← Book details Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 189 OF 211

Sashe 189

Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Inda zaki ɗauki shawarata kija yaron nan a jiki ki gina rayuwar shi sai yafi ma ruƙe maki ɗiyar taki da daraja" shiru Hajiya Maryam ɗin tay saida Hajiya tace bata jita bane sannan ta ɗan ta6e baki tace nawa akai ma haka amman suka butulce da sauri Hajiya tace sai dai dama can in butulun ne amman tana da yaƙinin zuri'ar Dije ba butulu bane Hajiya Maryam ɗin tay shiru bata ce komai ba can Hajiyar ta ƙara cewa "bari in maku da yaren daku yan siyasa kuka fi ganewa, yanzu aji kinja shi a jiki kin ginashi sannan kin ɗauki ɗiyarki kin bashi wane irin farin jini kike tunanin zaki a wurin mutane ta yadda koda nan gaba kin fito takara hakan zai iya saka mutane su za6e ki don ansan baki ƙyamar talaka kuma su naki ne, yanzu kamar yaron nan Sameer yadda ya auri ƙawar ita Fateema akai ta jinjina abun yanzu bashi ba ko mahaifinshi ya fito wata takara mutane da dama sai sun za6e shi dalilin haka, amman kawai misali ne na baki kan amfanin taimakon talaka a wurin ku yan siyasa nafi son komai zaki mashi kiyi mashi don Allah, ɗan jimm tayi kamar bazata tanka ba can ta tambayi Hajiyar mi yake karanta ta ɗan yi shiru alamar tunani kafin ta faɗi mata,

"Yanzu kenan ita Farhar zatayi ta zaman jiranshi har ya gama karatun?" ta tambaya idonta akan Hajiya tace mata to yanzu duka ba saura shekara ukku ba ganin lokacin ne mai wuya ai amman yadda yanzu shekara ta zama kamar wata ai kaman gobe ne zai gama in kuma zasu bashi yana karatun to sai a kawota nan Katsina shi yana karatunshi Hajiya Maryam ɗin ta ɗan ta6e baki bata ce komai ba, tambayarta Hajiya tayi yaushe zata koma tace tana tunanin ko zuwa anjima Hajiyar tace ta bari sai gobe mana tana kallonta tace to dama ba dalilin Farhar yasa ta kirata ba Hajiya tana murmushi tace "Eh, amman ban gaji da ganin yar autar tawa ba" ba shiri Hajia Maryam ɗin tayi murmushi,

"Kina yarinya Haƙuri ne dake sosae ba wanda zai ce in kin girma zaki zama rigimamma" tana murmushin tace mata ita ai bata rigima sai akan abunda take ganin shine daidai Hajiya na dariya tace haka dai tace,

"Yanzu da Farhar zaki tafi ne?" Hajiya ta tambaya tace mata eh saboda su Abraham suna zaune gida su kaɗai Hajiya ta jinjina kai kafin tace yakamata ma su koma gabanta can Abujar tace eh tana shirin yin hakan sai kuma Hajiya ta sake cewa to shi Dr ɗin sai a barshi a Lagos shi kaɗai Hajiya Maryam tace to tunda can yake aiki dole can zai zauna sai su rinƙa zuwa mashi Weekend ko kuma shi yaje Abujar in anyi hutun School ma sai yaran suje mashi hutu,

"To ki bashshi kawai ya ƙara aure mana" wani kallo tay ma Hajiyar sai kuma tayi ɗan murmushi tace ashe bata sonta har haka Hajiyar tayi dariya tace miye abun rashin so daga ta bata shawara yadda zata yi ma Dr adalci tace ai bata mashi rashin adalci tana kamantawa kuma itama ai bata rayu da kishiya ba ko, Hajiyar tace ai ita shine ke tafiya can aikin sojan shi ya barta ba itace ke barin shi ba kamar ita, Hajiya Maryam ɗin tace ai koda take barin shi bai zarta ƙa'ida ba da har zai sashi ƙara wani aure, ruƙe ha6a Hajiya tayi tace oh kowa gudun kishiya ita ko da ba'a yi mata ba General ɗin ne bai ra'ayi ba wai ita ta hanashi ba, Hajiya Maryam dake ɗan murmushi tace ai ba abun daɗi bace ita ko sunanta ma bata son ana faɗa,

"anya Maryam, adai rage zafin kishi tunda ba'asan abunda Allah ya ƙaddaro ba" da sauri tace "in dai ta wannan bangaren ne ba abunda ya ƙaddaro in sha Allah auren zobe mukai da shi" dariya Hajiya tayi tace banda wanda aka ɗaura masu a Masallaci kenan wani suka ƙara ɗaurawa tsakaninsu Hajiya Maryam ɗin na murmushi tace mata eh, haka suka cigaba da yin hira sama sama har baccin ya sake ɗaukar Hajiya Maryam.

