Sashe 194
Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Bayan zuwa da Hajiya Abuja a babban private hospital ɗin likitansu na Germany wanda yana ɗaya daga cikin likitocin da Shugaban ƙasa ya maido nan wanda yana aiki a Asibitin Gwamnati sannan kuma ya buɗe private hospital ya zuba ƙwararrun ma'aikata wanda wasu abokan aikinshi ne a can, bayan anyi mata aune aune aka tabbatar da abunda akace yana damunta a Katsina suke damunta kuma ma da sauƙi sosae nan aka tabbatar da jikinta yana buƙatar hutu sosae wataƙil bata hutawa sosae ko tana yawan yin zurga zurga, ran Hajiya Maryam ne ya 6aci tace ita dama ba son zamanta take a Katsina ba kawai don ta nuna hakan take so tunda basu a kusa da ita dama ai abunda taga dama zatai tayi ba mai hanata ko aikin NGO da take da ƙyar aka samu ta daina, ita dai Hajiya jin abunda likitan yace kawai tayi don tasan ita ba wata zurga zurgar da take yi, a ɗaki na musamman aka kwantar da ita sosae ake bata kulawa hatta zuwa dubata an ware lokacin da za'a rinƙa zuwa don kada a dameta, bayan sati ɗaya sai gashi jikin nata ya fara yin kyau lokacin har massaging jikin ake mata ana kuma bata lafiyayyun abinci da zasu ƙara mata ƙarfi da kuzari, bayan tayi satin su Tk da Gwaggo suka zo dubata harda Amadu gaba ɗaya sunji daɗi ganin yadda ta fara samun sauƙi ba kamar Tk kullum da zullumin ciwon nata yake kwana duk ya damu kwanansu biyu suka koma, bayan sati biyu aka sallameta suka wuce Villa da ita, zo kaga murna Hajiya ta warke kowa sai farinciki yake duk sun haɗu harda su Fatuu, a can Katsina ma sai murnar jin Hajiya ta samu lafiya ake, anan Villa aka cigaba da kula da ita tana shan magunguna, bayan tayi sati biyu ya kama watan ta guda a Abuja lokacin ta warke sosae har ɗan ƙara jiki tayi da haske tace ma President tana son komawa Katsina nan fa ya shiga roƙonta kan ta haƙura da zaman Katsina taci gaba da zama nan amman ta nuna mashi ita tafi son zaman can, koda Hajiya Maryam taji itama zuwa tayi suka haɗu da President ɗin suna roƙonta kan ta zauna nan Hajiya Maryam harda yin ƙwalla tana faɗin su basu son su rasata ne yanzu da basu yi gaggawar ɗaukkota nan ba da Allah kaɗai yasan mi zai faru Hajiyar na murmushi tace abunda Allah ya ƙadarro shi zai faru da lokacinta yayi sai ta tafi kuma a tunaninta su suka sa ta warke ne, Hajiya Maryam ɗin tace eh duk da hakan dai gara ta zauna anan tafi samun kulawa, ƙarshe dai saida suka yi nasarar tursasa mata ta dawo nan amman tace masu dole zata koma tayo sallama da mutane Hajiya Maryam harda cewa in don wannan ne ai sai suje rana ɗaya tayo su dawo tace a'a tana buƙatar lokaci ba wai daga taje zata dawo ba don haka aƙalla zata yi wata guda Hajiya Maryam tasa rigimar gaskiya yayi yawa da ƙyar aka tsaya kan sati biyu shima saida Hajiyar ta kafe kafin ta amince, kafin su tafi ne tace tana son bar masu wasiyya ko ba yanzu ba in ajali ya risketa tana son kada su tada Tk daga gidanta koda zasu yi amfani da gidan to a ware mashi isasshshen wurin da zai zauna ta bashi halak malak sannan su Saude ma a barsu suci gaba da zama har sai in su suka buƙaci tashi ko kuma su in suna buƙatar su tashi to sai su siya ma Sauden gida, gaba ɗaya suka haɗa baki wurin cewa in sha Allahu zasu yi kamar yadda tace Hajiya Maryam tace amman ta daina faɗin wasiyyar nan tana tada masu hankali, Hajiyar tayi yar dariya tace to miye abun tashin hankali abunda ya zama dole da lokacinta yayi kuma su ai yan gata ne tunda sun rayu da ita tsawon lokaci wasu da yawa ma basu san Mahaifiyarsu ba, Hajiya Maryam ɗin tace duk da hakan dai suna roƙon Allah ya yasa su cigaba