Sashe 178
Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Alhamdulillah Ranar Asabar da Misalin ƙarfe sha biyu da rabi na rana Jama'a suka shaida ɗaurin auren Amadu da Haulat sai Khadija (Gwaggo) da Kawu Mani a masallacin gidan Hajiya su ango Kawu Amadu ansha babbar rigar farar shadda sai washe baki yake ganin abun yake kamar a mafarki, sosae mutane suka halarci ɗaurin auren har Nameer yazo da kuma Senator, misalin ƙarfe biyu bayan anyi sallar Azahar aka ɗaura auren Tukur da Asma'u wadda ake cema Husna a Masallacin G.r.a dake layout Senator ne ya kar6ar mashi auren sai fatan Allah yasa alkhairi yaba ma'auratan zaman Lafiya, Gidan Gwaggo ya cika da yan biki duk an sha anko baka jin bakin kowa sai Aunty Mareeya sai shegantaka suke ma Gwaggo har saida suka matsa mata ita da Fatuu sukai mata kwalliya sai ga amarya Gwaggo ta fito fess kai kace ba ita ba tasha leshi mai kyau gaba ɗaya duk sun cikata da kunya, bayan sallar La'asar jerin Motoci suka je daukko Amaryar Tk bayan an kawota aka ɗaukko Haulat abun sai san barka komai ya tafi daidai dangin Hajiya sun yi ma Tk kara tun daga kan yan Daura da yan nan Katsina duk sunzo har Hajiya Maryam ma tazo haka Fanan dasu Mom ɗin Haisam duk sun zo, ta bangaren Tk ɗinma danginshi duk sun zo, Washe gari da wuri akai Walima saboda masu tafiya su Hajiya Maryam da Mom har Nameer ranar zai koma Mino dai ta roƙi ya barta ta ƙara kwana biyu ya amince, a ranar da daddare angwaye suka shiga ɗakunan Amaren nasu sai fatan Allah yasa Albarka ya bada zuriya ɗayyiba.
Bayan sati guda da yin bikin su Fatuu suka koma lokacin Esha ta fara girma tubarkallah washe garin tafiyar su ranar Lahadi ango Kawu Mani yazo gidan harda akwatunan shi guda biyar na kaya da yayi ma Gwaggon da Kayan abinci sosae ta nuna jin daɗinta tayi mashi godiya, ta ɗauka zai tafi ne sai taga ba haka ba ashe zuwa yay shima wurin Amaryar tashi duk da ba haka taso ba taso ace sai bayan kaman wata guda da bikin su Amadu saidai ba yadda zatayi dole ta bashi haɗin kai suma suka shiga shan amarci sauƙin ta ma kowa da bangaren shi bawan Allah Kamalu an bar shi da tsaron shago sauƙin shi ma Farha na nan kuma yana zuwa Makaranta.
Bayan wata guda da bikin su Amadu aka ɗaura auren Ashiru wato gaye da Amaryarshi Jamila mai awara dama itace Hajiya ta haɗasu yanzu ta zama babbar budurwa har ma ta gama karatunta a Health technology Haisam ne ya ɗauki nauyin karatun da bikin ma shida Hajiya suka yi mata kayan ɗaki shima gayen sun bashi gudunmawa sosae Fatuu ma ta aiko mashi da tata gudunmawar kuɗin ta wurin Gwaggo sai fatan Allah yasa Albarka a cikin auren Amin.......
102
~_*✊💋BOSS LADIES WRITERS💋✊*_~
.......Zaman su Hajiya da Husnah matar Tk gwanin daɗi, sosae take mata biyayya dama kuma Tk ya jaddada mata irin muhimmancinta a wajen shi, haka ma Saude suna shiri da ita kusan tare ma suke yin aiyukan gidan Abinci ma wasu lokuttan tare suke ci da Hajiyar har Farha ma ba laifi tana shiri da ita da yake Husnar wayayya ce gata fara tana da kyau ba laifi da yake fulanin Gombe ce, ba don Tk ya shigo birni ba da wannan ta wuce ajin auren shi, A bangaren Haulat ma wannan ko ban faɗa ba ansan zata yi ma Gwaggo biyayya tamkar uwa da ɗiya suke zamansu haka aiyukan gidan ma tare suke da yake tun kafin a ɗaura Auranta da Kawu Mani ya nuna bai son taci gaba da aikin da take yi to tun bayan ma da aka ɗaura auran bata je wurin aikin ba yanzu ma shirin ajewa take, Haulat har ce mata tayi ta bari ta rinƙa gyara mata part ɗinta tana yin Abinci Gwaggon tace to ita ta zauna tayi mi, Auransu na yin wata biyu upper ɗin aikinsu Tk da Amadu ta fito gaba ɗaya sun samu aiki a bangaren Lab na Teaching hospital kowa yayi farinciki har gida Gwaggo da Haulat suka je yi ma Hajiya Godiya don ita tasa aka samar masu aikin.
