Sashe 146
Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Bayan sun baro Asibitin tun akan hanya Fanan ta shiga kiran yan Nigeria su Hajiya da Mom ta sanar masu harda Gwaggo ma kowa yay mamakin jin samun cikin daga baya duk sukai Addu'oin Allah ya inganta ya raba lafiya. Sosae Fanan ke kulawa da Fatuu bayan da suka san da cikin haka su twins ma in dae tana gida bata je aiki ba ita ke duk wata ɗawainiya dasu dama tana kulawa dasu sosae yanzu sai ta k'ara don komai ita ke masu kama daga yin wanka shirya su basu Abinci yi masu wasa da sauransu haka Haisam ma in yana a gidan tare dashi ake masu komai koda Fatuu tayi yunƙurin yi masu wani abu sai suce ta bashshi ta huta duk da jikin nata da Sauk'i sosae iyakar ta shayar dasu sai kuma in suna zaune tare dasu ta d'auke su har tayi masu wasa, k'arshe ma Haisam cewa yay yakamata a samo masu nanny Saboda in basu nan ba sai ta rink'a wahalar kulawa dasu ba amma sai ta nuna mashi ba sai an samo ba tunda ba wani ciwo take ba zata iya wannan amman ya nuna ta bari dai a samo ganin hakan yake so yasa ta amince amman tace to ya bari tunda sun kusa tafiya biki in suka dawo sai a samu ya amince da hakan.
A kwana a tashi ba wuya a wurin Ubangiji, bikin su Nameer nata matsowa har ya rage saura sati ukku lokacin watan Fatuu biyu da sati guda a Us, a yadda sukai da Haisam in ya rage saura Sati biyu zata tafi shi kuma sai ana saura sati d'aya zasu taho shi da Fanan, gudunmawar miliyan biyu ya bata yace in basu isa ba tayi mashi magana cike da nuna farinciki ta nuna mashi sun isa har ma sun yi yawa, a yadda sukai da gwaggo bayan ta kirata kan Maganar kayan ɗaki ce mata tayi tana ganin kawai za'a siya mata ne ready made har ma tayi ma Aunty Mareeya magana kan hakan tace in an tashi siya akwae inda zata kai su suna da kaya masu kyau wanda za'a siya ma Minon, Fatuu taji dad'in jin hakan gaba d'aya gudunmawar da Haisam ya bata ta tura ma gwaggo tace saura tata in tazo Gwaggon tace wannan uban kuɗi haka da ɗanta ya bada anya basu yi yawa ba Fatuu na yar dariya tace mata a haka ma cewa yay in basu isa ba tayi magana ya ƙara da sauri gwaggo tace don Allah kada ta ƙara tambayar shi ko Naira wannan ai Kusan ma shi zai mata kayan ɗakin, tambayarta Fatuu tayi kamar ya za'a mata kayan gwaggo tace wai da ita a tunaninta ayi mata saitin gado da kujeru masu kyau wanda da an gani ansan masu kud'i ne tunda Baffan su ma sunyi Magana kan kayan ɗakin ta nuna mashi ya turo kuɗi kawai a siya sai duk a haɗa a siya mata, cewa Fatuu tay gaskiya kamata yay ayi mata komai set biyu kujerun da gadon don tasan gidan da za'a kaita babba ne alabashshi ko sai a siya set ɗaya masu kuɗi sosae sai ɗayan koda wanda basu kai su kuɗi ba Gwaggon tace to hakan ma bari in aka harhaɗa kuɗin sai aga kaman ya za'a siya mata don itama tana son a yi mata kaya sosae tunda ita ba'a yi mata komai ba Fatun tace komai kenan sai tazo sai suje a siya in sha Allah ba abunda zai gagara bane, itama Gwaggon tace in sha Allah nan take faɗi mata Hajiya tayi mata magana kan inda za'a ɗaura aure sun roƙi alfarmar in ba takura a ɗaura a nan Katsina sai a haɗa da na Laila a ɗaura gaba ɗaya anan sai a tura Mota can Adamawa ta ɗaukko masu zuwa ɗaurin auren nan don in akace ayi acan sannan ayi na Laila a Abuja za'a takura mutane don zirga zirgar zata yi yawa to ta kira Baffansu kan hakan shima yayi magana da yan'uwanshi duk sun amince da hakan shi Arɗo ma ance ba lalle yazo ba don bai jin daɗi Fatuu ta tambayi abunda ke damun shi tace mata kawai harda tsufa wai jikin nashi ne bai jin daɗin shi, fatan Allah ya bashi lafiya Fatuu tayi kafin suyi