da rayuwa da ita tsawon lokaci tana murmushi ta amsa da Amin, bayan kwana biyu ta dawo Katsina harda First Lady da Aunty suka rakota, zo kaga murna Hajiyar Sanata ta dawo kar ma su Tk gaba ɗaya bakunansu sun ƙi rufuwa dama Tk kusan yafi kowa shiga damuwar ciwon nata zuciyarshi tay ta raya mashi kodai mutuwa Hajiyar zata yi shi bama damuwar shi makomarshi ba a'a yadda zai rayu babu ita shine yafi tada mashi hankali don ba ƙaramin shaƙuwa yayi da ita ba ko Mahaifiyar shi bai jinta a ranshi kamar yadda yake jin Hajiya, Mutane sai so suke su shigo gidan suga Hajiya amman ba dama don ƙopar gidan dankam take da Security wasu kuma sun zagaye gidan wanda babu wasa a tattare dasu gasu da manyan makamai, su Gwaggo dai sun shiga har sun gaisa da Mom da Aunty sun masu ya maijiki, haka manyan mutane mata da maza da yan siyasa sun zo duk an barsu sun shiga sun gaisa da su Mom tare da yi masu ya mai jiki har Governor da First Lady ɗin Katsina sun zo unguwa fa ta ɗinke ba abunda kake gani sai motoci masu numfashi da jiniya, Washe gari su Mom suka tafi bayan tafiyarsu ne Tk ya faɗi ma Hajiyar mutane yan unguwa nata son su shigo su gaishe ta an hana su, tana jin hakan ta bada iznin duk wanda yazo a barshi ya shigo nan fa yan unguwa sukai ta shigowa dubiya manya da yara da dattawa Hajiya tayi amfani da wannan damar duk wanda yazo gaidata sai tayi mashi bankwana ta nemi yafiya, gaba ɗaya gwuiwar mutane sai tayi sanyi kuma jin Hajiyar zata bar Katsina harda masu yin ƙwalla tun ma ranar tafiyar bata yi ba, kowa ya nuna rashin jin daɗin tafiyar da zata yi tana ta ce masu kada su damu ai ba shikenan an rabu ba indai da sauran rayuwa za'a cigaba da zumunci kuma ga Tukur nan zai cigaba da zama a gidan don haka ba abunda zai fasu tsakaninsu, tunda su Tk da Saude da Husnah suka ji zancen komawar Hajiyar Abuja gaba ɗaya suka shiga damuwa kowa jikin shi yay sanyi, bayan dawowarta da sati ɗaya ne ranar Friday da daddare ta kira Tukur da Saude a cikin Bedroom ɗinta, a kan carpet suka zauna ita kuma tana zaune a bakin gado idanunta sanye a cikin gilashi, sun ɗan ɗauki lokaci shiru tana ta kallonsu su kuma duk sun sunnar da kai yayin da ƙirjinsu ke bugawa tamkar ana masu luguden ta6are can Hajiyar ta nisa kafin a nutse ta fara magana,
"Na buƙaci ganin ku ne don yin maganar da nasan bazaku ta6a jin daɗin ta ba kamar yadda nima ba don daɗin yasa zanyi maku ita ba, da farko dai ina mai matuƙar godiya a gare ku godiya mara iyaka, gaba ɗayan mu bamu da wata dangantaka ta jini face ta kasancewar mu musulmai amman Allah ya haɗamu muka zauna tare tsawon lokaci har muka zama tamkar dangin juna, ina son ku sani, ku mutane ne masu matuƙar muhimmanci a gare ni wanda wasu ma da yawa da nike da alaƙa ta jini dasu basu da irin muhimmancin a wurina, Tukur, kai tamkar ɗan dana haifa kake a wurina duk da kafi kama da jikana amman kallon ɗana na jini nake maka, haka kema Saudatu ina matuƙar jin ki a rai na ba kuma don hidimar da kike man ba sai don ƙaunar ki a gare ni wadda nasan ita tasa kika zauna tsawon lokaci kina hidimta man ba tare da gajiyawa ba kuma daidai da rana ɗaya bazan iya cewa ga lokacin da kika sa6a man ta hanyar yi man rashin biyayya ko makamancin hakan......to, gaba ɗaya dai ba abunda zance sai dai ince maku Nagode, Nagode Allah ubangiji ya saka maku da mafificin Alkhairinsa ya ji6anci al'amuranku, ina kuma roƙon shi da yadda ya haɗa mu a gidan duniyar nan ya haɗa mu a gidan aljanna muci gaba da yin rayuwa tare, nasan bazaku rasa jin zancen komawata Abuja ba duk da bamuyi maganar da ku ba kafin yanzu, nasan dole kuji