Za6e ya taho wanda kuma na canza shuwagabanni ne ma'ana waɗanda ke akan mulki tenure ɗin su ce ta ƙarshe, daga cikin masu sauka harda mahaifin su Sameer sannan cikin yan takarar neman shugabancin ƙasar nan da suka fito a ƙarƙashin Jam'iya mai mulki harda Mahaifinsu Haisam wato Senator Ali Adamu wanda mutane suka tursasa mashi dole ya fito don shi ba so yake ba ciki harda shugaban ƙasan da zai sauka shi ya fidda matsayin ɗan takararshi, Bayan ansha gwagwarmayar zaben fidda gwani na jam'iyar mai mulki cikin sa'a Senator Ali ne ya lashe saura Babban za6e nan da wata ukku, cikin lokacin aka shiga gudanar da Campaign saƙo da lunguna na ƙasar nan, A Katsina gidan Hajiya na cikin wuraren da ake raba kayan Campaign su Tk da Amadu na cikin masu gudanar da Campaign saƙo da lunguna tun ma kafin ayi za6en mutane keta hasashen Senator Ali ne zai lashe don sosae yay farinjini wurin al'umma a kudu da arewa ko ina ya samu kar6uwa dama shugaban da zai sauka ba musulmi bane kuma sai ya fiddo Senator Alin matsayin ɗan takarar shi, a Masallatai ma ana ta mashi Addu'o'i kan in Alkairi ne Allah ya bashi ko ina sai faɗin kyawawan halayenshi ake ana cewa ba don kuɗi yake takara ba don da nashi kuɗin ma aiki yake ma Al'umma yana taimakon su talakaw, ana gab da yin Babban za6e su Fatuu suka zo don yin za6en suma anan Abuja suka sauka. Alhamdulillah ranar za6e tazo cikin lumana aka fara gudanar da zaben an zuba matakan tsaro ko ta ina, bayan an kammala aka shiga zaman jiran sakamako wanda sai dare aka bayyana, Allah dai ya amince Senator Ali ne wanda ya lashe kujerar shugabancin ƙasa zo kaga murna wurin mutane gaba ɗaya Social Media ta ɗauka cikin gari aka fara celebrations wani abun sai ma a Katsina ban tunanin Mutane zasu yi bacci ranar saboda tsabar murna, Bayan an bayyana sakamakon Hajiya ta kira shi don ta taya shi murna da fatan Alkhairi yana ɗaukar wayar kawai sai ya saka mata kuka wanda har cikin ranta taji shi ita kanta tasan ba son mulkin yake ba, rarrashin shi ta shiga yi tace yayi haƙuri ya rungumi mulkin tunda Allah ya bashi cikin muryar kuka ya amsa mata tare da roƙonta kan a tayashi da Addu'a tana murmushi tace wannan koda yaushe cikin yi mashi take yanzun kuma zata ƙara zage damtse yayi mata godiya ta shiga yi mashi Addu'o'in Allah ya dafa mashi ya kare shi yanata amsawa da Amin daga baya sukai sallama, haka akaita kiraye kirayen wayoyi ana taya yan'uwa murna. Bayan wasu watanni aka gabatar da inauguration Ceremony a Eagle Square dake Abuja wuri ya cika maƙil da Jama'a an sha anko mai tambarin jam'iya da hoton President Ali da Vice ɗin shi wanda christian ne su Mom da Aunty an sha gwaggwaro suna gefen mai girma shugaban ƙasa harda Hajiya ma tana a wurin dasu Hajiya Maryam harda Hajiya Zainab da maigidanta dasu Sameer da iyalan sabon shugaban ƙasan su Haisam harda su Fatuu da Mino duk suna a wurin Laila ma tazo da Mijinta tare da kyakkyawar