Sashe 61
Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Washe gari da wuri akai gama Breakfast saboda masu tafiya kuma ranar aiki ce, Senator na cikin yin Breakfast jikin shi sanye da jallabiya yan'uwanshi da suka rage maza suka zo part d'in shi don su gaisa su kuma yi sallama wanda ya'yan yan'uwan mahaifinsu ne suma duk dattawa ne, bayan sun gaisa ya tambayi sunyi breakfast d'in suka ce eh yanzun nan suka gama, zancen wadda Nameer yake so yay masu yace bari ya gama sai suje suyi ma iyayen nata magana cikin nuna farinciki suka ce mashi to, bayan ya gama a tare suka mik'e har zasu tafi Senator ya dakata yace masu yana d'an zuwa duk suka tsaya suka ce to, hanyar Bedroom d'in shi ya nufa ya shige, bada jimawa ba ya fito ruk'e da babbar leda mai rubutu a jiki, d'aya cikin yan uwan nashi Alhaji Musa ne ya nufe shi da sauri wanda matsayin K'ani yake a wurin shi ya kai hannu ya amshi ledar suka nufi part d'in da su Ard'o suke, lokacin da suka shiga parlon ba kowa basu dad'e da gama yin Karin kumallo ba suna ciki suna shirin Tafiya, Alhaji Musa d'in ne yaje bakin k'opar tasu ya kwankwasa tare da yin sallama, Baban Altine ne yazo ya bud'e yana ganin shi ya k'arasa fitowa cikin washe baki ya gaishe dashi tare da d'an sunkuyawa bayan ya amsa ya sanar dashi tare suke da mai gidan suna son yin magana dasu ne yayi ma su magana, da sauri idanu a d'an waje ya tambayi lafiya dai ko yana murmushi yace mashi lafiya lou sai ma Alkhairi da sauri ya jinjina kai ya juya d'akin, ba'a d'au lokaci ba sai gasu sun fito su duka duk sun saka kaya da zasu tafi dasu Ardo yasha babbar riga da hula ha6ar kada, cikin parlon suka nufo su Senator na zaune suka nufe su da sauri, hannu suka basu suka shiga gaisawa don Senator ya hana su duk'awa k'asan da suke in zasu gaisa amman duk da haka in zasu gaisan dasu sai sun d'an sunkuya, bayan sun gama gaisawar yay masu nuni da su zauna duk suka nufi kujeru suka natsu, a nutse Alhaji Ibrahim ya fara magana yace dama abun Alheri ne suke tafe dashi duk suka jinjina kai, bayani yay masu d'an shi k'anin wanda ya auri yar wajen su ne shima ya ga yar'uwarta yana so to shine suka zo sake rok'on iri in ba'a yi mata miji ba, tun kafin ya rufe baki baban Altine ya hau girgiza kai bayan yayi shiru da sauri yace mashi ba'a yi mata miji ba wllh kuma koda an yi ma za'a warware a ba d'an wajen nasu ko don Mutuncin su a gare su, shi Baffan Fatun ma ya kasa magana tsananin mamaki had'i da farinciki ne suka lullube shi don kuwa yasan wadda ake Magana koma wacece d'iyar shi ce tunda da iya yaran shi su Aysha aka zo, shi Ard'o sam bai fahimci inda aka dosa ba tunda dama ba wani fahimtar hausar yake sosae ba cikin harshen fulatanci yake tambayar Baffan Altine abunda aka ce cike da farinciki ya hau sanar dashi, ai tun kafin ma ya k'arasa da sauri Ard'on har yana yin kaman zai fad'o daga kan kujera tsabar saurin yayi Magana Baffan Altine ya tare shi, cewa