sallama Gwaggo ta tambayi ina Y'ay'anta Fatun tace gasu can wurin Aunty Fanan wai tafiya take koya masu, yar dariya gwaggo tayi tace da wuri haka Fatun tace eh wai daga taga sun fara tsayuwa shine ta fara koya masu Gwaggo na dariya tace ina ruwan ɗiyarta tana dai kula da yaran sosae Fatun tace sosae don yanzu har aiki take tafiya dasu ta bada su wurin raino a can har makaranta aka so saka su amman ta hana wai ai a wurin rainon ana koya masu abunda ake koyawa a Makarantar, da alamun mamaki gwaggo tace "wace irin Makaranta kuma yaran da basu wuce wata bakwae ba" yar dariya Fatuu tayi tace mata su nan haka suke yi kamar wurin raino ne to sai a rinƙa nuna masu abubuwa don su taso sun sani gwaggon tace ta gane aikuwa bari itama tazo ta koma Makaranta ko ta ƙara sanin abubuwa kada suzo su ƙureta harda ma turanci zata koyo, Fatuu nata Dariya itama gwaggon Dariyar take daga baya ta tambayeta ya jikin nata ta bata amsa da Alhamdulillah tace badai ta laulayi sosae ko Fatun tace mata eh ai maganin da take sha kullum yana hana ta yin amai ko tashin zuciya lafiya lau take cin Abinci saidai wani lokacin tana jin kasala taita kwanciya sai kuma ciwon kai da take yi wani lokacin shima, Addu'ar Allah ya inganta ya sauketa lafiya gwaggon tayi Fatuu na murmushi tace "Amin ya rabbi, Allah ya amsa gwaggota mahaifiyata, ina tsananin son ki da dukkan zuciyata" wani irin murmushin daɗi gwaggo tayi itama tace "nima ina ƙaunar ki autata Fateema, ina roƙon Allah ya ƙara ma rayuwar ki albarka data zuriyar ki ya jiƙan Mahaifiyar ki" wani irin lumshe ido Fatuu tayi nan da nan idanunta suka ciko da kwalla don a lokacin nan koda yaushe Mahaifiyarta na a ranta sosae take jin maraicinta tana jin inama ace tana raye rayuwarta tayi albarka haka, jin tayi shiru yasa gwaggo kiran sunanta ta amsa a hankali tana jin yanayin muryar tata ta gane kuka take, itama zuciyarta karyewa tayi abubuwa suka fara mata yawo a rai tay ƙarfin halin ce ma Fatuu ta daina Kuka tayi mata Addu'a in sha Allahu ta dace a sanyaye ta amsa da Allah yasa, kafin suyi sallama gwaggon tace in kusa Fanan take ta bata su gaisa tace to, bayan ta kai ma ta a Nursery ta sanar mata ga gwaggo zasu gaisa cike da nuna jin daɗi ta amsa cikin washe baki suka gaisa gwaggo tace ai an faɗi mata tana nan tana ta aikin koya tafiya Fanan d'in tay dariya tace eh so take su iya kafin su zo biki yadda in suka zo zasu je ko ina da ƙafafun su gwaggon tace lallai kam akwae aiki yanzu nan da sati guda kenan take son su iya tafiyar tana ta dariya tace eh itama gwaggon dariyar take tace to Allah ya taimaka ya bada sa'a ta amsa da Amin kafin suyi sallama harda kara ma Adam wayar wai yace mata Hello sai gashi yace ɗin cike da jin daɗi gwaggon ta shiga yi mashi magana da hausa tana tambayar yadda suke shida ɗan'uwan shi yay zuru yana zaro ido Fanan da Fatuu sai yar dariya suke ganin yadda yay ganin sunata dariya yasa shima yin dariyar gefen kumatun shi duk suka lotsa Madarar kyau abun sai dai ace tubarkalla, amsar wayar Fanan tay gwaggo tace ko basu yi masu magana da Hausa ne tace a'a suna yi masu Momynsu ma harda Fulatanci tana masu magana haka Dad d'in su ma yana masu larabci zasu taso suna jin yare hudu Gwaggo tace Masha Allah Allah yay masu albarka da sauri ta amsa da Amin da zasu yi sallama Fanan ɗin harda cewa "We love you so much granny" gwaggo na murmushi da hausa tace "nima ina son ku Y'ayana, Allah ya ƙara ma rayuwar ku albarka ya ƙara haɗa kan ku ya kauda idon maƙiya da mahassada ya kare ku daga dukkan sharri" cike da jin daɗi Fanan ta amsa harda lumshe ido daga baya ta ba Fatuu wayar don suyi sallama.
