← Book details Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 180 OF 211

Sashe 180

Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 6 min read

"No Farha, kawai dai ina ganin Soyayya tsakaninmu bazata yuwu ba tunda kinga muna da bambanci sosae kuma kince so kike muyi aure ni kuma yanzu ba yadda za'ai in yi aure saboda ban daɗe da fara yin karatu ba kinga ba aiki nike ba da zan iya auren ki" da yanayin damuwa yayi Maganar itama fuskarta a yamutse tace mashi ba wani bambancin dake tsakanin su tunda ai duk ɗaya suke a wurin Allah kuma ai ba dole sai ana aiki za'ayi aure ba tunda yana yin business lafiya lou zasu iya yin aure sai a faɗaɗa business ɗin, ganin dai da gaske take yasa shi bata haƙuri yace gara su ci gaba da ƙawancensu su bar Maganar soyayya da aure don abu ne da shi yasan ba mai yuwuwa bane a tsakanin su ba lalle gaba ɗaya a amince masu ba ba kamar shi za'a ga yayi ƙarami da yin aure, idanunta ne suka ciko da ƙwalla cikin karyayyar murya tace yanzu duk da yana da ikon cire mata damuwa shine zai watsa mata ƙasa a ido tunda take dashi tana jin wannan ce buƙata ta farko data zo mashi da ita amman shine bazai taimaketa ba ya amince mata kuma da yake cewa baza'a amince masu ba sai dai in basu nuna suna son junansu ba sannan Maganar yayi ƙarami ai tasan shekarunshi yana da shekaru 26 ɗin ne zai ce bai isa aure ba wasu ma basu kai shekarun shi ba suke yin aure wani ma Matar ta girme shi suke yin auren balle su da ya girmeta, duk tabi ta ruɗa shi ganin yadda take magana tana yin ƙwalla sai bata haƙuri yake tace ita ba wannan take so ba kawae ya amince mata don in yaƙi za'a mata auren dole ne kuma ita shi take so in bai aureta ba to zata mutu kowa ya huta, zo kaga ido a wurin ɗan fillo yaji zancen za'a mutu saboda shi a razane ya shiga roƙonta kan ta daina cewa haka yanzu ta ɗan bashi lokaci zai yi shawara tunda yanzu tazo mashi da Maganar yana buƙatar yayi shawara idanunta sharkaf da ƙwalla tace har tsawon wane lokaci zai yi shawarar yace bada daɗewa ba zai kirata tace shikenan tana jiran shi, tana yanke kiran hannun shi har rawa yake wurin kiran Fatuu saida ta yanke sai gashi ta kira suka gaisa ta tambayi mutanen gidan da karatun shi ya amsa mata tana jin yanayin muryarshi ta tambayeshi ya akai ne da damuwa yace mata akwae matsala ne da sauri ta tambayi miya faru nan ya shiga faɗi mata yadda sukai da Farha ita kanta ta jinjina abun tace mashi to ita dae a shawarce ya rabu da ita don ta tabbatar ba abu bane mai yuwuwa ƙarshenta rayuka ne zasu 6aci ba kamar yanzu da Mamanta take babba a da ma ba son talaka suke ba balle yanzu ita kanta Farhar don ta nuna ta canza ne amman ba ƙaunar talaka take ba, nan ta kwashe komai daya ta6a shiga tsakanin su ta faɗi mashi tace koda ace auren ya yuwu a tsakaninsu to bata tunanin zata mutunta yan'uwansu don ance mai hali baya barin halin shi don haka ya bata haƙuri kawae kada wani tsara kalamenta su ruɗe shi gara taga bai mata daidai ba akan abunda zai je ya dawo ya amsa mata da to sukai sallama, zaune yay jugum bayan sun gama yin wayar gaba ɗaya ya rasa mike mashi daɗi Maganar Fatuu ta kashe mashi jiki sosae, suna gama yin wayar Gwaggo Fatuu ta kira bayan sun gaisa ta kwashe komai ta faɗi mata itama sosae ta jinjina abun ta kuma goyi bayan abunda Fatun tace mashi tace gara haka zama lafiya yafi zama ɗan sarki, Kamalu na zaunen har aka kira Magrib ya tashi don yaje masallaci jikinshi duk yayi sanyi lakwas, tun akan hanyarsu ta zuwa Kawu Amadu ya lura da kamar akwae abunda ke damunshi ya tambayeshi amman sai yace mashi ba komai ya gaji ne Amadun yace mashi halan kuma yayi baccin yamma ya bashi amsa da eh yace shi yasa, bayan an gama sallar sun dawo suna niyyar tsayawa shago Gwaggo ta kira Amadu ta tambayi sun dawo daga salla ne yace mata eh gasu nan sun tsaya shago tace to su shigo shida Kamalun tana son ganin su yace to, a falonta suka isketa zaune suma duk suka nemi wuri suka zauna cikin kwantar da murya ta fara magana idonta akan Kamalu tace taji yadda sukai da Farha a wurin Fatuu tana son ya sani ba wai ana ƙoƙarin hana shi yin soyayya da ita bane kawae ana gudun matsala ne don duk abunda Fatun ta faɗa mashi gaskiya ne ya faru don haka kamar yadda sukai da ita ya bata haƙuri shi ya fi don ko ya amince mata mawuyacin abu ne a barta ta aure shi, kai Kamalun ya jinjina a sanyaye yace to zai yi yadda suka ce da alamun rashin fahimta kawu Amadu ya tambayi mike faruwa ne tsakaninshi da Farhar Gwaggo ta kwashe komai ta faɗi mashi, shima jinjina abun yay yace ina ai ba abu bane mai yuwuwa ma shi dama tunda yaga take takenta yasan da wuya bata ce tana son shi ba to gara ya bata haƙuri kawae don ko kowa ya amince mamarta yasan bazata ta6a yarda wai ta aure shi ba an auri mijin ɗiyarta tayi ma mutane tijara ina ga kuma yanzu ace ɗiyar tata za'a aura ai sai yaƙi tsakaninsu balle yanzu da ta zama wata a ƙasa ita kanta Farhar ai ba kanwar lasa bace kawai dai don suna shiri ne yasa yake ganin kamar bata da matsala, ɗan murmushi Gwaggo tayi tace ƙilan da gaske ta canza tunda tun kafin tasan Kamalun ta canza sai ai mata kyakkyawan zato Amadun yace to ko dai ita lafiya lou wannan Maman tata ba lafiya lou ba, haka suka dingi tattaunawa daga baya suka fito suka koma shago, bayan sallar isha yana shago sai ga kiran Farha saida ya fito daga shagon ya nufi gate ɗin shiga gida sannan yay picking, bayan ya ɗauka tace yay keeping nata tana ta jira kuma yace bada daɗewa ba zai kirata, haƙuri ya bata yace dama yana niyyar kiran nata bai gidane amman gashi nan zai je ɗaki sai suyi magana tace Ok, bayan ya shiga cikin ɗakin da yake zaune ya nufi katifa ya zauna saida yay ƙoƙarin daidaita natsuwarshi sannan ya fara mata magana ya nuna mata yayi magana da yan'uwan shi kanta gaskiya duk sun nuna ba abu bane da zai yuwu don haka yana bata haƙuri ba wai don bai sonta ba sai don ba'a goyi baya ba,
Chapter 180 · 0% Book details