yay an ba yaron duka don haka yanzu ma sai a d'aura aure kawai, gaba d'aya murmushi su kai Senator yace masu yaron yana karatu ne yanzu kuma ba'a K'asar nan ba amman nan da shekara guda zai gama zuwa lokacin sai ayi masu Auren dama akwae Yayar shi da za'a ma Aure a lokacin sai a had'a su yanzu sun yi magana ne don asan da Maganar, Baban Altine ne ya k'ara yi ma Ardon bayani yadda zai fahimta sosae sai faman d'aga kai yake, Senator ne ya sake cewa yakamata a kira yaran aji ta bakin su don a tabbatar kafin a tsaida magana duk suka ce hakan yayi, kiran Nameer yayi a wayar shi bayan ya d'auka saida ya amsa gaisuwar da yay mashi sannan ya bashi umarnin ya iske shi a part d'in sannan ya kira itama yarinyar da yayi ma Hajiya Magana akan ta, bayan ya cire wayar ne daga kunnan shi ya kai hannu kan k'atuwar ledar da suka zo da ita ya d'an tura saitin su yace gashinan suyi amfani da su, Baban Altine ne ya taso ya d'auka har da duk'awa yana godiya haka Baffan Fatuu ma sai da ya d'an zamo daga kan kujera yay godiya Ard'o ma sosae ya hau yin godiya, after some minutes Nameer ya shigo jikin shi sanye da k'ananun kaya, amsa mashi sallamar da yayi sukai ya k'araso ciki kan shi a k'asa, daga gefen su Dad d'in shi ya zauna a k'asa duk idon su na akan shi, d'an d'ago da kai yay ya gaishe dasu Dad bayan sun amsa ya juya kan su Ard'o ya gaishe dasu cikin washe baki babban Altine ya amsa shi kuma Baffan su Fatun murmushi yake ya amsa, bai dad'e da shigowa ba Mino ta shigo da yar sallama jikinta sanye da Hijab duk suka kai idon su kan ta suna amsawa, kan ta a k'asa ta k'araso cikin parlon, a d'ayan bangaren ta zauna ya zamana suna facing juna da Nameer, gaishe dasu tay ba tare da ta d'ago kanta ba duk suka amsa, shiru suka d'an yi kafin Dad yay d'an gyaran murya idon shi akan Nameer yace mashi Hajiya ta fad'i mashi sak'on shi shine suke son ji daga gare shi da gaske yana son ta, shiru Nameer yay kan shi a k'asa gaba d'aya idanun su na akan shi, ganin yak'i magana yasa cikin d'an d'aga murya Dad yace,
"C'mon Ka bud'e baki kai mana magana my friend! baka ji nauyin wadda ka ba sak'on ba sai mu" duk murmushi akai k'asa k'asa Nameer yace Eh,
"Eh what?" da k'yar ya furta eh yana sonta ba tare da ya d'ago ba, "kuma zaka Aure ta?" kai ya d'aga kafin yace eh,
"Ka sani in muka riga muka gama magana ba zancen ka dawo ka ce ka canza ra'ayi" da sauri ya jinjina mashi kai, maida idon shi yay kan Mino itama ya tambayeta tay shiru bata ce komai ba, k'ara tambayar ta yay nan ma tak'i tace komai baffan Altine ne cikin d'aga murya da fulatanci yace mata bata ji ana magana bane still bata ce komai ba idon Baffan ta na a k'asa, Ardo ne yay yar tsawa Dad yace su rabu da ita hakan data yi ta nuna masu ita cikakkiyar bafullatana ce, Albarka ya saka masu duk aka amsa da Amin yace su tashi su je,