A kwana a tashi ba wuya a wurin Ubangiji, bikin su Nameer nata matsowa har ya rage saura sati ukku lokacin watan Fatuu biyu da sati guda a Us, a yadda sukai da Haisam in ya rage saura Sati biyu zata tafi shi kuma sai ana saura sati d'aya zasu taho shi da Fanan, gudunmawar miliyan biyu ya bata yace in basu isa ba tayi mashi magana cike da nuna farinciki ta nuna mashi sun isa har ma sun yi yawa, a yadda sukai da gwaggo bayan ta kirata kan Maganar kayan ɗaki ce mata tayi tana ganin kawai za'a siya mata ne ready made har ma tayi ma Aunty Mareeya magana kan hakan tace in an tashi siya akwae inda zata kai su suna da kaya masu kyau wanda za'a siya ma Minon, Fatuu taji dad'in jin hakan gaba d'aya gudunmawar da Haisam ya bata ta tura ma gwaggo tace saura tata in tazo Gwaggon tace wannan uban kuɗi haka da ɗanta ya bada anya basu yi yawa ba Fatuu na yar dariya tace mata a haka ma cewa yay in basu isa ba tayi magana ya ƙara da sauri gwaggo tace don Allah kada ta ƙara tambayar shi ko Naira wannan ai Kusan ma shi zai mata kayan ɗakin, tambayarta Fatuu tayi kamar ya za'a mata kayan gwaggo tace wai da ita a tunaninta ayi mata saitin gado da kujeru masu kyau wanda da an gani ansan masu kud'i ne tunda Baffan su ma sunyi Magana kan kayan ɗakin ta nuna mashi ya turo kuɗi kawai a siya sai duk a haɗa a siya mata, cewa Fatuu tay gaskiya kamata yay ayi mata komai set biyu kujerun da gadon don tasan gidan da za'a kaita babba ne alabashshi ko sai a siya set ɗaya masu kuɗi sosae sai ɗayan koda wanda basu kai su kuɗi ba Gwaggon tace to hakan ma bari in aka harhaɗa kuɗin sai aga kaman ya za'a siya mata don itama tana son a yi mata kaya sosae tunda ita ba'a yi mata komai ba Fatun tace komai kenan sai tazo sai suje a siya in sha Allah ba abunda zai gagara bane, itama Gwaggon tace in sha Allah nan take faɗi mata Hajiya tayi mata magana kan inda za'a ɗaura aure sun roƙi alfarmar in ba takura a ɗaura a nan Katsina sai a haɗa da na Laila a ɗaura gaba ɗaya anan sai a tura Mota can Adamawa ta ɗaukko masu zuwa ɗaurin auren nan don in akace ayi acan sannan ayi na Laila a Abuja za'a takura mutane don zirga zirgar zata yi yawa to ta kira Baffansu kan hakan shima yayi magana da yan'uwanshi duk sun amince da hakan shi Arɗo ma ance ba lalle yazo ba don bai jin daɗi Fatuu ta tambayi abunda ke damun shi tace mata kawai harda tsufa wai jikin nashi ne bai jin daɗin shi, fatan Allah ya bashi lafiya Fatuu tayi kafin suyi sallama Gwaggo ta tambayi ina Y'ay'anta Fatun tace gasu can wurin Aunty Fanan wai tafiya take koya masu, yar dariya gwaggo tayi tace da wuri haka Fatun tace eh wai daga taga sun fara tsayuwa shine ta fara koya masu Gwaggo na dariya tace ina ruwan ɗiyarta tana dai kula da yaran sosae Fatun tace sosae don yanzu har aiki take tafiya dasu ta bada su wurin raino a can har makaranta aka so saka su amman ta hana wai ai a wurin rainon ana koya masu abunda ake koyawa a Makarantar, da alamun mamaki gwaggo tace "wace irin Makaranta kuma yaran da basu wuce wata bakwae ba" yar dariya Fatuu