Sashe 91
Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 7 min read
"Yanzu ni abunda nike gani in sun amince zasu zo Weekend d'in kar a wani ce za'a takura kai tunda nasan maza ne masu zuwa kuma ko gidan namu suka gani zasu fahimci irin k'arfin mu, yanzu bari in je d'aki in natsu sai in kira Yaya Mubarak d'in tunda shine mai kud'in gidan yana aiki kuma dama ko ba yanzu ba kullum cikin yin hidima yake sai mu tsara abunda ya kamata duk dai a taru a had'a k'arfi da karfe, ina ganin har fenti yakamata ayi ma gidan sannan tunda a parlon Baba za'a tarbe su sai a gyara shi sosae a canza kujerun ciki da duk abunda yakamata, gaskiya dole ma in je" ta k'arasa Maganar tana jinjina kai, a sanyaye Fauzy tace to banda gadon Baban za'a canza Aunty tace tana tunanin ba sai an canza dashi ba tunda a parlor ai za'a zauna,
"Amman in suka ce zasu kwana fa?" Fauzy ta fad'a fuska a d'an yamutse, shiru Aunty tayi alamar nazari can tace gaskiya bata tunanin hakan su fa manyan mutane basu kwana wuri irin haka in ma ta kama masu a Hotel suke sauka amman ko don k'ilan su buk'aci shiga yin alwala ko wani abu akwae buk'atar a canza d'in hatta toilet d'in ma a gyara shi abunda ke buk'atar canzawa a canza, kai Fauzy ta jinjina sai kuma tace ma Aunty Mareeyar akwae kud'i a account d'in ta sai a had'a dasu da sauri tace Yauwa to aikuwa zasu taimaka sosae tunda suna da d'an yawa tana rufe baki Fatuu tace itama bari ta tura mata gudunmawarta duk sai a had'a,
"A'a Zarah don Allah ba sai kinyi wata dawainiya ba tunda kema ai baki rasa uzurorin kud'i ko" d'an murmushi tayi tace "ai Aunty Mareeya shine yanzu uzurin ya taso ko, ko bamu zama yan'uwa bane?" da sauri ta girgiza kai "tabbas mun zama Zarah, tun tuni ma" yar dariyar jin dad'i Fauzy tayi, nan take ta turo ma Fauzy 300k lokacin data duba alert d'in gaba d'aya ta zaro ido baki bud'e ta d'ago ta kalli Fatun sai kuma ta juya ta kalli Aunty dake niyyar tambayarta minene ta rigata ta hanyar d'aga mata wayar tana nuna mata credit alert d'in, waro ido itama tayi ta hau girgiza kai "gaskiya Zarah kud'in nan sun yi yawa a rage don Allah hidindimun rayuwar nan da yawa daga wannan fa sai wannan" girgiza kai Fatuu tay tace Allah ko an maido mata itama sai ta sake turowa, ba yarda Aunty bata yi da ita ba amman tace Allah baza'a rage ba ai don tana da su ne ta bada kuma in tasan zata k'waru ai bazata bada har haka ba inda ma tana dasu sosae fin haka zata bada to don ta tura ma Baffan ta wasu ya k'ara jari sannan kuma an siya mata shanaye, gaba d'aya fuskokin su sun nuna damuwa tana dariya tace don Allah wai ba an zama d'aya bane kuma itama ai ba wahala tayi ta same su ba nan ta shiga fadi masu da bikinta ta samu kud'i sosae don ko Mahaifiyar Sameer d'in 500k ta tura mata banda wanda k'awayen Mom suka babbata mai dubu hamsin mai dubu d'ari, daga baya godiya suka shiga yi mata Fauzy ta rungumeta ta saka kuka tana fad'in bata san da wane baki zata mata godiya ba tabbas dama tunda ta fara ganinta a school taji tana kaunarta ashe ita d'in Alkhairi ce a gareta, murmushi kawai Fatun ke yi tana ce mata haba ba komai fa,
"In rungume ku to nima in yi kukan" Aunty ta fad'a ta kai hannu ta rungumo su gaba d'aya Fatuu ta saki dariya, bayan ta sake su sosae tayi ma Fatuu godiya da Addu'oi daga baya ta mik'e tace bari taje suyi magana da Yaya Mubarak d'in, har ta juya Fatuu ta kirata ta juyo fuskarta da murmushi ta tambayeta ya akai ta d'an yamutsa fuska tace Abincin data dafa take son ci, hannu Aunty ta kai ta ruk'e ha6a tace "wani aikin sharri sai ciki, yanzu ki kawo mana wannan had'addan Abincin amman namu tagajan tagajan kike son ci" gaba d'aya sukai dariya Fauzy tace wllh ta manta ne bata zubo mata ba tunda tazo ko ruwa ma bata kawo mata ba Aunty tace gaskiya bata kyauta ba wato ta dafi abincinta mai dad'i kuma ita ko ruwa bata kawo mata ba hakan ai ba Adalci bane, da sauri Fauzy ta saukko tana fad'in ayi hak'uri tasan tayi ba daidai ba bari ta kawo mata suka nufi k'opa tare da Aunty,
