← Book details Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 170 OF 211

Sashe 170

Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Washe gari bayan sallar La'asar sai ga Abbas yazo tare da wasu Mutane bayan sun gaisa da Amadu ya tambayeshi Gwaggo na nan ne yace mashi eh, juyawa yay wurin Motar mutanen da suka zo tare su biyu yace masu yana zuwa suka furta Ok ya juyo ya nufi gidan, a bakin ƙopar zauren ciki ya tsaya yana sallama Gwaggo ta leƙo daga cikin falo tana amsawa tana ganin shine ta washe baki tana faɗin "ɗana Abbas ashe kai ne ka shigo mana" yana murmushi ya nufo falon Gwaggon ta koma ciki, bayan ya shiga a kujera ya zauna suka gaisa ta tambayi su Abdul yace mata duk suna lafiya kafin yace mata yaji abun murna na auren Amadu Allah ya sanya alkhairi tana fara'a ta amsa da Amin, ce mata yay dama yazo tare da injiniyoyi zasu duba gidan da alamun rashin fahimta Gwaggon tace gida kuma ganin yadda tayi Maganar yasa yace mata basu yi Magana da Haisam bane akan aikin da za'ayi a gidan da sauri ta girgiza kai tace gaskiya basu yi Magana ba sai dai ko Amadu, yar dariya Abbas yayi yace ina ruwan H,Zakee nan ya shiga yi mata bayanin aiki za'a ma gidan don har ma anyi cinikin gidan dake makwabtaka dasu Haisam ɗin ya siya za'a haɗe da wannan ayi sabon gini, zaro ido Gwaggo tayi baki buɗe take kallon shi a ɗan ruɗe tace "anya dai ɗana Abbas haka maganar nan take" yana dariya yace mata tabbas haka take ƙilan da Amadu sukai maganar, cike da mamaki tace anya ai daya faɗi mata amman bari ta kira shi taji, wayarta ta ɗaukko ta shiga kiran nashi bayan ya ɗaga tace mashi ya shigo yanzun tana son ganinshi, bada daɗewa ba ya shigo da sallama ya nufi kujera ya zauna yace mata gashi, tambayar shi tayi ko sunyi maganar za'ayi aikin gidanan da ɗanta Haisam da alamun rashin fahimta ya girgiza mata kai alamar a'a kafin ya faɗi mata yadda sukai dashi game da gidansu Umar da lambobin daya tura mashi sai kuma zuwan da Babansu Umar yayi cike da farinciki ya bayyana mashi sunyi waya da shi yace yana buƙatar siyan gidan da yake ciki shi kuma zai siya mashi wani ya zauna, Abbas na murmushi yace to ai su ya siya ma gidan za'a haɗe da wannan a maida shi babban gini shi ya ɗaura ma kan aikin shine ma yazo da injiniyoyi don su fara duba gidajen, gaba ɗaya Gwaggo da Amadu idanunsu a waje suke kawu Amadu ya kai hannu ya rufe baki alamar Al'ajabi da alama mamaki ya kashe masu bakuna can da tsananin mamaki kawu Amadu yace "Wai Yaya Abbas yanzu kana nufin saboda mu ya siya gidan su Umar ɗin kuma har ya siya masu suma gida?" kai Abbas ya ɗaga mashi yace eh a yadda sukai za'a haɗe sai ai babban Flat a fidda ma Gwaggo part ɗinta sai shima Amadun a fidda mashi nashi da zai zauna da iyalinshi harda ma 6angaren baƙi, nannauyar ajiyar zuciya Gwaggo ta sauke ta shiga girgiza kai da alamun damuwa tace "Amman gaskiya ɗana Abbas wannan hidiman tayi yawa sosae ace ya siya masu gida sannan ya siya wanda suke ciki kuma a haɗe da wannan a fara sabon gini yadda gini kede cin kuɗi ai gaskiya abun yayi yawa nidai da za'a bi ta tawa don Allah ya barshi in ma dole so yake yayi to a gyara wannan namun kawai ni sai in koma can ɗayan ɗakin shi kuma Amadun sai su ɗauki dakina da nan falon za'a ma iya ƙara girman falon tunda ga ɗan sauran wuri nan daga gefe har banɗaki ma za'a iya yi masu a ƙuryar lafiya lau wannan ma zai ishe mu" fuskarta ɗauke da damuwa tayi maganar Abbas na dariya yace "to Gwaggon mu waya ƙi cigaba tunda shi yayi niyya yana da halin yi ne karki wani damu tunda daya san zai takura da bazai fara cewa zai yi ba, a yadda ma ya faɗi man dama yana ta son a canza ginin gidan to yadda yake son a maida gidan bazai isa ba kuma yasan kun riga kun saba da unguwar bazaku ji daɗi ba in ya yi maku ginin wani wuri Hajiya ma yasan bazata so ku rabu ba shine yanzu yay tunanin yin hakan harma anyi cinikin gidan ya biya shi kuma wanda aka siya ma gidan dama can yanada rabo a wurin shi ne, yanzu dai na bar mutane a waje zan iya masu magana su shigo?" duk tayi sukuku da ita ta ɗaga mashi kai alamar eh ya miƙe yana dariya yana faɗin karta wani damu abun farinciki ne don haka tayi farinciki kawai ta ɗan yi murmushi ya juya kan Amadu da yayi duruduru yace ya taso yaje gidan su Umar ɗin yaga in mai gidan na nan yace za'a shigo a duba yace to tare da miƙewa suka fita, Gwaggo dai tayi zuru tana ta jinjina abun a ranta tasan dole gidan su Umar ɗin yayi kuɗi don yafi nasu girma ga gida kuma da aka siyan masu sannan azo a dasa gini, Bayan duk sun gama dubawa Abbas yace ma Gwaggo za'a kawo hotunan gidaje sai su za6a tace to kawai sukai sallama, zaune sukai falon Gwaggo ta kasa yin magana sai Amadu dake ta faman jinjina abun yana faɗin to wai hakanan ya yanke yi masu ginin ko kuwa dai yaji batun gyaran gidan saboda aurenshi shine zai yi masu, wannan Maganar da yayi yasa Gwaggo ta ɗaukko wayarta ta shiga kiran Fatuu, bayan ta yanke Fatun ta kira suka gaisa nan take tambayar ta wai sunyi maganar gyaran gida da tace mata tana son ayi kafin bikin Amadu da Haisam ne tace mata a'a kawae dai ta sanar mashi zancen shine ya tambayi yaushe za'a saka rana ta fadi mashi yadda sukai da ita na ba yanzu ba sai an yi gyaran gidan Gwaggon ta sauke ajiyar zuciya, da sauri ta tambayeta miya faru ne nan ta kwashe komai ta faɗi mata ita kanta Fatun tayi mamaki sosae ido waje ta shiga jinjina Maganar aikin tace gaskiya hidiman tayi yawa sosae Gwaggon tace wllh itama duk ta damu Fatun tace bari tayi mashi magana gaskiya in ma aikin yake son yi masu to a gyara gidan nasu kawai Gwaggo tace itama abunda tace kenan to Abbas yace ai har ya riga ya siya gidan kuma shi Baban su Umar yanzu in aka hana yana iya ganin anyi mashi baƙin ciki, tana cikin yin Maganar Amadu ya miƙa hannu ta bashi wayar bayan sun gaisa da Fatun yace mata kawai a kyaleshi ai mashi godiya yanzu ko anyi mashi magana kan ya bari sun san dai ba fasawa zai yi ba, a sanyaye tace shikenan sukai sallama,