A tare suka mik'e dukkan su kan su na k'asa suka nufi hanyar fita daga part d'in su Dad suka cigaba da tattaunawa, suna fitowa bakin k'opar part d'in Nameer ya kai hannu ya kamo hannunta ta waro ido ya jata tana ta waige waigen kada wani ya gan su, bayan part d'in ya nufa da ita sannan ya sake ta suka bi juna da kallo fuskokin su d'auke da murmushi,
"Yanzu hankalin ki sai ya kwanta sosae kin zama tawa na zama naki" Nameer ya fad'a yana dariyar farinciki, itama dariyar take sosae take ganin abun kamar a mafarki daga fara soyayyar su har an yi Maganar aure ta wani bangaren dad'i ne cike da ranta,
"Yanzu ya za'ai Maganar karatun ki don ni gaskiya dana gama nan da one year in sha Allah za'a d'aura mana Aure tare da Yaya Laila" cikin tabbatar mata da hakan yay Maganar, shiru ta d'an yi sai kuma tace mashi to yayi duk yadda yake so, yana murmushi ya d'age mata gira "kenan k'in amince muyi aure ko baki gama Secondary d'in ba?" Kai ta jinjina mashi tace in dae zai barta taci gaba,
"in kuma ban son kici gaba da karatun fa?" Still da murmushi akan fuskarta ta d'an yarfa hannu tace mashi Shikenan zata hak'uri, wani k'ayataccen murmushi ya saki yace ashe haka take son shi ita dai murmushi kawae take,
"Ki sha kurumin ki zaki karatu har sai kin ce ya ishe ki, saidae gaskiya bana son a rink'a kalle man ke ya za'ai kenan?" Yar dariya tayi tace sai ta rink'a rufe Fuskar ta to, lumshe mata ido yay ya furta "that's what makes me love u more babe, duk abunda nike so kina so in sha Allahu zan yi bakin kokarina wurin saka ki farinciki bazaki ta6a yin dana sanin amince mani ba" jinjina mashi kai tay tana ta murmushi,
"Kema zaki man haka?" Da sauri ta d'aga mashi kai kafin ta furta "in sha Allah" yace Allah ubangiji ya basu iko ta amsa da Amin,
"Gaba d'aya ji nike inama ba sai nan da one year zamu zama ma'aurata ba don gaba d'aya kin mamaye heart ena" yar dariya tay sai kuma tace "ni kai ne heart d'in nawa" tana furta hakan tasa tafukan hannuwanta ta rufe fuska, sosae yaji dad'in Maganar sai zabga uban murmushin jin dad'i yake, hannu ya kai ya cire hannuwan nata suka zuba ma juna ido wani sabon son junan su ke ratsa zuciyoyin su, kasa jurewa Mino tay ta sadda idanun ta k'asa,
"I'm going to miss you" d'ago ido tay a hankali tace itama haka, yar Ajiyar zuciya yayi yace yaso ya canza mata waya amman bai samu yin hakan ba, tambayar ta yay tana da bank account ta girgiza mashi kai alamar a'a, d'an jimm yay kafin yace Shikenan zai tura ma Uncle d'inta sai ya canza mata wayar don su rink'a yin Vedio call lafiya lou suna rage kewar juna, ce mata yay itama yakamata ace tana da account d'in zai sa a bud'e mata don ya rink'a tura mata kud'in da zata rink'a yin hidindimun ta, tana ta kallon shi har ya gama sannan tace mashi ya bar shi ba sai ya rink'a tura mata ba tunda ana mata komai, tun kafin ta rufe baki ya d'an yi mata hararar love yace tun yanzu ta sani hakkin ta ya hau kan shi tana dariya tace ai ba'a d'aura auren ba shima dariyar yake yace eh ai an bashi ita ko.
