← Book details Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 79 OF 211

Sashe 79

Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read

A bud'e kopar parlon take, lokacin da suka shiga wani irin k'amshi mai dad'i had'e da sanyin Ac ne suka tarbe su, parlon tsab da shi yasha gyara a wurin Saude, saman L-shape suka zauna wani irin farinciki Fatuu ke ji ganin ta a parlonta sosae tay missing part d'in nata, cire veil d'inta tay ta aje gefe Fauzy ta kalli kanta tace ba dai ta son kitso Fatun ta d'an yatsina baki tace wllh kitso takura mata yake, Fauzy tace harda don yana da yawa ne gashin ga kuma tsawo, hannu takai ta dafa Shoulder d'in Mino tace "Amaryar Nameer Ali Zakee ya Angon naki halan ana ta shan love?" dariya Mino tay sai kuma ta mik'a mata wayar hannunta wadda Samsung ce, bayan ta amsa Jujjuya ta tay tana k'are mata kallo kafin tace "Amman dai tayi kyau wllh, itace Wayar da aka Siya maki d'in" tay Maganar idonta akan Mino,

d'aga mata kai tay "eh, 300k ya turo sai Kawu Amadu ya siyo man, rannan ma ya k'ara turo man 200k" d'an waro ido Fatuu tay tace "Lalle Nameer ba K'aramin ji yake da ke ba, shi da yake d'alibi yake turo maki kud'i haka, koda yake yi mashi komai ake gara shima ya fara hidiman iyalin shi" duk sukai dariya,

"K'awata ke kuma ya ake ciki tsakanin ki da Sameer ince ko an samu cigaba kun fara shan love ku ma?" Yar dariya Fauzy tay kawai ba tare data ce komai ba, hannu Fatuu ta kai ta d'an bugi shoulder d'inta tace don Allah ta fad'i mata ya ake ciki,

"To ni mi zance maki ai duk abunda ake ciki kin sani, har yanzu yadda kika sani muke muna dai gaisawa yaji ya nake shikenan" d'an jinjina kai Fatuu tay "ba komai ai anyi mai wuyar tunda kunsan juna duk ya gama nuk'u nuk'un shi zai fito ya bayyana abunda ke ran shi ne ai sannu bata hana zuwa zamu yi ta zuba mashi ido har muga gudun ruwan shi" Fauzy na dariya tace haka Aunty Mareeya ke cewa,

"Allah sarki Aunty Mareeyata itama nayi missing d'inta Sosae wllh" Fatuu ta fad'a tana murmushi, Fauzy tace "kinsan kuwa da tare da ita zamu zo Airport don har ta shirya kawai sai tayi bak'uwa amma tace in maki sannu da zuwa sai tazo har gida" Fatun tace zama ta kirata kuma zata je har gidan ba sai ta zo ba. Sai da aka kira sallar Magrib sannan suka tashi suka nufin Bedroom, Fatuu ce ta fara yo Alwala sannan Fauzy ma ta shiga, ganin har zasu kabbara Mino na zaune yasa Fatuu dakatawa tace mata ita bazata tashi tayi sallar bane tay mata murmushi kawai, tambayarta tay bata yi ne ta d'aga mata kai Fatun ta d'an ta6e baki ta kabbara, suna gama sallar Saude ta zo ta sanar dasu ga Abinci can ta kawo kan table da sauri Fatuu ta mik'e daga kan prayer mat tana fad'in "Allah yay maki Albarka Aunty Saude kamar kinsan yunwa nike ji wllh" duk sukai dariya, bayan sun cire hijabs da sukai sallar gaba d'aya suka nufi parlon. Bayan sun yi sallar isha Fauzy ta mik'e tana fad'in bari ta tafi dare yayi Fatuu tace ta tsaya ta kwana mana,

"Kwana kuma?" Fauzyn ta fad'a tana yar dariya, Fatun tace eh,
"a'a gida zan tafi abu dai ana gari d'aya miye na in kwana kuma"

Fatuu tace to ai wanda take mawa dai baya nan kuma Mino ma anan zata kwana, shiru Fauzyn tay Fatuu ta k'ara cewa "Ke Allah ma sai kin kwana, dama bakuyi man kwanan Amarya ba to shi zaki biya ni" gaba d'aya suka sa dariya,

"To ai dama yanzu Kusan so ake a kashe kwanan gidan Amarya in an kaita wasu garuruwan ma dama ba'a yi don haka ba sai na biya ba" kafewa Fatuu tay kan ta kwana tace to ai bata tambayi Aunty Mareeya ba, hannu Fatuu ta kai ta d'aukko wayarta tana fad'in abu mai sauk'i in don wannan ne bari ta tambaya ma da kanta, tana fara ringing Aunty ta d'auka,

"Yar gidana ta kaina an dawo lafiya" tana murmushi ta amsa mata da lafiya lau,

"To ya jiki jikin?" Amsa mata tayi da Alhamdulillah, tace "anata laulayi kenan halan ma har ya fito?" k'asa k'asa ta bata amsa da eh,