bayan taje Bedroom d'inta nan ta hau fad'i ma mijinta Abban su Hanif yadda sukai da Fatuu game da bayanin da Haisam yayi kan Sameer da yadda sukai da Mahaifinta harda kud'in da Fatun ta bada, sosae yaji dad'in dukkan bayanan dama jiya da daddare Aunty ke fad'i mashi yadda sukai da Baban su, godiyar kud'in da Fatuu ta bada yay da Addu'ar fatan Alkhairi, kiran yayan nasu ta shiga yi bayan ya d'aga sun gaisa yace mata ai gashi ma a gida yanzu Baban su ke fad'i mashi yadda sukai yanzu ma suna niyyar kiran su Mutanen da suka kira din ne tace to duk yadda sukai dasu sai ya sanar mata, har zata mashi sallama yace mata ta dai tabbatar da duk bayanan da aka bada kan shi gaskiya ne ko don kada aga yana da nasaba ayi abunda za'a zo ayi dana sani daga baya ba fata ake ba, halin Haisam ta shiga fad'i mashi harda yadda ya auri Fatuu shima duk da ba ajin auran shi bace ta kuma tabbatar mashi da yadda yake ruk'e da ita yanzu daga baya ma sai ta mik'a ma mijin nata wayar don ya k'ara mashi bayani yana d'an murmushi ya amsa, bayan sun gaisa a nutse ya shiga yi mashi bayanin gaskiya Haisam mutumin kirki ne tun daga kan mahaifin shi da dangin shi yace yana da yak'inin bazai fad'i abun da ba haka bane akan d'an uwan nashi, hamdala Yaya Mubarak yay yace dama haka suke son ji tunda bai kamata ba ace ba ai wani bincike ba akan shi saboda aure ba abun wasa bane bayan sun k'ara tattaunawa daga baya sukai sallama ya mik'a ma Aunty wayar, cigaba da tattaunawa kan abunda yakamata ayi sukai daga baya sukai sallama.
Bayan sallar Magrib Aunty ta shigo d'akin Fauzy lokacin Fatuu na zaune akan abun salla cikin washe baki ta sanar masu yanzu Yaya Mubarak ya kirata yana sanar da ita an kira wurin su Sameer din yadda aka fad'a yayi masu sun ce ranar Asabar zasu je Funtua har saida gaban Fauzy yay wani irin bugu jin abun dai da gaske ne gashi ko waya da Sameer d'in ma basu yi ba, sosae Fatuu tayi murnar jin hakan sai faman washe baki take haka Aunty Mareeya ma da alama ta manta da zancen rocket, kiran Mahaifiyar su tayi tace mata ga Zarah d'in dama suna gaisawa da ita ta wayar Fauzy, cikin girmamawa kaman ko yaushe Fatuu ta gaishe ta bayan ta amsa ta tambayi su gwaggo da mai gidan nata duk tace mata lafiyar lau nan ta hau yi mata godiya da Addu'oi Fatun na murmushi tace mata ai ba komai duk an zama d'aya tace hakane kam. Bayan sallar isha Tk ya kirata yace gashi nan kopar gida ya zo tace to dama a shirye take don sunyi waya da Haisam yace mata ga Tk d'in nan zuwa, hijab Fauzy ta saka suka fito a tare, a cikin parlon suka iske Aunty Mareeya tana serving mijinta Abinci da Hanif shida k'annan shi guda biyu sultan da iman, tana ganin su tace badai tafiya ba Fauzy tace eh ga Tk nan yazo shi zai maida ta, mik'ewa tay tana fad'in maimakon to ya shigo, gaisawa sukai da mijin Aunty d'in yana d'an murmushi ya amsa tare da yi mata godiyar abun Alkhairi daya ji itama murmushin take tace mashi ba komai, Bedroom Aunty ta nufa bada Jimawa ba ta fito ta yafo gyale Fatuu tay ma mijin nata sallama yace ta gaishe da maigidan ta, harda su Hanif suka mik'e don yi mata rakiya, har zasu fita daga parlon Aunty tace ma Fauzy to ina basket d'in Abincin da sauri tace au ta manta wllh ta koma don ta d'aukko su kuma suka fita.
