Sashe 184
Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 11 min read
"Mutum ne amman wanda bai kai yayi soyayya da ita ba" ɗan ta6e baki Hajiya tayi tace "to ni a wurina ya akai shiyasa ban dakatar da abun ba" yarfa hannu Hajiya Maryam tayi muryarta har tana sarƙewa wurin faɗin "Wai Hajjaju miyasa a koda yaushe kike goyon bayan bare ne taya za'ace wai kamar Farha ta auri wannan dangin ƙarnin" faɗaɗa dariya Hajiya tayi tace "A'a Maryam banda sharri, anan ai ba bare na goyi baya ba tamun na goya ma baya tunda ita ta fara nuna tana son shi hasali ma su dangin yaron ba so suke ba don kakarshi har nan ta same ni tayi man magana kan hakan kinga da bare na goya ma baya to zan ƙi abun ne", cikin huci tace ai duk wannan munafurci ne don sun san sun asirce Farhar Hajiya ta shiga girgiza kai tace "anya Maryam, taya akai wai kike neman barin imanin ki yay rauni ne, komai kice anyi asiri",
Murya kamar zata yi kuka tace to in ba asirin ba taya Farha zata kamu da son wannan yaron Hajiyar tace ta in Allah ya ƙaddaro hakan don haka tana bata shawara tabi komai a hankali in har Allah ya ƙaddaro aure tsakanin su to dole zasu yi, ai kamar Hajiyar ta watsa mata garwashin wuta a cikin zuciya cike da cin alwashi tace Wllh bazata bari Farha ta auri wannan yaron ba Hajiya tace ai shikenan ɗiyarta ce tayi duk abunda take ganin yayi mata Hajiya Maryam ɗin tace zatayi kuma ta faɗi ma kakar yaron in ma wani abu sukai ma ɗiyarta suyi gaggawar warware shi in ba haka ba duk abunda ya faru dasu to su suka siya ma kansu Hajiya tace tsakaninsu ne tazo da kanta sai ta faɗi masu,
tana niyyar kashe wayar Hajiya tace "Maryam ina son ki sani yadda kike uwar zamani haka Farha take ɗiyar zamani sannan yin jayyaya da ikon Allah tamkar ɗaukar dutsen Dala ba gammo ne don haka ina mai baki shawara da ki bi komai a hankali sannan kibar ikon Allah yay aikin shi, ki gaida man da kowa" daga haka ta yanke wayar,
komawa Hajiya Maryam tay ta zauna da6as saman gado ta shiga juya Maganar Hajiya ta ƙarshe nan take ta yanke wani abu a ranta, gaba ɗaya yinin ranar a cikin ɗaki Farha ta wuni koda lokacin cin abinci yay aka aiko kiranta ƙin fita tayi ƙarshe saidai Dad ɗin su yazo ya fito da ita suna zuwa Dining ɗin Hajiya Maryam ta miƙe ta bar wurin hakan yasa Farhar fashewa da kuka Dad ɗinta ya shiga rarrashinta, ganin abunda ya faru yasa da daddare Dad ɗin bai matsa ma Farhar ta fito ba bayan sun gama cin abincin ya ɗauki nata ya kai mata ɗaki saida ya zauna taci sannan ya baro ɗakin, a daren ta kira Fanan tana kuka ta faɗi mata abunda ke faruwa itama rarrashinta ta shiga yi tace tunda Dad ya nuna zai taimaka mata ta kwantar da hankalinta tasan Momynsu nada zuciya dole bazata goyi bayan abun ba ta cikin sauƙi amman itama tana goyon bayan abunda take so don haka zata tayata da Addu'a itama ta dage da yi tace to tare da yi mata godiya, suna gama yin wayar Fanan ta kira Mom ɗin nasu ko daga yanayin muryarta ta fahimci tana cikin 6acin rai, bayan sun gaisa cikin kwantar da murya Fanan ɗin ta fara lallashinta tana nuna mata ba aibu bane don Farha ta auri Kamal tasan kawai don basu da arzuƙi ne matsalansu kuma shi na Allah ne a duk lokacin daya so sai ya azurta bawa haka mai kuɗin ma duk yawan kuɗinshi cikin few seconds sai ya maida mutum talaka don haka suyi fatan