Babynta data haifa wadda taci sunan surukarta wato Safeeya suna ce mata Mimi, su Gwaggo dai suna a gida suna kallo a Tv, bayan Senator Ali yayi rantsuwar karbar office aka tabbatar dashi a matsayin cikakken shugaban ƙasa, daga nan rakiyar tsohon shugaban ƙasa aka tafi bakin city gate ana dawowa aka raka President Ali Adamu Aso rock presidential Villa abun na Allah ne sai ga su Fatuu da Mino yan fillo a Villa, daga cikin waɗanda suka lashe kujerun yan Majalissar tarayya harda Alhaji Lawal mahaifin Khalid, bayan sati ɗaya da komawar su Mom Villa su Haisam suka tafi wannan karon harda Nameer da Mino don zaici gaba da karatun shi itama Mino har ya samar mata makaranta zata yi Nursing a can,
Bayan tafiyarsu Fatuu da sati biyu matar Tk ta haiho san6aleliyar budurwa mai kama da mamanta Hajiya na jin Haihuwar ta dawo don tunda aka rantsar da shugaban ƙasa sun ƙi bari ta dawo, zo kaga murna a wurin Tk an zama baba tun a ranar ya raɗa mata sunan Hajiya wato Hauwa'u suka yanke zasu rinƙa kiranta da Jiddah Hajiya tace a rinƙa kiranta da sunanta kada a wani 6oye mata suna shikenan ita ta samu ƙawa kuma takwara, Haulat ma a lokacin ciki ne da ita wurin wata shidda da yake Husnar ta rigata samu, tunda Mino taji batun Haihuwar matar Tk gaba ɗaya ta ƙara shiga damuwa da rashin Haihuwarta har Asibiti Nameer ɗin yasa suka je ganin yadda ta damu aka tabbatar masu da lafiyar su lou nan ya shiga rarrashinta yana nuna mata lokacin haihuwar ne bai yi ba kuma shi koda bata haihu ba bazai damu ba zasu yi zaman su a haka ko kuma su amshi yaro a wurin Adda Fatunta tunda ita tana haihuwa akai akai yasan bazata hana su ba wannan Maganar tashi tasa ta ɗan kwantar da hankalinta ta maida hankali kan karatunta, ganin Mino na karatu yasa Fatuu tayi ma Haisam magana kan in zai yuwu itama tana son taci gaba da karatun Medicine yace mata shima yana son hakan saidai matsalan shekarun suna da yawa gashi kuma suna gab da komawa Nigeria amman in tana so ita sai ta zauna anan taci gaba da Karatun ko kuma ta bari in suka koma Nigeria sai tayi Karatun a India inda Fanan tayi shekarun karatun basu kai na nan America ba ta amince da hakan, tuni Farha ta gama bautar ƙasanta amman taƙi komawa gida tay zaune abunta gidan Hajiya kuma ba saboda kowa bane face Kamalu.
Bayan sati guda da yin bikin su Fatuu suka koma lokacin Esha ta fara girma tubarkallah washe garin tafiyar su ranar Lahadi ango Kawu Mani yazo gidan harda akwatunan shi guda biyar na kaya da yayi ma Gwaggon da Kayan abinci sosae ta nuna jin daɗinta tayi mashi godiya, ta ɗauka zai tafi ne sai taga ba haka ba ashe zuwa yay shima wurin Amaryar tashi duk da ba haka taso ba taso ace sai bayan kaman wata guda da bikin su Amadu saidai ba yadda zatayi dole ta bashi haɗin kai suma suka shiga shan amarci sauƙin ta ma kowa da bangaren shi bawan Allah Kamalu an bar shi da tsaron shago sauƙin shi ma Farha na nan kuma yana zuwa Makaranta.