Bayan sun gama yin wayar Haisam ta shiga kira da yake su safiya ce yana wurin aiki, bayan yayi picking tace mashi tana son suyi vedio call ya furta Ok, yana zaune a Office ɗin shi jikinshi sanye da baƙaƙen suit fuskar shi sai annuri take, fuska a tur6une ta gaishe dashi yana ɗan murmushi ya amsa ya gane laifi yayi mata daga yanayin face ɗinta, daga gaisuwar tayi shiru tana ta tura baki, lumshe mata ido yay ya furta "ya akai ne My Baby?" wani kallo tayi mashi a marairaice tace taji abunda yayi amman gaskiya hidiman yayi yawa in aikin za'ayi to ayi iya gidansu basai ya kashe uban kuɗi ba haka, murmushi kawai yake ganin har yanzu halinta na rashin son ya kashe kuɗi sosae na nan, ganin bai ce komai ba ta tura baki tace bazai yi magana ba,

"Yanzu nayi laifi don zan ma Family ena abu?" ya tambaya tare da ɗage mata gira, kaman zatayi kuka tace "a'a ni bance kayi laifi ba Amman gaskiya kashe kuɗin zai yi yawa" sigh yay still murmushi yake yace "bazai yi yawa ba akwae kuɗin Baby so don't worry" yamutsa fuska tayi tace to in suka ƙare fa har saida yayi yar dariya ganin taƙi ta girma har yanzu tana behaving kamar da yarintarta duk da yasan yanzun ma ba wani girma tayi ba tunda yanzu take 20yrs, yana yar dariya yace mata bazasu ƙare ba saboda yana dasu da yawa akwae Dollars ya tara cike da tsokana yayi Maganar ta zaro ido ya ɗage mata gira,

murmushi tay tace "baka tsoron insa ai kidnapping ɗinka kana faɗi man ka tara Dollars" dariya yay har haƙoranshi suka bayyana yace ai tuntuni ta riga tayi kidnapping ɗin Heart ɗinshi yanzu ko duka kuɗin dake gareshi tace ya bata zai tattara ya bata, wani kallo tayi mashi tace is he serious ya jinjina mata kai yace amman zai fidda na aikin gidan da za'ai don kar aga yayi magana biyu sai kuma wanda zai ciyar dasu kafin ya sake tara wasu kada Allah ya kama shi ya barsu da yunwa, wani irin kallon ƙauna ta shiga bin shi da shi shima kallon nata yake idanu a ɗan lumshe cikin sanyin murya ta furta mashi "Thank you for loving me unconditionally Hubby. You have shown me what true love is, and I am forever grateful for that. I couldn't imagine my life without you" tana gama Maganar kwalla suka zubo mata sharrr, lumshe ido yay tare da ɗan murmushi yasa yatsa saman screen ɗin yana yin alamar goge mata ƙwallan hakan yasa ta yi yar dariya, Godiya ta shiga yi mashi sosae da Addu'o'i a hankali yake amsa mata daga baya sukai sallama cike da nuna ƙauna, a ranar haɗaɗɗun abinciccika suka haɗa mashi ita da mai aikin su da daddare kuwa duk da halin da take ciki saida ta tabbatar tayi mashi godiya ta hanyar gigitashi ta yadda har saida suka zubda hawaye su duka..........

101

~_*✊💋BOSS LADIES WRITERS💋✊*_~

.......Ranar Alhamis Hajiya ta kira kawu Mani na Daura ta tambaye shi gobe Juma'a zai shigo Katsina ne yace mata a'a amman in tanason ganin shi sai yazo tace mashi in bazata takura shi ba tana son ganin shi yace to ba damuwa zai shigo.
Chapter 170 · 0% Book details