alkhairi a gare su kawai, har ta gama maganarta Mom ɗin bata katseta ba saida ta gama tace mata ta gama Fanan ɗin tace eh kawai sai ta kashe wayar tare da buga uban tsoki, gaba ɗaya Farha ta koma rayuwar ɗaki washe gari lahadi da yamma Hajiya Maryam ta shirya komawa Abuja taci gayu cikin jigunannan lace ta soke kallabi bayan ta fito ne ta nufi ɗakin Farha lokacin data shiga tana kwance kan gado kamar mara lafiya tana ganin Mom ɗin nasu ta shigo ta yunƙura ta tashi zaune tana kallonta can ta gaishe da ita a hankali Mom ɗin ta ta6e baki tace ta ruƙe gaisuwarta bata so ai yanzu bata da daraja a wurinta saboda dangin shanu shiyasa bata iya zuwa ta gaishe da ita, idanun Farhar ne suka ciko da ƙwalla tace mata tayi haƙuri Hajiya Maryam ɗin ta ƙara ta6e baki tace ita ai zata ba haƙuri don tazo ne ta sanar mata nan da sati biyu za'a ɗaura auranta da Emran don haka gara ta tsaida hankalinta wuri ɗaya tana gama faɗin hakan ta juya ta tafi Farhar tasa wani irin kuka tana faɗin Wllh bazata aure shi ba Kamal zata aura in ba haka ba mutuwa zatai, daidai Hajiya Maryam ta kai bakin ƙopa ta watsa mata hannu daga haka ta fuce. Gaba ɗaya hankalin Dr ya tashi ganin halin da Farhar take ciki kullum cikin kuka ta daina cin abinci sai ya rarrasheta dole hankalinshi ya kasu biyu wurin aiki da kuma gida a haka har sati ya ƙare Hajiya Maryam ɗin ta dawo ya sameta don suyi magana ya nuna mata gara a bar Farhar ta auri wanda take so don tana niyyar lahanta kanta Hajiya Maryam ɗin tace ya rabu da ita duk tana yi ne don a saduda a goyi bayanta da an ɗaura masu aure da Emran ya tafi da ita America zata koma daidai, bayan ta gama Weekend ta koma an shiga wani satin ganin yana niyyar rasa ɗiyarshi yasa ya kirawo Hajiya ya sanar mata halin da Farhar ke ciki da hukuncin da Hajiya Maryam ta yanke na ɗaura masu aure da Emran a satin Hajiya na jin haka ta saka salati tace Maryam badai taurin kai ba ai ita bata san da ta yanke wannan hukuncin ba tace ma Dr ɗin abunda za'ai yasa Farha ta rubuta takarda cewa tunda an hanata wanda take so to ta shiga duniya kuma kada a nemeta don baza'a sameta ba in ta rubuta sai ya turo mata ita amman kada ta hawo jirgin Katsina ta hawo na Kano in ta sauka sai ta hau Motar haya ta ƙaraso Katsina sannan kada ya bari kowa yasan da wannan plan ɗin daga shi sai Farhar kuma ya siya mata sabon layin waya sannan itama wayar ya siya mata ƙarama tata ta baro ta nan gida, bayan sun gama wayar tasa ya kai ma Farha wayarshi ta sanar da ita yadda sukai da Mahaifinta tace mata ta kwantar da hankalinta ta samu niƙab in ta isa kano ta saka shi a fuskarta har ta iso Katsina sannan kuma tayi dubara ta saka dogon Hijab a park ɗin data iso Katsina sai ta kirata ta sanar mata zata sa azo a ɗauketa da sauri tace to, kamar yadda suka tsara haka sukai ya sakata ta siya ticket ta online washe gari ya kama talata lokacin duk ƙannanta sun tafi School shima Dad ɗin ya fito daga gidan matsayin ya tafi aiki bayan wani lokaci ya kirata ta sabon layinta yace ta fito daga gidan koda wani zai tambayi ina zata tace zata je Abuja ne wurin Mom ɗinta, tana janye da madaidaicin trolley ta fito cikin sa'a har ta fito daga gidan ba wanda ya ganta sai Security dake gadin gate da suka gaisa suka tambayi unguwa zata je ne tace eh zata Abuja wurin Mom ɗinta har wani