"ma sha Allah, Allah ya inganta mana, ai naso in zo tarbar ki wllh sai nayi bak'uwa" tace haka Fauzy ta fad'i mata ai ba komai, tambayarta tay ya mijinta yana can K'asar turawa ko tace mata eh tace to Allah ya maido shi lafiya, bayan ta amsa tace mata dama so take ta roketa don Allah Fauzy zata kwana anan, da sauri Aunty tace "kai haba ba komai Zarah ta kwana, nan gaba ma kad'an ai sai kin fini iko da ita in ta zama Matar d'an uwan mijin ki d'an Governor don ma d'an bantan uban izza ta hana ya fito ya bayyana da yanzu k'ilan Maganar aure ake tunda da gani son ta yake wllh ba don haka ba yaushe zata samu ma ya rink'a kula ta" dariya Fatuu tay tace haka Fauzy ta fad'a mata har yanzu yak'i bayyanawa, a k'ufule Aunty tace "k'yale shi yayi ya gama ai ina nan ina jiran shi ya shigo hannu sai ya rabu da wannan cutar miskilancin don shi sai yama fi mijin ki magantuwa" dariya sosae Fatuu ke yi bayan ta tsagaita tace to shima na Mino a had'a da shi da sauri tace "ahhh anya Zarah, shi ai kinga baida irin cutar su ta miskilanci bawan Allah bakin shi a sake yake adai kamanta don in akai mashi irin nasu ba wuya zai zare" wata uwar dariya Fatuu ta kyalkyace da ita har Fauzy na fad'in ta dai bi a hankali kar tasa Babyn su ya fito, bayan sun gama wayar tay mata godiya suna yin sallama da sauri Fauzy tace bari tayi mata magana, bayan ta bata wayar a d'okance tay ma Aunty Mareeyar Albishir d'in Motar da aka Siya ma Fatuu, wata uwar gud'a ta rangad'a tace taba Fatuu wayar,

"Da kyau yar gidana, Wllh na taya ki murna Allah yasa Alkhairi ya tsare ya kuma raba lafiya, Wannan in dai za'a rink'a bamu kyautar Mota haka ai duk shekara sai mun haifa masa Baby" dariya kawai Fatuu ke yi tace mata sai tazo d'ani Fatun tace ai suna nan zuwa gobe da Motar a nuna mata tace to Allah ya kaimu tana jiran su, bayan sun gama wayar Mino ta kira Yadikko ta sanar mata zancen Motar sosae tay farinciki tasa aka ba Fatuu wayar ta taya ta murna da Addu'oi daga jin muryarta ba K'aramin farinciki take ba, tambayarta Fatun tay baffan su tace bai kaiga dawowa ba amman da ya shigo zata sana'ar mashi suka cigaba da yin wayar ta tambayi ya suka dawo da lafiyar Fatun duk ta amsa mata daga baya sukai sallama tana ta masu Addu'oi, bayan ta aje wayar mik'ewa tay har lokacin rigar da ta dawo da ita ce tace ma su Fauzy bari ta shiga tay wanka suka ce to kowannan su na latsa wayar shi, daga baya Mino ma ta mik'e tace bari taje gida ta canzo kaya Fauzy tace to bari ta rakata suka tafi tare,

After some minutes ta fito d'aure da towel a k'irjinta ganin ba su Fauzy a cikin d'akin yasata yin tunanin ko sun tafi parlor suyi kallo, shiryawa ta shiga yi cikin silky kayan bacci riga da wando blue bayan ta gama saka kayan ta feshe jikinta da turare, tana cikin gyara gashinta wayarta dake a saman side drawer ta fara ringing ta juya ta nufeta, saida ta zauna a bakin gado sannan ta kai hannu ta d'auko, ganin mai kiran nata yasa ta saki k'ayataccen murmushi dama da suna Airport a Abuja sun yi waya da shi, idasa hayewa tay saman gadon sannan tayi picking, tana d'auka taji yace suyi Vedio call tace to, yana zaune a cikin Office d'in shi jikinshi sanye da blue suit shirt d'in ciki fara ce sai bak'in bow tie sosae kayan sukai fitting d'in shi sumar shi a gyare luff, murmushi suka shiga sakar ma juna kafin ta gaishe da shi ya amsa yay mata sun dawo lafiya tace lafiya lou, tambayar ta Hajiya yay tace tana part d'inta su sun dawo nasu part d'in da Fauzy da kuma Mino ya jinjina mata kai still da murmushi a fuskokin su,

"What are u doing?" Ya tambaya idanunshi a d'an lumshe ta bashi amsa da wanka tayi yanzu ta gama shiryawa ya kira, shiru yay yana ta kallonta can ta tura mashi baki ya d'age gira "What?" A shagwabe tace "shine don kasan Mota d'in nan tana da kud'i sosae kak'i fad'a man ko" shiru yay yanata murmushi tace yayi Magana mana, tambayarta yay waya fad'i mata mai kud'i ce tace ita ta gane data ganta,

"nayi laifi kenan?" ya k'ara d'age gira, a shagwabe tace "a'a, kawai dai naga akwai wasu hidindimun bai kamata ka siyan man mai tsada ba sosae" yana murmushi yace "anything for you Baby ko banda halin abu indae kina so zan yi bakin k'ok'arina ki mallake shi wannan kuma ina da halin shi ne in ma fin shi kike so zan siya maki" wani kalan murmushin dad'i tayi ta lumshe ido irin yadda yake yi bayan ta bud'e a tare suka sa dariya,
Chapter 79 · 0% Book details