Washe gari da safe ta koma tare da Farhar, sosae Dr Mahaifin Farha yay farincikin amincewar da Hajiya Maryam ɗin tayi, bayan dawowarta ne Dr ɗin yasa suka zauna don yin shawara game da Kamal yadda zasu inganta rayuwar shi nan ya bada shawarar su fitar dashi ƙasar waje yayi karatu a can ita kuma Farha sai taci gaba da yin Master's degree ɗinta ta amince da hakan, Hajiya ta kira ta sanar da ita suna son fitar da Kamalun waje tace ta sanar da dangin shi, Gwaggo ta kira ta sanar mawa koda Amadu yaji zancen bai goyi baya ba haka da aka sanar ma Fatuu cewa tayi gaskiya kada a amince a ƙyale shi yaci gaba da karatun shi anan salon nan gaba ayi mashi gorin an ɗauki nauyin karatun shi Gwaggo tace to ai ba roƙonsu akai ba su suka yanke hakan Fatun tace ita dai gaskiya bata goyon bayan hakan tunda ai karatun nan ma lafiya lou zai yi ya kuma samu aiki mai kyau, Gwaggo tace itama in son samu ne tafi son a ƙyale shi tunda ma har ya fara yin nisa saidai kuma bata son Hajiya taga anyi masu ba daidai ba, Amadu yace ai Maganar bata Hajiya bace ita da saƙo aka bata yasan zata fahimce su in aka nuna mata tunda ya riga ya fara anan har ya shiga shekara ta biyu a barshi ya ƙarasa, Gwaggo da kanta taje wurin Hajiyar cikin fahimta tayi mata bayanin da Amadun yayi tace itama saida tayi tunanin hakan to amman tunda saƙo ne aka bata shiyasa ta isar, kamar yadda sukai da Gwaggon haka Hajiya ta sanar ma Hajiya Maryam hakan yasa ta fara tabbatar da su bama su Kwaɗayi bane sanin da wuya ai ma wani tayin karatu a ƙasar waje amman ya maida, Soyayya sosae su Farhar suke sha ita da Kamalu don sun samu yanci daga baya ta fara shirye shiryen fara cigaba da karatunta.

Bayan sabuwar Gwamnati ta fara ayyuka sosae Haisam ya tuntubi Alhaji lawal kan buƙatar ayi ma garin su Fatuu hanya a kuma gyara masu wutar lantarki kasantuwar shine ɗan majalissarsu na tarayya ya bashi tabbacin za'ayi masu, tuni aikin ginin Kamfanin Haisam wanda ƙwararran kuma sanannen Companyn gini anan Abujar keyi ya kankama, a yadda aka tsara zuwa nan da shekara guda za'a gama, tuni Al'umma sun fara sheda cewa sabuwar Gwamnati data hau ta aiki ce don kuwa anfara gudanar da ayyuka gadan gadan a faɗin ƙasa bayan hawan ta mulki ciki harda shirye shiryen da zasu tallafa ma talaka ya dogara da kan shi da yake ba laifi mai girma shugaban ƙasa ya samu abokan tafiya da shawara na ƙwarae masu tausayin talakawa, Kawu Mani har Abuja ya fara zuwa da Gwaggo acan ya samu inda ya kaita aka fara koya mata turanci don ta iya karatu, kan kace mi Gwaggo ta canza ta ƙara murmurewa duk alamun tsofanta daya bayyana yanzu babu sosae farinta ya ƙara fitowa tayi dumurmur abunta dama gata doguwar mace abun dai saidai ace tubarkallah, a bangaren First Lady kuwa wato Mahaifiyar su Haisam abun ba'a magana yanzu jin daɗi ya ninninku ta ƙara wani irin kyau Jama'a kowa yabon kyaunta da kuma kirkinta ake don mace ce mai sauƙin kai wadda kowa nata ne mutane har so suke a nunota tana jawabi don ta iya magana ba ƙaɗan ba, a yadda mutane keta faɗa ba'a ta6a First Lady kamarta ba wadda ta ko ina tayi, su Fatuu da Mino ana can America Mino ta maida hankali tanata karatu haka Nameer ma.

Lokacin da za'ayi bikin cikar President shekara ɗaya a kan kujerar mulki aka shirya buɗe Companyn Haisam, da lokacin Hajji yayi gaba ɗayansu suka je harda shi shugaban ƙasan da Hajiya dasu Mom suma su Fatuu da Mino da Fanan da Haisam da Nameer nan Nigeria suka zo suka tafi tare harda Aunty Laila da Mijinta harda Jidderh ma duk wanda suka isa aikin Hajji a Familyn shugaban ƙasan saida suka je haka bangaren Minister Hajiya Maryam taje ita da Mijinta da Farha, sosae sukai ma shugaban ƙasa Addu'oi kan Allah ya tallafa mashi ya taya shi sauke nauyin dake kan shi kamar yadda ya roƙesu kan suyi mashi Addu'oin, Haisam ma sunyi mashi Addu'oin Allah yasa ya buɗe Companyn shi a sa'a, bayan gama aikin Hajjin suka dawo gida Nigeria, abun na Allah ne su Fatuu an zama Hajiya harda haƙorin Makka tasa haka ma Mino kuma sosae yay masu kyau, bayan dawowar su sun ɗan zauna a Nigeria Haisam ya duba ginin nashi wanda tuni yayi nisa lokacin Fatuu da Mino suka tafi Katsina Hajiya dai President ya ruƙeta kan sai ta ƙara hutawa sosae ita Hajiya Maryam ma cewa tayi kada ta koma Katsina ta dawo nan da zama kawai shima President ɗin dasu Mom suka nuna goyon bayan hakan Hajiyar ta nuna tafi son zama a can don ta saba da mutane kuma bai kamata ace duk sun baro can ba tunda nan ne tushen su, bayan zuwan su Fatuu Katsina har gidan Aunty Mareeya da Feenah taje ta kai masu tsaraba harda Abdul ɗan gidanta shima yasha tsaraba haka Aminiyarta ma Haulat tayo mata tsaraba kullum tana a gidan Gwaggo anan ma take kwana tunda shi Haisam na Abuja, bayan sati biyu suka koma America, bayan komawarsu ne Haisam yaba Fatuu da Fanan damar za6a ma Companyn suna yace yana son duk sunayen su ya fito a ciki nan suka shiga haɗa sunaye ita Fatuu tace ko asa HAIFAN ita kuma Fanan tace HAIFAT zai fi, ƙarshe dai HAIFAT TechWorld aka yanke saka ma Companyn.
Chapter 189 · 0% Book details