yace to ina driver ta fito ita kaɗai tace bai dawo daga kai su Noor School ba tana sauri zata hau taxi kawai sukai mata Allah ya kiyaye, bayan sun haɗu da Dad ɗin nata inda ya tsaya tace ya bari ta hau taxi tunda in ya kaita Airport za'a iya gane plan ne tunda akwae cctv yace ta bari in suka kusa isa sai ta hau taxi ɗin, tun a cikin Motar ta naɗa gyalenta tayi kamar niƙab a cikin Motar suka yi bankwana da Dad ɗin nata duk ya damu, bayan ta fito saida ta samu taxi ta hau sannan Dad ɗin nata ya tafi har suka isa Airport bata buɗe fuskarta ba sai bayan data shiga tana janye da trolley da zasu tafi sannan ta buɗe, bayan sun iso Kano fuskarta a rufe ta bar Airport ɗin ta hau keke napep don ya kaita tasha, wuraren azahar ta iso Katsina ta kira Hajiya ta sanar mata ta tambayi inda take bayan ta faɗi mata ta kira Tk ta sanar dashi ya ɗauki Mota tinted yaje ya taho da Farhar tace kada ya ɗaukkota a tashar in ya kusa isa ya kirata ta fito sai su haɗu kan hanya ya ɗaukkota, duk yadda Hajiya ta tsara haka akayi lokacin da suka iso gidan Hajiya na Bedroom bata daɗe da gama yin sallar Azahar ba Farhar ta shigo tana hangota ta nufota da sauri tana zuwa ta faɗa jikinta tana kuka Hajiyar na murmushi tace mata ya isa miye abun kuka, gaba ɗaya su Saude da Husnah harda Tk saida Hajiya taja kunnansu kan kar wanda ya sake ya bayyana Farhar na gidan koda za'a tambaye su nan gaba har su Gwaggo tace kar a bari su san da zuwanta gidan duk suka ce to, itama Farhar tace mata kada ta bari kowa yasan tana gidan har Kamalun tace to. Lokacin da Dr ya kira Hajiya Maryam da alamun tashin hankali ya sanar mata zancen barin Farha gida da takardar data bari harda wayarta zo kaga rawar jiki da tsananin tashin hankali ta shiga tambayar ina taje ya akai har ta bar gida ba wanda ya sani yace to shi dai ya tafi wurin aiki yara kuma an tafi kai su School koda ya dawo dubata kamar yadda yake yi sai dai takarda ya gani kuma ya tambayi security sun tabbatar mashi da fita tayi kuma cewa tayi wurinta zata zo Abuja, a fusace tace to ubanwa yace su bari ta fita Dr yace sunce ba'a basu umarnin su hana wani ya fita ba sai lokacin ta tuna da haka gaba ɗaya ta gama ruɗewa tace mashi a bibbincika inda ake tunanin zata iya zuwa pls yace mata bai tunanin zata tsaya kusa don da gani ta shirya ma abun bazata tsaya inda za'a ganota ba shi dama abunda yaketa kwatanta mata kenan tace yanzu ba lokacin wannan bane duk da haka adai bincika ko ina itama zata kira wasu wuraren taji ko taje can, abu kamar wasa har zuwa yamma ba'a ji taje wani wuri ba, lokacin da ta kira Hajiya ta tambayi ko Farha tazo da alamun mamaki ta tambayi ina Farhar taje farko shiru Hajiya Maryam ɗin tayi saida Hajiya ta ɗaga mata murya tace bazata faɗi mata ba sannan tace aje takarda tayi wai tunda baza'a bata wanda take so ba ta shiga duniya, wani salati da Hajiya ta saka baka ta6a cewa tasan inda Farhar take da alamun tashin hankali tace yanzu duk Maganar data yi mata shine bata ji ba saida tayi sanadin barin ta gida kamar Hajiya Maryam ɗin zatai kuka tace yanzu dai don Allah ta bar Maganar a taya su bincikawa inda ake tunanin zata iya zuwa, zuwa dare har zancen 6atan Farhar ya fara baza wurare har Mai girma shugaban ƙasa yaji sosae hankalinshi ya tashi ba kamar da yaji cewa takarda ta aje ta tafi shima