Sashe 72
Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 7 min read
..........A daidai bakin k'opa tana k'ok'arin fita cikin parlor sukai karo da Mutum, a razane ta kai idon ta fuskar shi nan take ta gane Haisam ne don gari ya fara wayewa, dawowar shi kenan daga Masallaci ya zo don yaji yadda suka k'are, ganinta a rud'e fuska sharkaf da hawaye yasa shi saurin kama ta yana tambayar lafiya da hannu ta rink'a nuna mashi saitin Hajiya tana fad'in tak'i tashi, kamata yay suka nufi ciki ta bangaren gefen Hajiyar ya zauna a bakin gadon ita kuma ta zagaya ta haye saman gadon idanu waje take kallon Hajiyar sai kuma ta kalli Haisam dake bubbuga Hajiyar yana kiranta, hankalin shi ne ya fara tashi har Fuskar shi ta bayyana ya kalli Fatuu ya ce mata miya faru da ita ne, wani Wahalallan miyau ta had'iya sai motsa baki take gaba d'aya ta zaro ido duk tayi kalar rashin gaskiya, k'ara tambayar ta yay yace ta fad'i mashi miya faru da ita ne cikin kuka murya na rawa tace "Don Allah Ya Haisam kayi hak'uri, wllh bada nufin haka nayi ba na rantse maka da Allah" mamaki ne ya bayyana akan fuskar shi jin abunda tace wanda yake nuni da wani abu tay ma Hajiyar, ce mata yay ta fad'i mashi abunda ya faru zai fahimceta da sauri ta fara fad'i mashi tiryan tiryan abunda tay mata na maganin baccin data bata guda biyu, d'an waro ido Haisam d'in yay cike da Al'ajabi yake kallon ta ganin yanayin shi yasa ta hau yin rantse rantse, gaba d'aya shima Haisam d'in ya rud'e ya rasa tunanin da zai yi ga Fatun ta gigice sosae wanda a halin da take ciki bai kamata ace ta tashi hankalin ta haka ba,
Hannuwanta ya kamo ya shiga rarrashinta yana fad'in ta kwantar da hankalin ta ya fahimce ta zata tashi in sha Allah, ganin ta d'an sassauto yasa shi tambayarta shi maganin data batan ta tabbatar baida illa, da sauri tace wllh baida illa na bacci ne ko su suna sha in sukai karatu sosae suka kasa bacci, jinjina mata kai yay ya maida idon shi akan hajiya, k'ok'arin tada ta yaci gaba da yi Fatun na taya shi, ganin tak'i tashi yasa shi kallon Fatun yace bai kamata suna 6ata lokaci ba bari yaje ya d'aukko Mota sai ya kaita Asibiti aikuwa a rud'e ta kamo hannun shi da duka hannuwanta tana girgiza mashi kai tace "Don Allah Yaya Haisam kada aje Asibitin wllh in aka je za'a gane an bata wani abu ne gashi Nameer ne ya siyo man kuma ba lalle a fahimce ni ba" shiru yay ya rasa miye abun yi don gaskiya ta fad'a saidae kuma yasan kaita Asibitin shi ya kamata, tambayarta yay an rage sauran Furan ne da sauri ta girgiza kai "a'a, duka muka shanye robobin na a cikin dust bin a parlor",
"Ok, ki kwantar da hankalin ki Hospital d'in yakamata akai ta zan san yadda za'ai baza'a gane kin bata wani abu ba muyi Addu'a Allah yasa komai yazo da Sauk'i" da sauri tace Amin, har zai sauka daga saman gadon sai kuma ya maido idon shi kanta yace ta sa mata ruwa ne da sauri ta girgiza mashi kai tace a'a ko taje ta kawo, da hannu yay mata alamar ta tsaya shi ya mik'e ya nufi hanyar parlor, bada jimawa ba ya dawo hannun shi ruk'e da bottle water daya d'aukko daga cikin Fridge ruwan mai d'an madaidaicin sanyi ne, bayan ya koma ya zauna bud'e murfin robar yay ya tarba hannun shi ya cika shi da ruwan, sai da yay bismilla sannan ya watsa mata shi a fuska nan take tay wata ajiyar zuciya, k'ara zaro ido Fatuu tay suka kalli juna da shi atare suka shiga kiran sunanta saidae bata k'ara yin wani abu ba daga haka, da sauri Fatuu tace mashi ya k'ara watsa mata ruwan, yana k'ara zuba mata ta k'ara yin ajiyar zuciya suka cigaba da kiran sunanta, Motsi ta fara yi Fatuu ta fara d'an murmushi, Haisam ne ya rankwafa yasa hannu yana d'an bubbuga gefen fuskar ta yana fad'in "Sweetheart open your Eyes" a hankali ta fara bud'e idanun tana yi tana rufe su yana cigaba da ce mata ta bud'e idanunta, lokacin data bud'e su gaba d'aya sun yi ja sosae tabi Haisam da kallo tamkar mai son gane wanene shi kuma ya d'an rankwafa da kan shi sai murmushi yake mata,