ba daɗi amman ina mai baku haƙuri dama haka rayuwa ta gada in har aka haɗu to tabbas wata rana sai an rabu koda kuwa ba mutuwa ba, don haka inason ku kwantar da hankalinku dan na tafi ba yana nufin an rabu ba kenan indai da rayuwa dole aci gaba da zumunci, kai Tukur zaka cigaba da zama a gidan nan koda kuwa bayan bani a duniya kana da kaso a cikin sa so nike Hajiyar Sanata taci gaba da wanzuwa ta dalilin ka, haka kema Saudatu zaku cigaba da zama keda mijinki har zuwa lokacin da kuke so ke bazance ki zauna dundundun ba saboda yanayin aikin mijinki a koda yaushe za'a iya canza mashi wuri dama ni na roƙa aka bar man shi tsawon lokaci muna tare ba'a ɗauke shi ba saboda ina jin daɗin zaman shi sai kuma yazo ya aure ki aka ƙara zama ɗaya...., akwae gida da nike son siya maki koda bani ba na faɗa za'a siya maki in kun buƙaci barin nan, A ƙarshe ina mai ƙara godiya a gareku sannan ina roƙon yafiyarku saboda ance zo mu zauna zo mu sa6a indai nayi maku ba daidai ba da sani na ko akasin hakan ina mai roƙon ku da ku yafe man ni dai na yafe ma kowa sannan ina mai roƙon ku da kuci gaba da kyautata ma abokan zaman ku",
"Na buƙaci ganin ku ne don yin maganar da nasan bazaku ta6a jin daɗin ta ba kamar yadda nima ba don daɗin yasa zanyi maku ita ba, da farko dai ina mai matuƙar godiya a gare ku godiya mara iyaka, gaba ɗayan mu bamu da wata dangantaka ta jini face ta kasancewar mu musulmai amman Allah ya haɗamu muka zauna tare tsawon lokaci har muka zama tamkar dangin juna, ina son ku sani, ku mutane ne masu matuƙar muhimmanci a gare ni wanda wasu ma da yawa da nike da alaƙa ta jini dasu basu da irin muhimmancin a wurina, Tukur, kai tamkar ɗan dana haifa kake a wurina duk da kafi kama da jikana amman kallon ɗana na jini nake maka, haka kema Saudatu ina matuƙar jin ki a rai na ba kuma don hidimar da kike man ba sai don ƙaunar ki a gare ni wadda nasan ita tasa kika zauna tsawon lokaci kina hidimta man ba tare da gajiyawa ba kuma daidai da rana ɗaya bazan iya cewa ga lokacin da kika sa6a man ta hanyar yi man rashin biyayya ko makamancin hakan......to, gaba ɗaya dai ba abunda zance sai dai ince maku Nagode, Nagode Allah ubangiji ya saka maku da mafificin Alkhairinsa ya ji6anci al'amuranku, ina kuma roƙon shi da yadda ya haɗa mu a gidan duniyar nan ya haɗa mu a gidan aljanna muci gaba da yin rayuwa tare, nasan bazaku rasa jin zancen komawata Abuja ba duk da bamuyi maganar da ku ba kafin yanzu, nasan dole kuji ba daɗi amman ina mai baku haƙuri dama haka rayuwa ta gada in har aka haɗu to tabbas wata rana sai an rabu koda kuwa ba mutuwa ba, don haka inason ku kwantar da hankalinku dan na tafi ba yana nufin an rabu ba kenan indai da rayuwa dole aci gaba da zumunci, kai Tukur zaka cigaba da zama a gidan nan koda kuwa bayan bani a duniya kana da kaso a cikin sa so nike Hajiyar Sanata taci gaba da wanzuwa ta dalilin ka, haka kema Saudatu zaku cigaba da zama keda mijinki har zuwa lokacin da kuke so ke bazance ki zauna dundundun ba saboda yanayin aikin mijinki a koda yaushe za'a iya canza mashi wuri dama ni na roƙa aka bar man shi tsawon lokaci muna tare ba'a ɗauke shi ba saboda ina jin daɗin zaman shi sai kuma yazo ya aure ki aka ƙara zama ɗaya...., akwae gida da nike son siya maki koda bani ba na faɗa za'a siya maki in kun buƙaci barin nan, A ƙarshe ina mai ƙara godiya a gareku sannan ina roƙon yafiyarku saboda ance zo mu zauna zo mu sa6a indai nayi maku ba daidai ba da sani na ko akasin hakan ina mai roƙon ku da ku yafe man ni dai na yafe ma kowa sannan ina mai roƙon ku da kuci gaba da kyautata ma abokan zaman ku",