi aikuwa ta d'aga sandarta zata kwad'a mashi da sauri ya kauce yana dariya yace "Sweetheart yau ni zaki buga" fuska a d'aure tace ai bai fi k'arfin shi ba in dai bai fita ya bata wuri ba Allah zata bubbuga nashi ita, cewa yay Allah ya bata hak'uri bari ya fita ai duk abu mai sauk'i ne, saida safe yay mata a dak'ile tace Allah ya tashe su lafiya ya juya ya tafi, d'an murmushi tay ta girgiza kai bayan ya fita ta kai hannu ta kama trolley d'in ta nufi Bedroom, lokacin data shiga Fatun na zaune a bakin gado suna had'a ido da sauri ta janye nata ta koma kallon k'asa, cikin d'akin ta nufo tazo bangaren da Fatun take zaune ta aje trolley d'in a wurin sauran akwatunan, juyowa tay ta kalleta ta tambayi taci Abinci a hankali tace mata eh bayan Magrib taci, "to yanzu kina jin yunwa" girgiza mata kai tay alamar a'a tace to ta kwanta, idasa hayewa gadon tay ta kwanta tay lamo duk tayi kalar rashin gaskiya, wucewa Hajiya tay ta nufi hanyar fita, jin fitar ta yasa Fatun d'ago kai ta kalli k'opar sai kuma ta saka dariya, wayarta ce ta fara ringing da sauri ta kai hannu ta d'agota taga Haisam ne ke kiran, picking tay tana kara wayar a kunne ta saka mashi dariya shima ita yake yi sai kuma a shagwabe tace mashi yaga abunda take ta gudu kenan yace kar ta damu ai ba wani abu bane kawae Hajiyar ce ta d'auke shi a wani abu, tambayar ta yay mi take yi tace mashi gata nan ansa ta kwanta yadda tay Maganar har saida ta bashi dariya itama ita take ta yi,

"Ina Hajiyan?" Ya tambaya, tace mashi ta fita k'ilan tana parlor ya furta Ok bari ya k'yaleta ta huta kar su k'ara wani laifin, har zai mata saida safe sai kuma ya tambayi akwae abunda take so tace mashi eh cike da kulawa yace Ok minene tace "Kai" maimaita abunda tace d'in ya yi tace "Eh Hubby, kai nike so" tana jin sautin murmushin shi yace mata ai shi ta riga ta same shi, cike da tsokana tace "to baby yace so yake ya kwana a part d'in Dad d'in shi sai kazo ka d'auke shi ko ka d'auke ta" yana dariya yace saidae yazo ya d'auki Maman Baby wanda daidai yake da tada yak'i tsakanin shi da Hajiya, labarin buga mashi sanda da tace zatai ya bata Fatun nata dariya, sai da Safe sukai ma juna cike nuna k'auna da kuma kewar juna,

Bayan su Mom sun dawo tana shiga Bedroom d'inta taga ba Fatuu bata kawo komai a ranta ba tay tunanin ko tana wurin Jidderh, bayan ta rage kayan jikinta a cikin Laundry room ta wuce toilet don yin wanka, tana cikin yin shafa Jidderh ta shigo zata fad'i mata abu nan ta tambayi Fatuu na d'akinta ne tace mata a'a ita rabon ta da ita tun kafin Magrib data shigo nan ta duba ta, bayan ta gama shiryawa cikin kayan bacci ganin har lokacin Fatun bata dawo ba yasa ta nufi k'opa, bayan ta fito daga part d'in nata part d'in Laila ta wuce tana shiga cikin parlon ta iske su zaune ita da Fanan duk suna sanye da k'ananun kaya suna kallo a Tv, maido kallon su sukai kanta jin sallamar ta suka amsa mata da murmushi, k'arasawa tay ciki ta zauna akan kujera Fanan ta gaishe da ita ta amsa Laila tace har sun dawo ta d'aga mata kai, tambayar ta tay Daughter na nan ne da alamun rashin fahimta ta tambayi wace daughter d'in tace mata Sis d'in Fanan d'an jimm tay don bata fahimci wadda take nufi ba, Fanan ce data gane tace mata Zarah take nufi, yar dariya tay tace ai cewa zatay matar big bro Mom d'in tayi d'an murmushi kawae, ce mata tay bata nan ai rabonta ma da nan part d'in tun kafin ayi D'inner, d'an jimm Mom tay duk idanunsu na akanta Laila ta tambayi Lafiya, fad'i mata tay tunda ta dawo bata iske ta a bedroom d'in ta ba kamar yarda ta barta tayi tunanin tana a wurin Jidderh kuma bata nan shine tazo nan, ce mata Laila tay to ba sai ta kirata taji ba Mom d'in tace ai bata da no d'in ta,

"To ko dai Big Bro ya fita da ita bari a kira shi a ji don nima banda no d'in nata amman zan amsa ko don irin haka" jinjina kai Mom tay tace bata tunanin Haisam zai yi haka tunda yasan halin da take ciki, Fanan ce tace bari ta kirata sai aji, bayan ta kira layin Fatun ya shiga ta d'auka tana fara'a suka gaisa tace mata tana ina ne nan ta sanar mata tana d'akin Hajiya tace Ok sukai sallama, fad'i ma Mom inda take tay tace to ta mik'e ta nufi hanyar fita Laila na zolayarta tana fad'in duk hankalinta ya tashi kar ace ta 6atar da Amarya tana murmushi ta fuce,

part d'in Hajiya ta nufa tana shiga parlon ta isketa zaune tana kallo, ciki ta shiga ta zauna kujerar gefen ta tana murmushi ta gaishe da ita itama fuska a sake ta amsa mata, shiru ta d'an yi can tace dama ta dawo ne daga unguwa da suka je bata iske Daughter ba tun d'azu shiru ashe tana nan, d'an ta6e baki Hajiya tay tace "eh tana nan ni naje na taho da ita nan kuma bazata koma ba" da sauri Mom ta kalleta da alamun mamaki ta tambayi Lafiya ba dai wata matsala ta faru ba,
Chapter 67 · 0% Book details