"Kai, wane gardi ne wannan a kai na, lafiyaaa???" da wani irin sauti tay Maganar nan take Fatuu ta bud'a baki Haisam ya d'aga ido ya kalleta gaba d'ayan su sun fahimci maganin bugar da ita yay da alama yayi mata k'arfi ne sosae, k'ara ce mashi tay waye shi ya d'age mata gira yace mata masoyinta ne ta wani k'ank'ance mashi ido fuska a tsuke, kallon Fatuu tay ta k'ura mata ido duk Fatun tasha jinin jikinta sai motsa baki take, hannu Haisam ya kai ya tada ita zaune ta jingina da kan gado yace mata ta kalle shi sosae ta kuwa zuba mashi ido, bayan wani lokaci yace mata to ta gane shi kawae sai ji yay tayi d'an guntun tsoki tace to shi d'in ne bata sani ba, murmushi yay tace wai mi ya faru ne shi kuma miya kawo shi nan, yana murmushi yace "da yake kin samu kan ki ko",
kai idon ta kan Fatuu dake ta zare ido tayi tace ita kuma wannan mi akai mata tayi kuka Haisam d'in na k'ok'arin bud'e baki yay magana a rud'e Fatuu ta hau girgiza mashi kai alamar kada ya fad'i mata, yar dariya yay yace ma Hajiyar hankalinta ne ya tashi tana ta tada ita gari ya waye amman tak'i tashi, hannu ta kai ta dafe goshinta Haisam d'in yace mata lafiya tace ciwo yake mata, sannu yayi mata yace ta tashi tayi salla sai tasha magani, tambayar shi tay anyi salla ne yace eh tun d'azun, da alamun mamaki tace to wai miya faru da ita ne haka ya d'an ta6e mata baki, tunani ta shiga yi can tace mashi tana zargin furar data sha jiya ce ta sata Nauyin bacci haka don tun a parlor jiya ta fara yin bacci da k'yar ta dawo d'aki kuma daga nan bata k'ara sanin inda kanta yake ba gashi yanzu suma sun ce suna ta tada ita bata tashi ba tabbas Furar nan ce, gaba d'aya Fatuu ta rud'e sai zare ido take Haisam ya kalleta suka had'a ido yanayin fuskar shi kamar zai yi dariya, ganin tana ta Maganar furar yasa shi ce mata dama ya ta6a sata haka ne tace a'a yace to ba shi bane, da sauri tace ai dama fura na bugarwa wani lokacin fa yace to tunda tasan hakan ba Shikenan ba miye na dogon magana ta tashi taje tayi salla kawai Allah ya kyauta gaba,
ganin tana ta k'ok'arin saukkowa yasa shi mik'ewa ya taimaka mata ta tashi tsaye tay mashi alamar ya bata sanda sai faman hamma take, ce mata yayi ko baccin bai ishe ta bane a k'ara nemo wani Furan ya saci kallon Fatuu suka had'a ido ta tura mashi baki yay yar dariya, duk da sandar saida ya kaita har bakin toilet don sai fad'i take jikinta ba kwari yace mata sai ta fara yin wanka taji k'arfi ta d'aga mashi kai, tura kopar toilet d'in tay yana ta fad'in tabi a hankali, saida yaga ta shige sannan ya juyo ya dawo wurin gadon ta side d'in da Fatun take idonta akan shi, zama yay a bakin gadon ya mik'a mata hannu ta matso, jawota yay jikinshi kawai sai ta fashe da kuka ya shiga rarrashinta yana fad'in ba Shikenan ba tunda ta farka, bayan tayi shiru ya tambayi ba abunda ke mata ciwo ta d'aga mashi kai alamar eh, shiru suka d'an yi kafin can k'asa k'asa da murya ya rad'a mata ta rage sauran maganin anjima da daddare a k'ara bata suje part d'in shi a zabure ta d'ago ta kalleshi kawai sai gani tay ya saka dariya aikuwa ta kai hannu ta bugi chest d'in shi ta fara k'ok'arin raba jikinsu ya matseta yana cigaba da yin dariyar yace shima ai wasa ne yayi mata ko irin wanda tay mashi tay d'an murmushi tare da lumshe ido ta maida kanta saman chest d'in nashi sosae yanzu hankalin ta ya kwanta amman ba k'aramar razana tayi ba, kai bakin shi yay saitin kunnanta cikin rad'a yace mata kar ta k'ara irin wannan kuskuren da sauri ta d'aga mashi kai kafin a hankali tace bazata k'ara ba ya jinjina mata kai.
