← Book details Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 162 OF 211

Sashe 162

Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Ranar Juma'a lokacin sati guda da bikinsu Nameer Jirginsu Fatuu ya tashi zuwa Yola, a yadda Haisam ya shirya masu zasu sauka a gidan wani abokin Dad ɗin shi wanda shima Senator ne mai suna Buba daga nan sai suje garin su Fatun, bayan sun sauka wurin ƙarfe goma na safe Driver ne tare da ɗan mutumin mai suna Amir wanda zai yi shekara ashirin da biyar suka je ɗaukko su, kyakkyawar tarba suka samu daga iyalan mutumin harda shi aka saukesu a part guda cikin ƙaton kuma haɗaɗɗan gidan nashi anata so a ɗauki su twins sunƙi yarda, lafiyayyun abinci da abubuwan sha aka kawo masu bayan sun ci suka huta har lokacin sallar Juma'a yayi Haisam suka tafi Masallaci tare da Senator Buba da yaran shi maza, bayan sun dawo ne ya sanar mashi zasu tafi can garin su Fatuu yace ai yayi zaton zasu kwana su ƙara hutawa ya tambayi zasu kwana acan ne Haisam ɗin yace mashi ita zai baro ta can ta kwana biyu shi zai dawo nan yace tunda hakane yana ganin kaman yanzu lokaci ya ƙure kar suyi dare ya bari gobe tunda safe sai Driver ya kaisu yadda shima zasu gaisa sosae Haisam ɗin ya amince da hakan. Washegarin wuraren ƙarfe tara da yan mintuna sukai sallama da mutanen gidan suka tafi, tafiyar Awa guda sukai suka iso tun shigowarsu bakin garin Fatuu ta fara murmushin farinciki sosae tayi kewar garin don kusan fin shekara ukku rabonta dashi da yake yanayin damuna ya fara don wasu wuraren sun fara samun ruwa ciki harda nan garin hakan yasa ganyayyaki da tsirrai sun yi kore shar shar gwanin sha'awa ga makiyaya nata koro garken shanaye da tumakai za'a tafi kiwo, Haisam dake zaune seat ɗin gaba nata kallon garin bayan sun shigo Fatuu ce ke nuna ma Driver hanya yana bi har suka ƙaraso kopar gidan tace mashi nan ne, wasu dattawan mutane da a ƙalla zasu kai biyar na zaune a ƙarƙashin ƙatuwar bishiyar dake a ƙopar gidan wasu daga cikin su yan gidan ne ciki harda Mahaifin Fatuu daya zauna yana dakon zuwan su da yake da zasu baro Yola ta kirashi ta sanar mashi sai mutum biyu a cikin su duk yayyen shi ne sauran biyun kuma abokai ne, daga can gefen su yara ne ba masu yawa ba suna ta wasa, bayan ya parker suka buɗe ƙofofin Motar suna fitowa Mutanen dake zaune suka miƙe a kusan tare suka nufo su, cikin washe baki suka shiga yi masu sannu da zuwa Baffan su Fatuu dai murmushi yake idon Fatun na akan shi itama tana murmushin farincikin ganin shi, bayan sun gama gaisawa da Haisam itama ta gaishe su suna ta fara'a suka amsa mata duk wanda yay yunƙurin ɗaukar su twins sai su ƙanƙame jikin iyayen nasu da yake kowa na ɗauke da guda ɗaya, bayan an gama yi masu sannu da zuwa Baffan tare da yayun nashi sukai ma Haisam jagora zuwa ciki, suna shiga cikin soro su Aysha suka shigo da gudu suka nufi Fatuu suka ƙanƙameta cike da farinciki suke mata sannu da zuwa da fullanci Adam dake hannunta ya fara ta6e baki zai yi kuka don sun rungumeta Aysha ta ɗago tana miƙa mashi hannu ya ƙiya sai kallonta yake kaman mai son tuna ta don da bakin su Mino ya yarda da ita Fatuu ta rinƙa faɗi mashi kowacece da fulatanci sai gashi ya tuno ta ya miƙa mata hannu cikin washe bakin jin daɗi ta ɗauke shi, ganin an amshi Adam yasa tace ma Haisam yabata Abie kafin suka idasa shiga cikin gidan mutane duk an leƙo ana masu sannu da zuwa Fatuu ke amsawa shi kuma Haisam kai yake ta jinjina masu fuskarshi a sake.......