Bayan wata guda da bikin su Amadu aka ɗaura auren Ashiru wato gaye da Amaryarshi Jamila mai awara dama itace Hajiya ta haɗasu yanzu ta zama babbar budurwa har ma ta gama karatunta a Health technology Haisam ne ya ɗauki nauyin karatun da bikin ma shida Hajiya suka yi mata kayan ɗaki shima gayen sun bashi gudunmawa sosae Fatuu ma ta aiko mashi da tata gudunmawar kuɗin ta wurin Gwaggo sai fatan Allah yasa Albarka a cikin auren Amin.......
102
~_*✊💋BOSS LADIES WRITERS💋✊*_~
.......Zaman su Hajiya da Husnah matar Tk gwanin daɗi, sosae take mata biyayya dama kuma Tk ya jaddada mata irin muhimmancinta a wajen shi, haka ma Saude suna shiri da ita kusan tare ma suke yin aiyukan gidan Abinci ma wasu lokuttan tare suke ci da Hajiyar har Farha ma ba laifi tana shiri da ita da yake Husnar wayayya ce gata fara tana da kyau ba laifi da yake fulanin Gombe ce, ba don Tk ya shigo birni ba da wannan ta wuce ajin auren shi, A bangaren Haulat ma wannan ko ban faɗa ba ansan zata yi ma Gwaggo biyayya tamkar uwa da ɗiya suke zamansu haka aiyukan gidan ma tare suke da yake tun kafin a ɗaura Auranta da Kawu Mani ya nuna bai son taci gaba da aikin da take yi to tun bayan ma da aka ɗaura auran bata je wurin aikin ba yanzu ma shirin ajewa take, Haulat har ce mata tayi ta bari ta rinƙa gyara mata part ɗinta tana yin Abinci Gwaggon tace to ita ta zauna tayi mi, Auransu na yin wata biyu upper ɗin aikinsu Tk da Amadu ta fito gaba ɗaya sun samu aiki a bangaren Lab na Teaching hospital kowa yayi farinciki har gida Gwaggo da Haulat suka je yi ma Hajiya Godiya don ita tasa aka samar masu aikin.
Za6e ya taho wanda kuma na canza shuwagabanni ne ma'ana waɗanda ke akan mulki tenure ɗin su ce ta ƙarshe, daga cikin masu sauka harda mahaifin su Sameer sannan cikin yan takarar neman shugabancin ƙasar nan da suka fito a ƙarƙashin Jam'iya mai mulki harda Mahaifinsu Haisam wato Senator Ali Adamu wanda mutane suka tursasa mashi dole ya fito don shi ba so yake ba ciki harda shugaban ƙasan da zai sauka shi ya fidda matsayin ɗan takararshi, Bayan ansha gwagwarmayar zaben fidda gwani na jam'iyar mai mulki cikin sa'a Senator Ali ne ya lashe saura Babban za6e nan da wata ukku, cikin lokacin aka shiga gudanar da Campaign saƙo da lunguna na ƙasar nan, A Katsina gidan Hajiya na cikin wuraren da ake raba kayan Campaign su Tk da Amadu na cikin masu gudanar da Campaign saƙo da lunguna tun ma kafin ayi za6en mutane keta hasashen Senator Ali ne zai lashe don sosae yay farinjini wurin al'umma a kudu da arewa ko ina ya samu kar6uwa dama shugaban da zai sauka ba musulmi bane kuma sai ya fiddo Senator Alin matsayin ɗan takarar shi, a Masallatai ma ana ta mashi Addu'o'i kan in Alkairi ne Allah ya bashi ko ina sai faɗin kyawawan halayenshi ake ana cewa ba don kuɗi yake takara ba don da nashi kuɗin ma aiki yake ma Al'umma yana taimakon su talakaw, ana gab da yin Babban za6e su Fatuu suka zo don yin za6en suma anan Abuja suka sauka. Alhamdulillah ranar za6e tazo cikin lumana aka fara gudanar da zaben an zuba matakan tsaro ko ta ina, bayan an kammala aka shiga zaman jiran sakamako wanda sai dare aka bayyana, Allah dai ya amince Senator Ali ne wanda ya lashe kujerar shugabancin ƙasa zo kaga murna wurin mutane gaba ɗaya Social Media ta ɗauka cikin gari aka fara celebrations wani abun sai ma a Katsina ban tunanin Mutane zasu yi bacci ranar saboda tsabar murna, Bayan an