Hannuwanta ya kamo ya shiga rarrashinta yana fad'in ta kwantar da hankalin ta ya fahimce ta zata tashi in sha Allah, ganin ta d'an sassauto yasa shi tambayarta shi maganin data batan ta tabbatar baida illa, da sauri tace wllh baida illa na bacci ne ko su suna sha in sukai karatu sosae suka kasa bacci, jinjina mata kai yay ya maida idon shi akan hajiya, k'ok'arin tada ta yaci gaba da yi Fatun na taya shi, ganin tak'i tashi yasa shi kallon Fatun yace bai kamata suna 6ata lokaci ba bari yaje ya d'aukko Mota sai ya kaita Asibiti aikuwa a rud'e ta kamo hannun shi da duka hannuwanta tana girgiza mashi kai tace "Don Allah Yaya Haisam kada aje Asibitin wllh in aka je za'a gane an bata wani abu ne gashi Nameer ne ya siyo man kuma ba lalle a fahimce ni ba" shiru yay ya rasa miye abun yi don gaskiya ta fad'a saidae kuma yasan kaita Asibitin shi ya kamata, tambayarta yay an rage sauran Furan ne da sauri ta girgiza kai "a'a, duka muka shanye robobin na a cikin dust bin a parlor",
"Ok, ki kwantar da hankalin ki Hospital d'in yakamata akai ta zan san yadda za'ai baza'a gane kin bata wani abu ba muyi Addu'a Allah yasa komai yazo da Sauk'i" da sauri tace Amin, har zai sauka daga saman gadon sai kuma ya maido idon shi kanta yace ta sa mata ruwa ne da sauri ta girgiza mashi kai tace a'a ko taje ta kawo, da hannu yay mata alamar ta tsaya shi ya mik'e ya nufi hanyar parlor, bada jimawa ba ya dawo hannun shi ruk'e da bottle water daya d'aukko daga cikin Fridge ruwan mai d'an madaidaicin sanyi ne, bayan ya koma ya zauna bud'e murfin robar yay ya tarba hannun shi ya cika shi da ruwan, sai da yay bismilla sannan ya watsa mata shi a fuska nan take tay wata ajiyar zuciya, k'ara zaro ido Fatuu tay suka kalli juna da shi atare suka shiga kiran sunanta saidae bata k'ara yin wani abu ba daga haka, da sauri Fatuu tace mashi ya k'ara watsa mata ruwan, yana k'ara zuba mata ta k'ara yin ajiyar zuciya suka cigaba da kiran sunanta, Motsi ta fara yi Fatuu ta fara d'an murmushi, Haisam ne ya rankwafa yasa hannu yana d'an bubbuga gefen fuskar ta yana fad'in "Sweetheart open your Eyes" a hankali ta fara bud'e idanun tana yi tana rufe su yana cigaba da ce mata ta bud'e idanunta, lokacin data bud'e su gaba d'aya sun yi ja sosae tabi Haisam da kallo tamkar mai son gane wanene shi kuma ya d'an rankwafa da kan shi sai murmushi yake mata,
"Kai, wane gardi ne wannan a kai na, lafiyaaa???" da wani irin sauti tay Maganar nan take Fatuu ta bud'a baki Haisam ya d'aga ido ya kalleta gaba d'ayan su sun fahimci maganin bugar da ita yay da alama yayi mata k'arfi ne sosae, k'ara ce mashi tay waye shi ya d'age mata gira yace mata masoyinta ne ta wani k'ank'ance mashi ido fuska a tsuke, kallon Fatuu tay ta k'ura mata ido duk Fatun tasha jinin jikinta sai motsa baki take, hannu Haisam ya kai ya tada ita zaune ta jingina da kan gado yace mata ta kalle shi sosae ta kuwa zuba mashi ido, bayan wani lokaci yace mata to ta gane shi kawae sai ji yay tayi d'an guntun tsoki tace to shi d'in ne bata sani ba, murmushi yay tace wai mi ya faru ne shi kuma miya kawo shi nan, yana murmushi yace "da yake kin samu kan ki ko",
