← Book details Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 150 OF 211

Sashe 150

Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 5 min read

Washe gari da safe su Aunty suka tafi a ranar da daddare Haisam da Fanan suka iso, Washe gari Litinin Jidderh ta iso daga Dubai a ranar da yamma Haisam ya taho Katsina don gaba ɗaya a ƙagare yake da ganin Baby Fatuu ɗin sa, ko gaya mata zai zo bai yi ba saidai ta gan shi yazo sosae taji daɗi amman duk da haka saida tayi mashi shagwabar miyasa bai faɗi mata zai zo nan ba yace yana son yi mata surprise ne su twins ma sun yi murnar ganin Daddyn su, a daren ranar sun nuna yadda sukai kewar juna sosae, Washe gari aka fara program na Laila a Abuja don su zasu yi abubuwa bayan Dinner da walima da za'ayi in aka kawo Mino su zasu yi Ethiopian Night da Arabian, a ranar yan Adamawa suka iso babbar mota guda nan fa gidan gwaggo ya cika kamar yadda Yaya sukai da innar su Altine duk sun kwaso yan matan gidan a nufin su na suma su samu mazaje a dangin su Haisam, zuwa dare gidan har ya fara fita hayyacinshi don ma Yadikko na ɗan tsawatar ma yaran, har bayan isha Fatuu na gidan anata hira su twins tun bayan da aka cika gidan suka fara koke koke sun ƙi yarda a ɗauke su hakan yasa ta kai su wurin Hajiya don yanzu suna yarda da ita kuma Haisam na nan, suna hirar ne ake tambayar Fatuu inda gidan su yake ta faɗi masu ba nisa da an fita ne nan wasu suka ce wai zasu bita suga gidan sai su kwana kan ta basu amsa Gwaggo tace ai Mijinta na nan hakan ba ƙaramin daɗi yayi mata ba don ƙarshe tasan mi zai biyo baya in suka bitan, sai wurin ƙarfe goma saura ta baro gidan ta dawo gidan su lokacin data je part ɗin Hajiya ba kowa a cikin parlon hakan yasa ta wuce Bedroom ɗinta, da sallama ta shiga Hajiyar har ta kwanta amman bata yi bacci ba jin sallamarta yasa ta ɗago Fatun ta shiga, nuna mata bakin gado tayi alamar ta zauna, bayan ta zauna ta gaidata ta amsa kafin tace ai tayi tunanin ta dawo tuni gajiya tasa bata shigo ba Fatun tace a'a yan Adamawa suka zo ta tsaya yin hira dasu ne, tambayar yaushe suka iso tayi ta bata amsa da tun ɗazun zuwan nasu ne ma yasa ta aiko dasu twins don suna ta kuka sunga mutane tace "Allah sarki, sun zo lafiya ko?" amsa mata tayi da eh lafiya lou tace to Ma sha Allah, shiru suka ɗan yi kafin Hajiyar tace mata su twins ɗin na wurin babansu ya tafi dasu can part ɗin nasu ta amsa da to, miƙewa tay tayi mata sallama har zata juya Hajiya ta dakatar da ita da faɗin to maimakon ta taho da wasu nan su kwana tunda ga ɗakuna nan ko wanda suka zo ɗin basu da yawa ne ta bata amsa da suna da yawa tace to ai data rago wasu don su samu walwala gidan, shiru tayi bata ce komai ba a ranta tace ita yaushe zata rakito su suzo suyi ba daidai ba kawai sai gani tayi Hajiyar ta kai hannu gefen pillow ta ɗaukko wayarta, kiran layin gwaggo tayi bayan ta ɗaga ta amsa gaisuwar da take mata kafin tace hidima ta fara kankama Gwaggon na murmushi tace eh wllh Hajiyar tayi fatan Allah yasa taron ya tashi lafiya da sauri gwaggo ta amsa da Amin, ce mata tayi Fateema tace waɗanda suka zo da ɗan yawa to ta turo wasu sai su kwana anan ta amsa mata da to don ba damar ta musa mata, bayan sun gama wayar tace ma Fatuu da tayi tsaye sototo shikenan taje ta ƙara yi mata sallama ta juya ta tafi, sam Gwaggo bata so hakan ba duk da za'a samu sauƙin cukowar da aka yi amman tana fargabar tura wasu su kwana can, ƙarshe Yadikko ta kira gefe ta sanar mata ta bada shawarar a tura su Yaya da Mero sai innar su Altine sai kuma in za'a ƙara wasu amman su tana ganin lafiya lou bazasu yi ba daidai ba tunda sunje Abuja sun san wasu abubuwan na yan gayu gwaggo ta ɗauki sha'awararta, bayan anyi masu magana gwaggo taja Mero gefe don tana da natsuwa ta roƙe ta kan kada ta bari ayi ma Hajiyar ba daidai ba tace to suka tafi tare da Gwaggon ta raka su. Ranar Alhamis Mino tayi Friend's Eve anan part ɗin su Fatuu akayi decoration mai kyau a cikin harabar part d'in harda kujeru, cikin kuɗin da Nameer ya turo mata ta ba Aunty mareeya aka yo abubuwan ci da sha harda wanda zata raba, ba laifi kuma ƙawayenta yan makarantar bokon su da islamiyya da na nan cikin unguwa duk sun zo an ci an sha anyi rawa anyi nishaɗi sosae, a ranar bayan Magrib iyayen su maza harda Baffan su suka iso a gidan Hajiya ɗakin Tk aka sauke su shi kuma ya koma ɗakin Kawu Amadu, yan'uwan su Hajiya mata na nan Katsina da Daura duk sun wuce Abuja mazan kuma sun tsaya ɗaurin aure yan Daura ma sai gobe da safe zasu taho nan Katsina har angwayen da dangin su duk sai gobe in Allah ya kaimu zasu taho, da daddare Hajiya ta kira gwaggo take sanar da ita game da ɗaukar Amarya ance mutum biyar ake so su bada don a jirgi za'a tafi da ita tunda tafiyar bata kusa bace sosae hakan yayi ma gwaggo daɗi Hajiya tace da fatan ba'ai masu ba daidai ba da sauri gwaggo tace a'a wllh hakan yayi ai hidiman da yawa hakan ma ba ƙaramin ƙokari akai ba, Maganar sauran kayan ɗakin Minon da akwatunan lefenta gwaggo tayi ma Hajiyar,

"Wane kayan ɗaki kuma suka rage banda uwayen kayan da kuka takura kai kuka yi mata, ai dana san haka zaku yi mata kaya da bazan bari ba to bansan irin kayan da akai mata ba sai da akai kai su ake man magana abu duk ba an zama ɗaya ba sai a kama a matsa ma kai haka" da faɗa faɗa take Maganar Gwaggo na ɗan murmushi ta bata haƙuri tace ba takura ma kai akai ba an samu gudunmawa ne sosae Hajiyar tace "haka dai kika ce tunda ba sanin yadda akai akayi mata kayan nayi ba, yanzu su kayan da suka ragen su minene?" da sauri Gwaggon tace "dama kayan adon ɗaki ne da zasu iya fashewa sai akwatunan sai kuma kayan gara",
Chapter 150 · 0% Book details