tayi tace mata su nan haka suke yi kamar wurin raino ne to sai a rinƙa nuna masu abubuwa don su taso sun sani gwaggon tace ta gane aikuwa bari itama tazo ta koma Makaranta ko ta ƙara sanin abubuwa kada suzo su ƙureta harda ma turanci zata koyo, Fatuu nata Dariya itama gwaggon Dariyar take daga baya ta tambayeta ya jikin nata ta bata amsa da Alhamdulillah tace badai ta laulayi sosae ko Fatun tace mata eh ai maganin da take sha kullum yana hana ta yin amai ko tashin zuciya lafiya lau take cin Abinci saidai wani lokacin tana jin kasala taita kwanciya sai kuma ciwon kai da take yi wani lokacin shima, Addu'ar Allah ya inganta ya sauketa lafiya gwaggon tayi Fatuu na murmushi tace "Amin ya rabbi, Allah ya amsa gwaggota mahaifiyata, ina tsananin son ki da dukkan zuciyata" wani irin murmushin daɗi gwaggo tayi itama tace "nima ina ƙaunar ki autata Fateema, ina roƙon Allah ya ƙara ma rayuwar ki albarka data zuriyar ki ya jiƙan Mahaifiyar ki" wani irin lumshe ido Fatuu tayi nan da nan idanunta suka ciko da kwalla don a lokacin nan koda yaushe Mahaifiyarta na a ranta sosae take jin maraicinta tana jin inama ace tana raye rayuwarta tayi albarka haka, jin tayi shiru yasa gwaggo kiran sunanta ta amsa a hankali tana jin yanayin muryar tata ta gane kuka take, itama zuciyarta karyewa tayi abubuwa suka fara mata yawo a rai tay ƙarfin halin ce ma Fatuu ta daina Kuka tayi mata Addu'a in sha Allahu ta dace a sanyaye ta amsa da Allah yasa, kafin suyi sallama gwaggon tace in kusa Fanan take ta bata su gaisa tace to, bayan ta kai ma ta a Nursery ta sanar mata ga gwaggo zasu gaisa cike da nuna jin daɗi ta amsa cikin washe baki suka gaisa gwaggo tace ai an faɗi mata tana nan tana ta aikin koya tafiya Fanan d'in tay dariya tace eh so take su iya kafin su zo biki yadda in suka zo zasu je ko ina da ƙafafun su gwaggon tace lallai kam akwae aiki yanzu nan da sati guda kenan take son su iya tafiyar tana ta dariya tace eh itama gwaggon dariyar take tace to Allah ya taimaka ya bada sa'a ta amsa da Amin kafin suyi sallama harda kara ma Adam wayar wai yace mata Hello sai gashi yace ɗin cike da jin daɗi gwaggon ta shiga yi mashi magana da hausa tana tambayar yadda suke shida ɗan'uwan shi yay zuru yana zaro ido Fanan da Fatuu sai yar dariya suke ganin yadda yay ganin sunata dariya yasa shima yin dariyar gefen kumatun shi duk suka lotsa Madarar kyau abun sai dai ace tubarkalla, amsar wayar Fanan tay gwaggo tace ko basu yi masu magana da Hausa ne tace a'a suna yi masu Momynsu ma harda Fulatanci tana masu magana haka Dad d'in su ma yana masu larabci zasu taso suna jin yare hudu Gwaggo tace Masha Allah Allah yay masu albarka da sauri ta amsa da Amin da zasu yi sallama Fanan ɗin harda cewa "We love you so much granny" gwaggo na murmushi da hausa tace "nima ina son ku Y'ayana, Allah ya ƙara ma rayuwar ku albarka ya ƙara haɗa kan ku ya kauda idon maƙiya da mahassada ya kare ku daga dukkan sharri" cike da jin daɗi Fanan ta amsa harda lumshe ido daga baya ta ba Fatuu wayar don suyi sallama.