"Amman in suka ce zasu kwana fa?" Fauzy ta fad'a fuska a d'an yamutse, shiru Aunty tayi alamar nazari can tace gaskiya bata tunanin hakan su fa manyan mutane basu kwana wuri irin haka in ma ta kama masu a Hotel suke sauka amman ko don k'ilan su buk'aci shiga yin alwala ko wani abu akwae buk'atar a canza d'in hatta toilet d'in ma a gyara shi abunda ke buk'atar canzawa a canza, kai Fauzy ta jinjina sai kuma tace ma Aunty Mareeyar akwae kud'i a account d'in ta sai a had'a dasu da sauri tace Yauwa to aikuwa zasu taimaka sosae tunda suna da d'an yawa tana rufe baki Fatuu tace itama bari ta tura mata gudunmawarta duk sai a had'a,
"A'a Zarah don Allah ba sai kinyi wata dawainiya ba tunda kema ai baki rasa uzurorin kud'i ko" d'an murmushi tayi tace "ai Aunty Mareeya shine yanzu uzurin ya taso ko, ko bamu zama yan'uwa bane?" da sauri ta girgiza kai "tabbas mun zama Zarah, tun tuni ma" yar dariyar jin dad'i Fauzy tayi, nan take ta turo ma Fauzy 300k lokacin data duba alert d'in gaba d'aya ta zaro ido baki bud'e ta d'ago ta kalli Fatun sai kuma ta juya ta kalli Aunty dake niyyar tambayarta minene ta rigata ta hanyar d'aga mata wayar tana nuna mata credit alert d'in, waro ido itama tayi ta hau girgiza kai "gaskiya Zarah kud'in nan sun yi yawa a rage don Allah hidindimun rayuwar nan da yawa daga wannan fa sai wannan" girgiza kai Fatuu tay tace Allah ko an maido mata itama sai ta sake turowa, ba yarda Aunty bata yi da ita ba amman tace Allah baza'a rage ba ai don tana da su ne ta bada kuma in tasan zata k'waru ai bazata bada har haka ba inda ma tana dasu sosae fin haka zata bada to don ta tura ma Baffan ta wasu ya k'ara jari sannan kuma an siya mata shanaye, gaba d'aya fuskokin su sun nuna damuwa tana dariya tace don Allah wai ba an zama d'aya bane kuma itama ai ba wahala tayi ta same su ba nan ta shiga fadi masu da bikinta ta samu kud'i sosae don ko Mahaifiyar Sameer d'in 500k ta tura mata banda wanda k'awayen Mom suka babbata mai dubu hamsin mai dubu d'ari, daga baya godiya suka shiga yi mata Fauzy ta rungumeta ta saka kuka tana fad'in bata san da wane baki zata mata godiya ba tabbas dama tunda ta fara ganinta a school taji tana kaunarta ashe ita d'in Alkhairi ce a gareta, murmushi kawai Fatun ke yi tana ce mata haba ba komai fa,
"In rungume ku to nima in yi kukan" Aunty ta fad'a ta kai hannu ta rungumo su gaba d'aya Fatuu ta saki dariya, bayan ta sake su sosae tayi ma Fatuu godiya da Addu'oi daga baya ta mik'e tace bari taje suyi magana da Yaya Mubarak d'in, har ta juya Fatuu ta kirata ta juyo fuskarta da murmushi ta tambayeta ya akai ta d'an yamutsa fuska tace Abincin data dafa take son ci, hannu Aunty ta kai ta ruk'e ha6a tace "wani aikin sharri sai ciki, yanzu ki kawo mana wannan had'addan Abincin amman namu tagajan tagajan kike son ci" gaba d'aya sukai dariya Fauzy tace wllh ta manta ne bata zubo mata ba tunda tazo ko ruwa ma bata kawo mata ba Aunty tace gaskiya bata kyauta ba wato ta dafi abincinta mai dad'i kuma ita ko ruwa bata kawo mata ba hakan ai ba Adalci bane, da sauri Fauzy ta saukko tana fad'in ayi hak'uri tasan tayi ba daidai ba bari ta kawo mata suka nufi k'opa tare da Aunty,