da kan shi ya shiga kiran yan'uwa na jiki yana tambayar ko taje in aka ce bata je ba sai yace to a taya su bincikawa, lokacin da ya kira Hajiya nan ta warware mashi komai tace su kwantar da hankalinsu Farhar na wurinta amman kada a bari Hajiya Maryam ɗin taji in ba haka aka yi mata ba bazata saduda ta ƙyale yarinyar ba hakan kuma na iya haifar da abunda za'ayi dana sani tunda yaran zamani ba'a cewa za'a yi masu dole yace ya fahimta, Washe gari tunda safe Hajiya Maryam ta koma Lagos nan fa aka hau bincike wurare daban daban har gidajen radio da Tv aka kai cigiya ko wani ya ganta har binciken lambar wayarta akayi aka tabbatar wayar da tayi ta ƙarshe anan Lagos ne, kan kace mi zancen 6atan ya karaɗe social media ana ta faɗin ɗiyar ƙanwar shugaban ƙasa kuma Minister Maryam Adamu Zakee ta 6ace sai dai ba wanda yasan dalilin 6atan nata don ba'a bayyana ba da yawan mutane sun tafi akan ƙilan kidnapping ɗinta akai, har su Fanan sun samu labarin sosae hankalin Fanan ya tashi har ta fara shirin tahowa Nigeria Haisam ya kira Hajiya kan 6acewar Farha ɗin nan ta bayyana mashi komai tace su kwantar da hankalinsu amman kada wanda ya sanar ma Hajiya Maryam ɗin saida Fanan taji haka sannan hankalinta ya kwanta har waya sukai da Farhar amman ita Hajiya Maryam duk sai suka nuna mata hankulansu ya tashi, da yake abun na masu ƙasa ne an zurfafa bincike sai gashi zuwa yamma an tabbatar da ta siya ticket online kuma ta hau jirgin Kano a jiya nan da nan bincike ya koma Kano, bayan an tabbatar da taje kano Hajiya Maryam ta kira Hajiya ta sanar mata ta tambayi ko ta ƙaraso nan Katsina Hajiya tace a'a bata zo ba ai in nan zata zo mi zai sa ta hau jirgin Kano, cike da nuna Al'ajabi Hajiyar tace "to amman wai mi zaisa Farha taje kano, ko kinada mutanen da kike tunanin zata iya zuwa can wurinsu??" cike da damuwa Hajiya Maryam tace tana da abokan kasuwancinta acan saidai Farhar bata san su ba sai kuma abokanta da sukayi karatu tare suma ba kowanne Farha ta sani ba sai wata ƙawarta guda Hajiya Turai kuma ta kirata ta tambayi ko Farhar taje wurinta ta tabbatar mata da bata je ba,
Murya kamar zata yi kuka tace to in ba asirin ba taya Farha zata kamu da son wannan yaron Hajiyar tace ta in Allah ya ƙaddaro hakan don haka tana bata shawara tabi komai a hankali in har Allah ya ƙaddaro aure tsakanin su to dole zasu yi, ai kamar Hajiyar ta watsa mata garwashin wuta a cikin zuciya cike da cin alwashi tace Wllh bazata bari Farha ta auri wannan yaron ba Hajiya tace ai shikenan ɗiyarta ce tayi duk abunda take ganin yayi mata Hajiya Maryam ɗin tace zatayi kuma ta faɗi ma kakar yaron in ma wani abu sukai ma ɗiyarta suyi gaggawar warware shi in ba haka ba duk abunda ya faru dasu to su suka siya ma kansu Hajiya tace tsakaninsu ne tazo da kanta sai ta faɗi masu,
tana niyyar kashe wayar Hajiya tace "Maryam ina son ki sani yadda kike uwar zamani haka Farha take ɗiyar zamani sannan yin jayyaya da ikon Allah tamkar ɗaukar dutsen Dala ba gammo ne don haka ina mai baki shawara da ki bi komai a hankali sannan kibar ikon Allah yay aikin shi, ki gaida man da kowa" daga haka ta yanke wayar,
