← Book details Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 38 OF 211

Sashe 38

Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Da daddare bayan isha gaba d'aya Su Fauzy bajewa sukai a parlor harda su Aunty Mareeya gaba d'ayan su dai yan part d'in ana hirar Walima cike da nishad'i, Wayar Fatuu dake hannun Fauzy had'e da tata ce ta fara ringing ta kai idonta kan screen d'in, ganin Haisam ne yasa ta mik'e don taje ta kai mata, har lokacin ankonta ne a jikinta rigar ta kamata kanta tayi d'aurin kallabi mai steps da akayi mata gashinta dake fake ya fito ta tsakiya ya bud'e sosae, sauri sauri gudu gudu ta nufi cikin gidan ganin kiran ya yanke ya kuma sake kira, hanyar d'akin Mom d'in su Haisam ta nufa don tun bayan da aka gama Wa'azi Fatun na can Mom tasa ta zauna Saboda masu son ganinta ba sai an ta nemota ba, tana zuwa daidai bakin corridor tana niyyar shiga da d'an gudu gudu kwatsam taci karo da Mutum wanda har saida tai taga taga tayo baya, ba arziki ta kai hannu ta dafe goshinta idanunta a rufe ta shiga fad'in "wayyo..wai...wai.wai...." A yadda taji sai kace ta bugi dutse, a hankali ta d'ago still hannun na a goshin slowly ta fara bud'e idanunta, koda tay arba da wanda tay karon ai ba shiri ta idasa bud'e idanun ta waro su, tsaye yake k'ik'am sai kace an dasa shi don koda sukai karon bai ko yi gezau ba, Sameer ne yana sanye da farin jeans da farar riga ta ciki sai aka d'aura Yellow a sama ma6allan ta a bud'e hakan ya bayyana ta cikin agogon hannunshi fara ce itama daga wurin glass d'in kan yana reflecting yellow sai k'afafun shi ma sanye suke da fararen takalma, daga wurin Mom d'in shi yake Hajiya Zainab data kira shi bayan ya fito ya d'aga waya yana magana sukai karon, gaba d'aya wayar shin da glass d'in shi daya ruk'o a hannu sun fad'i k'asa, bin shi da kallo Fauzy tay gabanta na wani irin Fad'uwa ganin mugun kallon da yake mata ya tamke fuska sosae, Murya na rawa tace "D...don Allah kayi hakuri bansan ka taho bane ina sauri ne zan kai waya ana kira" ta k'arasa tare da d'aga mashi wayar don ya gani, in bango ya tanka to shima ya tanka haka yanayin fuskar tashi ma bai canza ba, yan kame kame Fauzy ta shiga yi tana haka idanunta suka sauka akan Wayar shi da glass d'in dake yashe a k'asa, da sauri ta duk'a ta d'aukko su Allah yaso glass d'in bai yi komai ba, tana juya wayar zata mik'a mashi taga glass d'in yayi lafiyayyun tsaga har kusan hud'u, zaro ido tay ta bud'e baki gabanta ya shiga wani irin bugu, ganin reaction d'in fuskar ta yasa slowly ya kai idanun shi kan wayar idanunshi suka sauka akan glass d'in dake a tsattsage, wani irin kallo ya d'ago yana mata da sauri ta fara ja da baya tana yamutsa fuska daga d'an can gaban shi ta tsaya, kawai sai gani tay ya fara nufota, tana shirin k'ara ja baya cikin husky voice d'in shi ya furta "Stay where you are!!!" har saida cikinta ya yamutsa, a gabanta ya tsaya ya mik'a mata hannu da sauri ta mik'a mashi wayar ya k'i amsa ta bishi da ido cike da tashin hankali, a kausashe ya furta ta bashi glass hannunta har kerma yake ta mik'a mashi ya amsa, saka shi a idanun shi yayi bayan ya gama ya tsaida kallonshi akanta duk da bata ganin idanun, k'ara Mik'o mashi wayar tay murya na rawa tace don Allah yayi hak'uri wllh bada niyya bane, banza yay mata sai da ya mula sannan ya furta "ki biya shi!" Wani irin miyau Fauzy ta had'iya ko ba'a fad'i mata ba daga ganin wayar tasan mai tsada ce balle kuma daya kasance ga wanda ke rike da ita, da yake dare ne kowa ya gaji wasu kuma basu a gidan ba wasu mutane da ke shigowa wurin sai wanda ba'a rasa ba sun fito su kuma ba lalle su fahimci abunda ke wakana ba don daga yanayin su sai kaga kaman magana suke, Magiya taci gaba da yi mashi kan yayi hak'uri tana cewa tasan bazata iya biyan shi ba, ringing wayar ta fara yi ta kalli wayar kafin ta kalle shi tana kikkafta idanu, hannu ya mik'a ya amsa ya furta mata "ki biyo ni" daga haka ya juya, tsaye tay duk da taji abunda yace aikuwa ya juyo cikin daka tsawa tace "I told you to Follow me!!!" bin shi tay ya nufi hanyar fita daga cikin parlon, daidai gaban wata Mota da aka parker a gaban Entry Hall ya dakata itama ta tsaya daga d'an nesa dashi, dama wayar da ya taho yana yi umarni yake badawa na azo a d'auke shi suka yi karon, hannu ya kai ya bud'e kopar gaba, da kai yayi ma driver d'in alamun ya fito, bayan ya fito tsayawa yay daga gefe ya d'an russuna kai, ce mashi yay yaje zai driving da kan shi yayi mashi godiya ya juya, juyawa yay ya kalli Fauzy da tay tsuru tsuru a kausashe yace "come and get in to the car!" Nan take k'wallan da suka tarun mata a ido suka fara zubowa taci gaba da yi mashi magiya tana yayi hak'uri don Allah, kai ya jinjina ya d'an cize baki can cikin d'an d'aga murya yace "I don't allow anyone to argue with me! Ki shiga Mota else, yanzu zan sa aje a kulle ki!" yarfa hannu Fauzy ta shiga yi a hankali ta fara fad'in ta bani, matsawa ta fara yi a hankali tana tunkarar Motar, ganin yadda take tafiya ya k'ara ce mata kada tay wasting time nashi, tana niyyar bud'e k'opar baya ya galla mata wata muguwar harara ba shiri ta fasa bud'ewa da kan shi yay mata alamar taje ta shiga gaba ta zagaya tana kuka k'asa k'asa, saida ta shiga sannan ya kai hannu cikin aljihun jeans d'in shi ya fiddo wani farin hanky ya shimfid'a a saman seat d'in sannan ya shiga, bayan ya zauna da k'arfi ya rufo k'opar, dama Motar a kunne take aikuwa a tsiyace ya ja ta bayan yasha round d'in ya Mik'i hanyar Gate ya fuce............