100

~_*✊💋BOSS LADIES WRITERS💋✊*_~

.........Bangaren da Arɗo yake aka kaisu can gefe da inda nasu Yaya yake an kewaye wurin da yar gajeruwar kanta daga cikin wurin harda siminti a ƙasa, shiga sukai cikin ɗakin wanda yana da ɗan matsakaicin girma akwae madaidaicin gado na katako yana da wardrobe mai gida biyu samantaa an ɗaura wasu tsofaffin akwatuna na fata dana ƙarfe akwae yan durowoyi na gadon sai wata yar kanta da aka ɗaura al'quranai da wasu littafan addini daga jikin bango kuma wanda ke shafe da siminti an rataye abubuwan fulani harda takubba a cikin gidajen su daga saman ɗakin anyi ceiling irin na da da ake yi da itatuwa ƙasan ɗakin kuma gaba ɗaya a rufe yake da ledar tsakar ɗaki harda ɗan madaidaicin carpet daga tsakiya wannan duk aikin Baffan su Fatuu ne don kullum cikin yi ma mahaifin nasu hidima yake dama kuma yafi duk yan uwan shi wayewa, lokacin da suka shiga Arɗon na kwance a saman gadon jikin shi sanye da riga da wando na yadi mara nauyi sai hula ha6ar kada a saman kan shi suna shiga ya fara ƙoƙarin tashi zaune bayan Baffan su Fatuu ya sanar mashi ga su Inna wuro da maigidan nata sun iso da yake yasan da Maganar zuwan nasu duba jikin shi, saida aka taimaka mashi sannan ya zauna Haisam na niyyar zama a saman carpet da sauri cikin muryarshi data disashe yace kar ya zauna nan Haisam ɗin bai ma ji abunda yace ba ya dai gane ta hanyar hannu daya ɗaga mashi hakan yasa ya dakata Arɗon ya kalli Baffan su Fatuu da fullanci yace ya ɗaukko masu darɗuman makkan shi a cikin kayan shi, Makkan da ya shekara kusan fin talatin da zuwa wasu Ƴaƴan shi ma basu san da yaje ba balle kuma su Fatuu jikoki, bayan ya ɗaukko dardumar wadda ba laifi bata ji jiki ba saboda ji yake da ita don ta shiga cikin tarihin zuwa makkan shi tana da girma, shimfiɗa masu yay a saman carpet suka ce ma Haisam ya zauna Fatuu ma ta zauna daga gefe suma Yayun Baffan dashi duk suka zauna daga gefe nan aka shiga ƙara gaisawa ya juya suka gaisa da Arɗo tare da yi mashi ya jiki a hankali yake amsawa Fatuu ma ta gaishe shi da fullanci tayi mashi ya jiki ya amsa yayi mata sunzo lafiya da tambayar ya suka baro sauran mutane duk ta amsa masu ya kalli su twins yace wannan sune Ƴaƴan nashi da bai sani ba tana murmushi tace eh ya miƙo hannu alamar a bashi su Babban ɗanshi wanda yana cikin wanda suka shigo shima ya manyanta sosae yana murmushi yace ai basu yarda da mutane duk da haka Fatuu ta miƙe da Abie tayi ma Aysha dake daga can bakin ƙopa alamar ta kawo Adam suka kai mashi su, kamar ma tsoron Arɗon suke duk sun waro fararen idanunsu tubarkallah suna bin shi da wani irin kallo daya miƙo masu hannu sai su ƙanƙame su Fatun ƙarshe saidai a hannun nasu ya gansu ya saka masu albarka harda tofin Addu'a yayi masu yace ma Fatuu kafin su koma zai bada magungunan kariya a rinƙa basu tace to, a nutse Haisam cikin cool voice ɗin shi ya tambayi an kai shi Asibiti ne don asan abunda ke damunshi Modibbo ya bashi amsa da sun kai shi Babbar Asibiti ta Jumeta anyi mashi gwaje gwaje an tabbatar ba abunda ke damunshi kawai shekarune to sun bada wasu magunguna sannan sun ce ya rinƙa samun hutu sosae to ya gama shan magungunan kuma yana samun isashshen hutun don ko zama a fadar shi ma bai yi yanzu shiyasa ma jikin nashi da sauƙi sosae, kai Haisam ya jinjina kafin yace yana ganin yakamata a kai shi Asibitin ƙwararru dake a Yola a ƙara mashi bincike sosae suka ce to shidai Baffan su Fatuu shiru yay saidai a ranshi yaji daɗin hakan da Haisam yace don ba yarda baiyi ba a kaishi can amman yayun nashi suka ce kawai 6arnar kuɗi ne tunda an tabbatar da lafiyar shi lau, nuna ma Fatuu wata yar ƙwarya dake a rufe da faifai Arɗo yay yace mata ga fura nan taba Haisam da sauri Baffanta yace mashi ya barta tashi ce yasha suma ga ta can an haɗa masu yanzu zasu je sai su sha ya ɗaga kai Modibbo yace yakamata suje an barsu ko ruwa ba'a basu ba Baffan yace to tare da miƙewa suka ce ma Haisam suje suci Abinci duk suka miƙe harda Fatuu,
Chapter 162 · 0% Book details