komawa Hajiya Maryam tay ta zauna da6as saman gado ta shiga juya Maganar Hajiya ta ƙarshe nan take ta yanke wani abu a ranta, gaba ɗaya yinin ranar a cikin ɗaki Farha ta wuni koda lokacin cin abinci yay aka aiko kiranta ƙin fita tayi ƙarshe saidai Dad ɗin su yazo ya fito da ita suna zuwa Dining ɗin Hajiya Maryam ta miƙe ta bar wurin hakan yasa Farhar fashewa da kuka Dad ɗinta ya shiga rarrashinta, ganin abunda ya faru yasa da daddare Dad ɗin bai matsa ma Farhar ta fito ba bayan sun gama cin abincin ya ɗauki nata ya kai mata ɗaki saida ya zauna taci sannan ya baro ɗakin, a daren ta kira Fanan tana kuka ta faɗi mata abunda ke faruwa itama rarrashinta ta shiga yi tace tunda Dad ya nuna zai taimaka mata ta kwantar da hankalinta tasan Momynsu nada zuciya dole bazata goyi bayan abun ba ta cikin sauƙi amman itama tana goyon bayan abunda take so don haka zata tayata da Addu'a itama ta dage da yi tace to tare da yi mata godiya, suna gama yin wayar Fanan ta kira Mom ɗin nasu ko daga yanayin muryarta ta fahimci tana cikin 6acin rai, bayan sun gaisa cikin kwantar da murya Fanan ɗin ta fara lallashinta tana nuna mata ba aibu bane don Farha ta auri Kamal tasan kawai don basu da arzuƙi ne matsalansu kuma shi na Allah ne a duk lokacin daya so sai ya azurta bawa haka mai kuɗin ma duk yawan kuɗinshi cikin few seconds sai ya maida mutum talaka don haka suyi fatan alkhairi a gare su kawai, har ta gama maganarta Mom ɗin bata katseta ba saida ta gama tace mata ta gama Fanan ɗin tace eh kawai sai ta kashe wayar tare da buga uban tsoki, gaba ɗaya Farha ta koma rayuwar ɗaki washe gari lahadi da yamma Hajiya Maryam ta shirya komawa Abuja taci gayu cikin jigunannan lace ta soke kallabi bayan ta fito ne ta nufi ɗakin Farha lokacin data shiga tana kwance kan gado kamar mara lafiya tana ganin Mom ɗin nasu ta shigo ta yunƙura ta tashi zaune tana kallonta can ta gaishe da ita a hankali Mom ɗin ta ta6e baki tace ta ruƙe gaisuwarta bata so ai yanzu bata da daraja a wurinta saboda dangin shanu shiyasa bata iya zuwa ta gaishe da ita, idanun Farhar ne suka ciko da ƙwalla tace mata tayi haƙuri Hajiya Maryam ɗin ta ƙara ta6e baki tace ita ai zata ba haƙuri don tazo ne ta sanar mata nan da sati biyu za'a ɗaura auranta da Emran don haka gara ta tsaida hankalinta wuri ɗaya tana gama faɗin hakan ta juya ta tafi Farhar tasa wani irin kuka tana faɗin Wllh bazata aure shi ba Kamal zata aura in ba haka ba mutuwa zatai, daidai Hajiya Maryam ta kai bakin ƙopa ta watsa mata hannu daga haka ta fuce. Gaba ɗaya hankalin Dr ya tashi ganin halin da Farhar take ciki kullum cikin kuka ta daina cin abinci sai ya rarrasheta dole hankalinshi ya kasu biyu wurin aiki da kuma gida a haka har sati ya ƙare Hajiya Maryam ɗin ta dawo ya sameta don suyi magana ya nuna mata gara a bar Farhar ta auri wanda take so don tana niyyar lahanta kanta Hajiya Maryam ɗin tace ya rabu da ita duk tana yi ne don a saduda a goyi bayanta da an ɗaura masu aure da Emran ya tafi da ita America zata koma daidai, bayan ta gama Weekend ta koma an shiga wani satin ganin yana niyyar rasa ɗiyarshi yasa ya kirawo Hajiya ya sanar mata halin da Farhar ke ciki da hukuncin da Hajiya Maryam ta yanke na ɗaura masu aure da Emran a satin Hajiya na jin haka ta saka salati tace Maryam badai taurin kai ba ai ita bata san da ta yanke wannan hukuncin ba tace ma Dr ɗin abunda za'ai yasa Farha ta rubuta takarda cewa tunda an hanata wanda take so to ta shiga duniya kuma kada a nemeta don baza'a sameta