bayan taje Bedroom d'inta nan ta hau fad'i ma mijinta Abban su Hanif yadda sukai da Fatuu game da bayanin da Haisam yayi kan Sameer da yadda sukai da Mahaifinta harda kud'in da Fatun ta bada, sosae yaji dad'in dukkan bayanan dama jiya da daddare Aunty ke fad'i mashi yadda sukai da Baban su, godiyar kud'in da Fatuu ta bada yay da Addu'ar fatan Alkhairi, kiran yayan nasu ta shiga yi bayan ya d'aga sun gaisa yace mata ai gashi ma a gida yanzu Baban su ke fad'i mashi yadda sukai yanzu ma suna niyyar kiran su Mutanen da suka kira din ne tace to duk yadda sukai dasu sai ya sanar mata, har zata mashi sallama yace mata ta dai tabbatar da duk bayanan da aka bada kan shi gaskiya ne ko don kada aga yana da nasaba ayi abunda za'a zo ayi dana sani daga baya ba fata ake ba, halin Haisam ta shiga fad'i mashi harda yadda ya auri Fatuu shima duk da ba ajin auran shi bace ta kuma tabbatar mashi da yadda yake ruk'e da ita yanzu daga baya ma sai ta mik'a ma mijin nata wayar don ya k'ara mashi bayani yana d'an murmushi ya amsa, bayan sun gaisa a nutse ya shiga yi mashi bayanin gaskiya Haisam mutumin kirki ne tun daga kan mahaifin shi da dangin shi yace yana da yak'inin bazai fad'i abun da ba haka bane akan d'an uwan nashi, hamdala Yaya Mubarak yay yace dama haka suke son ji tunda bai kamata ba ace ba ai wani bincike ba akan shi saboda aure ba abun wasa bane bayan sun k'ara tattaunawa daga baya sukai sallama ya mik'a ma Aunty wayar, cigaba da tattaunawa kan abunda yakamata ayi sukai daga baya sukai sallama.
Bayan sallar Magrib Aunty ta shigo d'akin Fauzy lokacin Fatuu na zaune akan abun salla cikin washe baki ta sanar masu yanzu Yaya Mubarak ya kirata yana sanar da ita an kira wurin su Sameer din yadda aka fad'a yayi masu sun ce ranar Asabar zasu je Funtua har saida gaban Fauzy yay wani irin bugu jin abun dai da gaske ne gashi ko waya da Sameer d'in ma basu yi ba, sosae Fatuu tayi murnar jin hakan sai faman washe baki take haka Aunty Mareeya ma da alama ta manta da zancen rocket, kiran Mahaifiyar su tayi tace mata ga Zarah d'in dama suna gaisawa da ita ta wayar Fauzy, cikin girmamawa kaman ko yaushe Fatuu ta gaishe ta bayan ta amsa ta tambayi su gwaggo da mai gidan nata duk tace mata lafiyar lau nan ta hau yi mata godiya da Addu'oi Fatun na murmushi tace mata ai ba komai duk an zama d'aya tace hakane kam. Bayan sallar isha Tk ya kirata yace gashi nan kopar gida ya zo tace to dama a shirye take don sunyi waya da Haisam yace mata ga Tk d'in nan zuwa, hijab Fauzy ta saka suka fito a tare, a cikin parlon suka iske Aunty Mareeya tana serving mijinta Abinci da Hanif shida k'annan shi guda biyu sultan da iman, tana ganin su tace badai tafiya ba Fauzy tace eh ga Tk nan yazo shi zai maida ta, mik'ewa tay tana fad'in maimakon to ya shigo, gaisawa sukai da mijin Aunty d'in yana d'an murmushi ya amsa tare da yi mata godiyar abun Alkhairi daya ji itama murmushin take tace mashi ba komai, Bedroom Aunty ta nufa bada Jimawa ba ta fito ta yafo gyale Fatuu tay ma mijin nata sallama yace ta gaishe da maigidan ta, harda su Hanif suka mik'e don yi mata rakiya, har zasu fita daga parlon Aunty tace ma Fauzy to ina basket d'in Abincin da sauri tace au ta manta wllh ta koma don ta d'aukko su kuma suka fita.