bayyana sakamakon Hajiya ta kira shi don ta taya shi murna da fatan Alkhairi yana ɗaukar wayar kawai sai ya saka mata kuka wanda har cikin ranta taji shi ita kanta tasan ba son mulkin yake ba, rarrashin shi ta shiga yi tace yayi haƙuri ya rungumi mulkin tunda Allah ya bashi cikin muryar kuka ya amsa mata tare da roƙonta kan a tayashi da Addu'a tana murmushi tace wannan koda yaushe cikin yi mashi take yanzun kuma zata ƙara zage damtse yayi mata godiya ta shiga yi mashi Addu'o'in Allah ya dafa mashi ya kare shi yanata amsawa da Amin daga baya sukai sallama, haka akaita kiraye kirayen wayoyi ana taya yan'uwa murna. Bayan wasu watanni aka gabatar da inauguration Ceremony a Eagle Square dake Abuja wuri ya cika maƙil da Jama'a an sha anko mai tambarin jam'iya da hoton President Ali da Vice ɗin shi wanda christian ne su Mom da Aunty an sha gwaggwaro suna gefen mai girma shugaban ƙasa harda Hajiya ma tana a wurin dasu Hajiya Maryam harda Hajiya Zainab da maigidanta dasu Sameer da iyalan sabon shugaban ƙasan su Haisam harda su Fatuu da Mino duk suna a wurin Laila ma tazo da Mijinta tare da kyakkyawar Babynta data haifa wadda taci sunan surukarta wato Safeeya suna ce mata Mimi, su Gwaggo dai suna a gida suna kallo a Tv, bayan Senator Ali yayi rantsuwar karbar office aka tabbatar dashi a matsayin cikakken shugaban ƙasa, daga nan rakiyar tsohon shugaban ƙasa aka tafi bakin city gate ana dawowa aka raka President Ali Adamu Aso rock presidential Villa abun na Allah ne sai ga su Fatuu da Mino yan fillo a Villa, daga cikin waɗanda suka lashe kujerun yan Majalissar tarayya harda Alhaji Lawal mahaifin Khalid, bayan sati ɗaya da komawar su Mom Villa su Haisam suka tafi wannan karon harda Nameer da Mino don zaici gaba da karatun shi itama Mino har ya samar mata makaranta zata yi Nursing a can,
Bayan tafiyarsu Fatuu da sati biyu matar Tk ta haiho san6aleliyar budurwa mai kama da mamanta Hajiya na jin Haihuwar ta dawo don tunda aka rantsar da shugaban ƙasa sun ƙi bari ta dawo, zo kaga murna a wurin Tk an zama baba tun a ranar ya raɗa mata sunan Hajiya wato Hauwa'u suka yanke zasu rinƙa kiranta da Jiddah Hajiya tace a rinƙa kiranta da sunanta kada a wani 6oye mata suna shikenan ita ta samu ƙawa kuma takwara, Haulat ma a lokacin ciki ne da ita wurin wata shidda da yake Husnar ta rigata samu, tunda Mino taji batun Haihuwar matar Tk gaba ɗaya ta ƙara shiga damuwa da rashin Haihuwarta har Asibiti Nameer ɗin yasa suka je ganin yadda ta damu aka tabbatar masu da lafiyar su lou nan ya shiga rarrashinta yana nuna mata lokacin haihuwar ne bai yi ba kuma shi koda bata haihu ba bazai damu ba zasu yi zaman su a haka ko kuma su amshi yaro a wurin Adda Fatunta tunda ita tana haihuwa akai akai yasan bazata hana su ba wannan Maganar tashi tasa ta ɗan kwantar da hankalinta ta maida hankali kan karatunta, ganin Mino na karatu yasa Fatuu tayi ma Haisam magana kan in zai yuwu itama tana son taci gaba da karatun Medicine yace mata shima yana son hakan saidai matsalan shekarun suna da yawa gashi kuma suna gab da komawa Nigeria amman in tana so ita sai ta zauna anan taci gaba da Karatun ko kuma ta bari in suka koma Nigeria sai tayi Karatun a India inda Fanan tayi shekarun karatun basu kai na nan America ba ta amince da hakan, tuni Farha ta gama bautar ƙasanta amman taƙi komawa gida tay zaune abunta gidan Hajiya kuma ba saboda kowa bane face Kamalu.