ba in ta rubuta sai ya turo mata ita amman kada ta hawo jirgin Katsina ta hawo na Kano in ta sauka sai ta hau Motar haya ta ƙaraso Katsina sannan kada ya bari kowa yasan da wannan plan ɗin daga shi sai Farhar kuma ya siya mata sabon layin waya sannan itama wayar ya siya mata ƙarama tata ta baro ta nan gida, bayan sun gama wayar tasa ya kai ma Farha wayarshi ta sanar da ita yadda sukai da Mahaifinta tace mata ta kwantar da hankalinta ta samu niƙab in ta isa kano ta saka shi a fuskarta har ta iso Katsina sannan kuma tayi dubara ta saka dogon Hijab a park ɗin data iso Katsina sai ta kirata ta sanar mata zata sa azo a ɗauketa da sauri tace to, kamar yadda suka tsara haka sukai ya sakata ta siya ticket ta online washe gari ya kama talata lokacin duk ƙannanta sun tafi School shima Dad ɗin ya fito daga gidan matsayin ya tafi aiki bayan wani lokaci ya kirata ta sabon layinta yace ta fito daga gidan koda wani zai tambayi ina zata tace zata je Abuja ne wurin Mom ɗinta, tana janye da madaidaicin trolley ta fito cikin sa'a har ta fito daga gidan ba wanda ya ganta sai Security dake gadin gate da suka gaisa suka tambayi unguwa zata je ne tace eh zata Abuja wurin Mom ɗinta har wani yace to ina driver ta fito ita kaɗai tace bai dawo daga kai su Noor School ba tana sauri zata hau taxi kawai sukai mata Allah ya kiyaye, bayan sun haɗu da Dad ɗin nata inda ya tsaya tace ya bari ta hau taxi tunda in ya kaita Airport za'a iya gane plan ne tunda akwae cctv yace ta bari in suka kusa isa sai ta hau taxi ɗin, tun a cikin Motar ta naɗa gyalenta tayi kamar niƙab a cikin Motar suka yi bankwana da Dad ɗin nata duk ya damu, bayan ta fito saida ta samu taxi ta hau sannan Dad ɗin nata ya tafi har suka isa Airport bata buɗe fuskarta ba sai bayan data shiga tana janye da trolley da zasu tafi sannan ta buɗe, bayan sun iso Kano fuskarta a rufe ta bar Airport ɗin ta hau keke napep don ya kaita tasha, wuraren azahar ta iso Katsina ta kira Hajiya ta sanar mata ta tambayi inda take bayan ta faɗi mata ta kira Tk ta sanar dashi ya ɗauki Mota tinted yaje ya taho da Farhar tace kada ya ɗaukkota a tashar in ya kusa isa ya kirata ta fito sai su haɗu kan hanya ya ɗaukkota, duk yadda Hajiya ta tsara haka akayi lokacin da suka iso gidan Hajiya na Bedroom bata daɗe da gama yin sallar Azahar ba Farhar ta shigo tana hangota ta nufota da sauri tana zuwa ta faɗa jikinta tana kuka Hajiyar na murmushi tace mata ya isa miye abun kuka, gaba ɗaya su Saude da Husnah harda Tk saida Hajiya taja kunnansu kan kar wanda ya sake ya bayyana Farhar na gidan koda za'a tambaye su nan gaba har su Gwaggo tace kar a bari su san da zuwanta gidan duk suka ce to, itama Farhar tace mata kada ta bari kowa yasan tana gidan har Kamalun tace to. Lokacin da Dr ya kira Hajiya Maryam da alamun tashin hankali ya sanar mata zancen barin Farha gida da takardar data bari harda wayarta zo kaga rawar jiki da tsananin tashin hankali ta shiga tambayar ina taje ya akai har ta bar gida ba wanda ya sani yace to shi dai ya tafi wurin aiki yara kuma an tafi kai su School koda ya dawo dubata kamar yadda yake yi sai dai takarda ya gani kuma ya tambayi security sun tabbatar mashi da fita tayi kuma cewa tayi wurinta zata zo Abuja, a fusace tace to ubanwa yace su bari ta fita Dr yace sunce ba'a basu umarnin su