*ASM 081*

~_*✊💋BOSS LADIES WRITERS💋✊*_~

*DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAI JIN KAI*

.........Suna fita daga cikin gidan suka hau hanya, hankalin Fauzy in yayi dubu to ya tashi tunanin ta ina zai kai ta kuma mi za'a mata, basu dad'e da hawa titi ba wayar Fatuu dake hannun Fauzy ta fara ringing, a hankali ta juya ta kalli Sameer da idon shi na akan titi yana driving, a d'arare takai hannu zata d'auka a kausashe taji yace "Don't pick it!" fasa d'agawar tay ta juya ta kalle shi fuskarta a yamutse har lokacin k'walla na zubo mata, wani kiran ne ya sake shigowa bayan wanccan ya yanke taji yace ta kashe wayan gaba daya, cikin muryar kuka tace "Don Allah ka bari in d'auka in fad'i mashi bana gidan, Ya Haisam ke kiran matar shi wayarta ce dama ita na taho in kai mawa Saboda yanata kira shine har na buge ka ban gani ba" banza yay mata yana ta driving d'in, saida kiran ya kusa yankewa ya bata umarnin ta d'aga, hannunta har d'an rawa yake tay picking kiran, tun kafin yace wani abu ta riga shi ce mashi k'awarta ce wayar na a hannunta kuma bata gida ya Furta Ok kawae daga haka ya katse kiran, tafiya suke ta faman yi a saman shimfidaddun titinun Abuja, tun Fauzy na yin k'walla tana kai hannu tana gogewa har ta saduda taci gaba da kallon hanya ta widescreen don glass d'in Motar blacktinted ne ba'a ganin waje sosae ta cikin su, saida suka d'auki kusan mintuna 30 sannan suka iso wata unguwa mai d'auke da had'add'un manyan gine gine ga fitilu ta ko'ina kaman da rana, yar tafiya sukai a kan titin Unguwar suka iso bakin wani katafaren gida da jami'an yan sanda guda biyu ke gadi kowannensu na rataye da bindinga a jikin shi, karya kan Motar yayi ya tunkari dank'areren gate d'in gidan da sauri su duka jami'an suka hau zuge gate din, bayan sun gama ya nufi shiga cikin gidan duk suka d'aga ma Motar hannu, ko horn baiyi masu ba balle ya tsaya ya shige ciki da Motar da gudu, babban parking space d'in gidan ya nufa bayan ya parker ya kashe Motar, sai lokacin ya juya ya kalli Fauzy tun bayan da suka fito ya furta mata "come out!" bud'e baki tay da niyyar yin Magana ya bud'e kopar ya fita, hannunta sai rawa yake ta bud'e kopar ta zuru k'afafunta dake sanye da takalma masu d'an tudu kafin ta k'arasa fitowa, hankali tashe take bin gidan da kallo wanda ba k'arya ya matuk'ar Had'uwa, ba wani mugun girma gidan gare shi ba kuma ba k'arami bane, bene ne hawa d'aya iya fentin gidan abun kallo ne don ya tsaru sosae, a harabar gidan akwae had'add'un Flowers su kan su an tsara shukar su gasu a gyare luf luf dasu, daga can gefe runfunan shak'atawa ne guda ukku kowacce na d'auke da k'ayatattun kujerun katako a zagaye da table, zagaye da runfunan akwae manyan shukokin Flowers harda irin Xmas tree da ake ma adon fitilu itama anyi mata hakan tana ta sakin haske kala daban daban haka sauran flowers d'in akwae masu reflecting hasken dogayen fitilun dake a wurare daban daban a cikin harabar gidan sun haske ko ina ta yadda ko allurar ka ta fad'i to zaka iya ganinta, a cikin hall d'in sama wata jigunannar katuwar fitilar sama ce mai adon sarkoki kai kace in mutum ya tsaya zata fad'o mashi,
Chapter 38 · 0% Book details