kai idon ta kan Fatuu dake ta zare ido tayi tace ita kuma wannan mi akai mata tayi kuka Haisam d'in na k'ok'arin bud'e baki yay magana a rud'e Fatuu ta hau girgiza mashi kai alamar kada ya fad'i mata, yar dariya yay yace ma Hajiyar hankalinta ne ya tashi tana ta tada ita gari ya waye amman tak'i tashi, hannu ta kai ta dafe goshinta Haisam d'in yace mata lafiya tace ciwo yake mata, sannu yayi mata yace ta tashi tayi salla sai tasha magani, tambayar shi tay anyi salla ne yace eh tun d'azun, da alamun mamaki tace to wai miya faru da ita ne haka ya d'an ta6e mata baki, tunani ta shiga yi can tace mashi tana zargin furar data sha jiya ce ta sata Nauyin bacci haka don tun a parlor jiya ta fara yin bacci da k'yar ta dawo d'aki kuma daga nan bata k'ara sanin inda kanta yake ba gashi yanzu suma sun ce suna ta tada ita bata tashi ba tabbas Furar nan ce, gaba d'aya Fatuu ta rud'e sai zare ido take Haisam ya kalleta suka had'a ido yanayin fuskar shi kamar zai yi dariya, ganin tana ta Maganar furar yasa shi ce mata dama ya ta6a sata haka ne tace a'a yace to ba shi bane, da sauri tace ai dama fura na bugarwa wani lokacin fa yace to tunda tasan hakan ba Shikenan ba miye na dogon magana ta tashi taje tayi salla kawai Allah ya kyauta gaba,
ganin tana ta k'ok'arin saukkowa yasa shi mik'ewa ya taimaka mata ta tashi tsaye tay mashi alamar ya bata sanda sai faman hamma take, ce mata yayi ko baccin bai ishe ta bane a k'ara nemo wani Furan ya saci kallon Fatuu suka had'a ido ta tura mashi baki yay yar dariya, duk da sandar saida ya kaita har bakin toilet don sai fad'i take jikinta ba kwari yace mata sai ta fara yin wanka taji k'arfi ta d'aga mashi kai, tura kopar toilet d'in tay yana ta fad'in tabi a hankali, saida yaga ta shige sannan ya juyo ya dawo wurin gadon ta side d'in da Fatun take idonta akan shi, zama yay a bakin gadon ya mik'a mata hannu ta matso, jawota yay jikinshi kawai sai ta fashe da kuka ya shiga rarrashinta yana fad'in ba Shikenan ba tunda ta farka, bayan tayi shiru ya tambayi ba abunda ke mata ciwo ta d'aga mashi kai alamar eh, shiru suka d'an yi kafin can k'asa k'asa da murya ya rad'a mata ta rage sauran maganin anjima da daddare a k'ara bata suje part d'in shi a zabure ta d'ago ta kalleshi kawai sai gani tay ya saka dariya aikuwa ta kai hannu ta bugi chest d'in shi ta fara k'ok'arin raba jikinsu ya matseta yana cigaba da yin dariyar yace shima ai wasa ne yayi mata ko irin wanda tay mashi tay d'an murmushi tare da lumshe ido ta maida kanta saman chest d'in nashi sosae yanzu hankalin ta ya kwanta amman ba k'aramar razana tayi ba, kai bakin shi yay saitin kunnanta cikin rad'a yace mata kar ta k'ara irin wannan kuskuren da sauri ta d'aga mashi kai kafin a hankali tace bazata k'ara ba ya jinjina mata kai.