hana wani ya fita ba sai lokacin ta tuna da haka gaba ɗaya ta gama ruɗewa tace mashi a bibbincika inda ake tunanin zata iya zuwa pls yace mata bai tunanin zata tsaya kusa don da gani ta shirya ma abun bazata tsaya inda za'a ganota ba shi dama abunda yaketa kwatanta mata kenan tace yanzu ba lokacin wannan bane duk da haka adai bincika ko ina itama zata kira wasu wuraren taji ko taje can, abu kamar wasa har zuwa yamma ba'a ji taje wani wuri ba, lokacin da ta kira Hajiya ta tambayi ko Farha tazo da alamun mamaki ta tambayi ina Farhar taje farko shiru Hajiya Maryam ɗin tayi saida Hajiya ta ɗaga mata murya tace bazata faɗi mata ba sannan tace aje takarda tayi wai tunda baza'a bata wanda take so ba ta shiga duniya, wani salati da Hajiya ta saka baka ta6a cewa tasan inda Farhar take da alamun tashin hankali tace yanzu duk Maganar data yi mata shine bata ji ba saida tayi sanadin barin ta gida kamar Hajiya Maryam ɗin zatai kuka tace yanzu dai don Allah ta bar Maganar a taya su bincikawa inda ake tunanin zata iya zuwa, zuwa dare har zancen 6atan Farhar ya fara baza wurare har Mai girma shugaban ƙasa yaji sosae hankalinshi ya tashi ba kamar da yaji cewa takarda ta aje ta tafi shima da kan shi ya shiga kiran yan'uwa na jiki yana tambayar ko taje in aka ce bata je ba sai yace to a taya su bincikawa, lokacin da ya kira Hajiya nan ta warware mashi komai tace su kwantar da hankalinsu Farhar na wurinta amman kada a bari Hajiya Maryam ɗin taji in ba haka aka yi mata ba bazata saduda ta ƙyale yarinyar ba hakan kuma na iya haifar da abunda za'ayi dana sani tunda yaran zamani ba'a cewa za'a yi masu dole yace ya fahimta, Washe gari tunda safe Hajiya Maryam ta koma Lagos nan fa aka hau bincike wurare daban daban har gidajen radio da Tv aka kai cigiya ko wani ya ganta har binciken lambar wayarta akayi aka tabbatar wayar da tayi ta ƙarshe anan Lagos ne, kan kace mi zancen 6atan ya karaɗe social media ana ta faɗin ɗiyar ƙanwar shugaban ƙasa kuma Minister Maryam Adamu Zakee ta 6ace sai dai ba wanda yasan dalilin 6atan nata don ba'a bayyana ba da yawan mutane sun tafi akan ƙilan kidnapping ɗinta akai, har su Fanan sun samu labarin sosae hankalin Fanan ya tashi har ta fara shirin tahowa Nigeria Haisam ya kira Hajiya kan 6acewar Farha ɗin nan ta bayyana mashi komai tace su kwantar da hankalinsu amman kada wanda ya sanar ma Hajiya Maryam ɗin saida Fanan taji haka sannan hankalinta ya kwanta har waya sukai da Farhar amman ita Hajiya Maryam duk sai suka nuna mata hankulansu ya tashi, da yake abun na masu ƙasa ne an zurfafa bincike sai gashi zuwa yamma an tabbatar da ta siya ticket online kuma ta hau jirgin Kano a jiya nan da nan bincike ya koma Kano, bayan an tabbatar da taje kano Hajiya Maryam ta kira Hajiya ta sanar mata ta tambayi ko ta ƙaraso nan Katsina Hajiya tace a'a bata zo ba ai in nan zata zo mi zai sa ta hau jirgin Kano, cike da nuna Al'ajabi Hajiyar tace "to amman wai mi zaisa Farha taje kano, ko kinada mutanen da kike tunanin zata iya zuwa can wurinsu??" cike da damuwa Hajiya Maryam tace tana da abokan kasuwancinta acan saidai Farhar bata san su ba sai kuma abokanta da sukayi karatu tare suma ba kowanne Farha ta sani ba sai wata ƙawarta guda Hajiya Turai kuma ta kirata ta tambayi ko Farhar taje wurinta ta tabbatar mata da bata je ba,