"C'mon Ka bud'e baki kai mana magana my friend! baka ji nauyin wadda ka ba sak'on ba sai mu" duk murmushi akai k'asa k'asa Nameer yace Eh,
"Eh what?" da k'yar ya furta eh yana sonta ba tare da ya d'ago ba, "kuma zaka Aure ta?" kai ya d'aga kafin yace eh,
"Ka sani in muka riga muka gama magana ba zancen ka dawo ka ce ka canza ra'ayi" da sauri ya jinjina mashi kai, maida idon shi yay kan Mino itama ya tambayeta tay shiru bata ce komai ba, k'ara tambayar ta yay nan ma tak'i tace komai baffan Altine ne cikin d'aga murya da fulatanci yace mata bata ji ana magana bane still bata ce komai ba idon Baffan ta na a k'asa, Ardo ne yay yar tsawa Dad yace su rabu da ita hakan data yi ta nuna masu ita cikakkiyar bafullatana ce, Albarka ya saka masu duk aka amsa da Amin yace su tashi su je,
A tare suka mik'e dukkan su kan su na k'asa suka nufi hanyar fita daga part d'in su Dad suka cigaba da tattaunawa, suna fitowa bakin k'opar part d'in Nameer ya kai hannu ya kamo hannunta ta waro ido ya jata tana ta waige waigen kada wani ya gan su, bayan part d'in ya nufa da ita sannan ya sake ta suka bi juna da kallo fuskokin su d'auke da murmushi,
"Yanzu hankalin ki sai ya kwanta sosae kin zama tawa na zama naki" Nameer ya fad'a yana dariyar farinciki, itama dariyar take sosae take ganin abun kamar a mafarki daga fara soyayyar su har an yi Maganar aure ta wani bangaren dad'i ne cike da ranta,
"Yanzu ya za'ai Maganar karatun ki don ni gaskiya dana gama nan da one year in sha Allah za'a d'aura mana Aure tare da Yaya Laila" cikin tabbatar mata da hakan yay Maganar, shiru ta d'an yi sai kuma tace mashi to yayi duk yadda yake so, yana murmushi ya d'age mata gira "kenan k'in amince muyi aure ko baki gama Secondary d'in ba?" Kai ta jinjina mashi tace in dae zai barta taci gaba,
"in kuma ban son kici gaba da karatun fa?" Still da murmushi akan fuskarta ta d'an yarfa hannu tace mashi Shikenan zata hak'uri, wani k'ayataccen murmushi ya saki yace ashe haka take son shi ita dai murmushi kawae take,
"Ki sha kurumin ki zaki karatu har sai kin ce ya ishe ki, saidae gaskiya bana son a rink'a kalle man ke ya za'ai kenan?" Yar dariya tayi tace sai ta rink'a rufe Fuskar ta to, lumshe mata ido yay ya furta "that's what makes me love u more babe, duk abunda nike so kina so in sha Allahu zan yi bakin kokarina wurin saka ki farinciki bazaki ta6a yin dana sanin amince mani ba" jinjina mashi kai tay tana ta murmushi,
"Kema zaki man haka?" Da sauri ta d'aga mashi kai kafin ta furta "in sha Allah" yace Allah ubangiji ya basu iko ta amsa da Amin,
"Gaba d'aya ji nike inama ba sai nan da one year zamu zama ma'aurata ba don gaba d'aya kin mamaye heart ena" yar dariya tay sai kuma tace "ni kai ne heart d'in nawa" tana furta hakan tasa tafukan hannuwanta ta rufe fuska, sosae yaji dad'in Maganar sai zabga uban murmushin jin dad'i yake, hannu ya kai ya cire hannuwan nata suka zuba ma juna ido wani sabon son junan su ke ratsa zuciyoyin su, kasa jurewa Mino tay ta sadda idanun ta k'asa,
"I'm going to miss you" d'ago ido tay a hankali tace itama haka, yar Ajiyar zuciya yayi yace yaso ya canza mata waya amman bai samu yin hakan ba, tambayar ta yay tana da bank account ta girgiza mashi kai alamar a'a, d'an jimm yay kafin yace Shikenan zai tura ma Uncle d'inta sai ya canza mata wayar don su rink'a yin Vedio call lafiya lou suna rage kewar juna, ce mata yay itama yakamata ace tana da account d'in zai sa a bud'e mata don ya rink'a tura mata kud'in da zata rink'a yin hidindimun ta, tana ta kallon shi har ya gama sannan tace mashi ya bar shi ba sai ya rink'a tura mata ba tunda ana mata komai, tun kafin ta rufe baki ya d'an yi mata hararar love yace tun yanzu ta sani hakkin ta ya hau kan shi tana dariya tace ai ba'a d'aura auren ba shima dariyar yake yace eh ai an bashi ita ko.