Sashe 142
Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 4 min read
Ana gama bikin Fauzy aka tsaida lokacin da za'a yi nasu Nameer da Aunty Laila nan da wata ukku lokacin sun gama duk wani abu daya danganci karatun su, Fatuu bata koma Katsina ba dama hada karatu ke zaunar da ita can yanzu kuma ta gama k'arshe ma Haisam yanke tafiya da ita Us yay ta shiga yin shiri, ta bangaren Amarya Fauzy ma itama barin K'asar zasu yi bayan bikin da sati d'aya don har anyi mata passport, ana saura kwana biyu su tafi ranar laraba suka zo Abuja zo kaga murna wurin Fatuu su Mom ma sun yi farinciki da zuwansu suka tarbi Fauzy hannu bibbiyu, bayan sun ke6e da Fatuu a part d'in su ne ta shiga yaba canzawar da tayi cikin d'an lokaci har tana fad'in lalle Sameer ya iya tarairaiya Fauzy dai sai dariya take itama tace ma Fatun ai itace za'a ce ta canza don gaba d'aya yanzu ta koma kalar hajiyoyi haka dai sukai ta hirar nishad'i tsakanin su, anan suka wuni sai k'arfe biyar na yamma suka tafi Fauzy harda ce ma Fatuu in taje Us d'in zata sa Sameer ya kawota wurinta. Ranar Friday Jirginsu ya tashi zuwa England sai fatan a sauka lafiya. Washe gari Asabar Haisam da Fatuu suka tafi Katsina don yin sallama dasu Gwaggo ta kuma d'aukko kayan da take son tafiya dasu, har gidan Aunty Mareeya taje dama tasa tayi mata tanadin kayan gyara ta amso suka yi bankwana haka gidansu Haulat ma taje sunyi bankwana harda abun Arzik'in da ta saba tayi mata, washe gari Lahadi wuraren Azahar suka komo Abuja ta ci gaba da yin shiri don gobe in Allah ya kaimu suma jirginsu zai tashi zuwa Us, da yamma bayan anyi La'asar suka tafi inda za'a mata k'unshi da gyaran kai, Washe gari da Safe sukai bankwana wad'anda ke a gidan sukai masu rakiya zuwa Airport Jidderh kaman zata yi kuka wai zata yi missing yaranta Abie da Grandpa kaman yadda suke ce masu Mom na dariya tace koda su basu tafi ba ai itama tafiyar zata yi Dubai ta barsu ko tunda a cikin satin zata tafi itama. Tuni jirginsu Fatuu ya d'aga sai Fatan a sauka lafiya Fanan na can tana shirya masu kyakkyawar tarba sai faman farinciki take yaranta su Twins zasu zo gareta.
Satin su Fauzy d'aya da zuwa lokacin tuni ta warke suna ta shan Amarci na gaske har yanzu ko ruwa bata ta6a dafawa ba bayan sunyi aure don anan d'in ma akwai mai aiki namiji da dama shi yake ma Sameer d'in Abinci da gyaran gida, koda tayi mashi magana kan ya sallame shi ta rink'a yi sai cewa yayi ba buk'atar sai tayi Abinci a marairaice ta nuna mashi ita dai tana son ta rink'a mashi girkin sai yace to ba yanzu ba, saidai ta ci ta sha ta ji da Sameer d'in, Washe gari ya kama Asabar ta kira Aunty lokacin bayan Azahar ne Sameer ya fita, Aunty na kwance tana bacci kiran ya shigo, saida ta kusa katsewa sannan ta farka ta duba tana ganin Fauzy ce ta saki murmushi tare da yin picking, bayan sun gaisa ta tambayi yadda suke ta bata amsa daga haka tay shiru, Aunty ta fahimci kaman akwae abunda take son fadi hakan yasa ta ce mata ya akai ne, ai kamar tana jira cikin murya kamar zata yi kuka tace "gaskiya Aunty wllh akwae Matsala" jin haka yasa Aunty Mareeya yunk'urin tashi zaune tana fad'in "Matsala kuma!, Allah ya rabamu da ita" bayan ta zauna sosae da alamun d'an tashin hankali tace mata wace matsala ce,
Shiru tay kaman bazata yi magana ba saida Aunty ta k'ara tambayarta tace bazata fad'i mata ba ko so take hankalinta ya tashi ne sannan tace "Aunty kwanaki ba cewa kikai in dai matsalata yace yana sona ba ke zaki sa shi ya rink'a fad'i man hakan kaman cin Abincin shi safe da rana da dare ba" da sauri Aunty tace "eh hakane, bai fad'i maki hakanne?" Da sauri tace "a'a yana yi amman fa....Ke ba wai kina nufin zai rink'a ce man hakan ba?" ta canza Maganar zuwa tambaya Auntyn tace mata eh mana haka take nufi,
Satin su Fauzy d'aya da zuwa lokacin tuni ta warke suna ta shan Amarci na gaske har yanzu ko ruwa bata ta6a dafawa ba bayan sunyi aure don anan d'in ma akwai mai aiki namiji da dama shi yake ma Sameer d'in Abinci da gyaran gida, koda tayi mashi magana kan ya sallame shi ta rink'a yi sai cewa yayi ba buk'atar sai tayi Abinci a marairaice ta nuna mashi ita dai tana son ta rink'a mashi girkin sai yace to ba yanzu ba, saidai ta ci ta sha ta ji da Sameer d'in, Washe gari ya kama Asabar ta kira Aunty lokacin bayan Azahar ne Sameer ya fita, Aunty na kwance tana bacci kiran ya shigo, saida ta kusa katsewa sannan ta farka ta duba tana ganin Fauzy ce ta saki murmushi tare da yin picking, bayan sun gaisa ta tambayi yadda suke ta bata amsa daga haka tay shiru, Aunty ta fahimci kaman akwae abunda take son fadi hakan yasa ta ce mata ya akai ne, ai kamar tana jira cikin murya kamar zata yi kuka tace "gaskiya Aunty wllh akwae Matsala" jin haka yasa Aunty Mareeya yunk'urin tashi zaune tana fad'in "Matsala kuma!, Allah ya rabamu da ita" bayan ta zauna sosae da alamun d'an tashin hankali tace mata wace matsala ce,
Shiru tay kaman bazata yi magana ba saida Aunty ta k'ara tambayarta tace bazata fad'i mata ba ko so take hankalinta ya tashi ne sannan tace "Aunty kwanaki ba cewa kikai in dai matsalata yace yana sona ba ke zaki sa shi ya rink'a fad'i man hakan kaman cin Abincin shi safe da rana da dare ba" da sauri Aunty tace "eh hakane, bai fad'i maki hakanne?" Da sauri tace "a'a yana yi amman fa....Ke ba wai kina nufin zai rink'a ce man hakan ba?" ta canza Maganar zuwa tambaya Auntyn tace mata eh mana haka take nufi,