Sashe 188
Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
tana fitowa ɗakin Husnah ta nufa tana niyyar shiga Husnar ta fito daga ɗayan bedroom ɗin nata cike da farinciki Farhar ta sanar mata Mom ɗinta ta amince ma soyayyarsu da Kamal ta ɗan buɗa ido kafin tana murmushi tace ta tayata murna Allah ya tabbatar da alkhairi ta amsa da Amin ta ƙarasa shigewa cikin ɗakin, gyale ta yafo saman kanta tana fitowa falo ta nufi hanyar fita, gidan Gwaggo ta nufa bayan ta fito koda tazo shagon Amadu a rufe yake ta shige gate, tana niyyar shiga entrance Amadu na sako kai dama wanka ya shigo yi yana ganinta yaja ya tsaya yana ƙare mata kallo ita kuma tana ɗan murmushi ta gaishe shi bai amsa ba da tsananin mamaki yace mata an ganta kenan tay yar dariya tace dama ba 6acewa tayi ba tana nan gidan Hajiya, da alamun rashin fahimta yace kuma shine aketa cigiyarta, nan ta kwashe komai ta faɗi mashi sosae ya jinjina abun yace lallai Hajiya ta iya shirya abu kamar Film, tare suka shiga ya nufi part ɗin Gwaggo da ita lokacin Haulat ma na can sun fara aikin abincin rana, a falo suka tsaya Amadun ya shiga ƙwala ma Gwaggo kira yana ta fito taga wani abu, tana fitowa tayi arba da Farha itama zaro ido tay cike da al'ajabi tace kamar Farha take gani Amadu na murmushi yace itace da sauri ta tambayi ina aka ganta nan Amadun ya faɗi mata ashe wai tana gidan Hajiya Gwaggon ta washe bakin farinciki tace dama sai da Haulat ta zargi hakan da suka je jaje nan ta shiga ƙwala ma Haulat kira, bayan ta fito daga cikin Kichen ɗin itama saida ta nuna mamakin ganin Farha cikin washe baki Gwaggo ta shiga faɗin zarginta ya tabbata ashe wai tana wurin Hajiya Haulat ɗin tace ita dama tunda suka je ta lura da sam Hajiyar bata cikin damuwar 6acewar tata, zama sukai kan kujeru Amadu yace ma Farhar yaga mamanta ma tazo ɗazun ta gano tana nan kenan tace mashi a'a sai bayan data zo, nan take faɗi masu ai yanzu ta amince da tarayyarsu da Kamal ɗin cike da tsokana Amadu yace ai da ta haƙura da Kamalun tabi abunda Mom ɗin nata ke so ta wani tura mashi baki tare da ɗaure fuska duk sukai dariya, tambayar shi tayi Kamal ɗin tace ko yana School yace mata ai rabon shi da School tunda yaji labarin ta gudu saboda shi yanzu haka yana ɗaki bai jin daɗi, ai tana jin haka zumbur ta miƙe ta nufi hanyar ɗakinshi tana faɗin bari taje ta faɗi mashi ba guduwa tayi ba duk suka bita da kallo, juyowa Amadu yay ya kalli Gwaggo dake murmushi yace Allah ya haɗata da suruka ƙwara ba kunya duk sukai dariya, lokacin data shiga cikin ɗakin yana kwance kan katifa idanunshi a rufe tay tsaye daga gaban ƙopa tana kallonshi da murmushi can ta kira sunan shi "Kamal" a hankali ya fara motsa idanun shi masu ɗauke da zarazaran gashin ido kafin ya buɗesu ya ƙura ma gabanshi ido duk ɗaukar shi muryarta ce ke mashi gizo, saida ta ƙara kiran nashi sannan da sauri ya ɗago kai ai koda yay arba da ita a firgice ya ƙarasa tashi zaune yana kallonta ita kuma sai murmushi take mashi ya murje idanun shi ya buɗe ganin still tana nan yasa shi nunata tare da kiran sunanta ta ɗage mashi gira tare da amsa mashi da Yes, zumbur yay ya miƙe tsaye da alamun al'ajabi yace don Allah da gaske itace yadda yay tambayar ne ya bata dariya don duk alamun tsoro ya bayyana a tattare da shi tace mashi itace mana amman tunda taga bai yi farincikin ganinta ba bari ta koma da sauri yace a'a ta tsaya pls ya nufeta, a ɗan gabanta ya tsaya har fuskar shi ta faɗa da tsananin mamaki yace mata yaushe aka ganta ne kuma miyasa zatai haka, saida ta matso gaban shi sannan tace mashi itafa ba 6acewa tayi ba dama duk shiri ne nan ta shiga faɗi mashi yadda akai, shima sosae yayi mamaki cike da farinciki ta kai duka hannuwanta ta kamo nashi tace "guess what?" da sauri ya girgiza mata kai ta sanar dashi yanzu babu wata matsala zasu yi soyayyarsu hankali kwance don Mom ɗinta ta amince masu ya ɗan buɗa ido yace don Allah da gaske tace eh mana yanzu haka Mom ɗin nasu na gidan Hajiya, ƙayataccen murmushin daɗi ya shiga saki tace yayi haƙuri ta saka shi ciwo in ba hakan akayi ba Mom ɗin nasu daba lalle ta amince masu ba, da sauri yace ba komai ai yanzu ma yaji ya warke shi dama abunda yafi damunshi shine a wane hali take ciki hakan har kuka yake saka shi, bin juna sukai da wani irin kallo mai nuni da tsantsar ƙaunar da suke ma juna can Farhar ta furta "I love so much Kamal, pls dont turn your back on me",
"I will never do that to you, My Love, i'm very grateful for accepting me for who i am, ban ta6a tunanin zaki so ni haka ba saboda tazarar dake tsakanin mu ajin ki ya wuce na ki soni shiyasa koda kika nemi da muyi ƙawance saida na jinjina abun sosae yanzu gashi kin za6i ma in zama abokin rayuwarki, i can't thank you enough, but, i give you all my heart in return" wani kalan murmushin daɗi tay ta faɗa jikinshi tare da lumshe ido yay shiru ƙirjin shi na bugawa don hakan abu ne da bai ta6a faruwa dashi ba ya haɗa jikin shi da mace koda kuwa yar'uwarshi tun bayan daya balaga duk da su a al'adarsu hakan ba wani abu bane amman su da yake suna da ilimin addini sun san hakan haramun ne shiyasa bai ta6a kowacce mace, hannu ya kai ya ɗagota suka haɗa ido tana ɗan murmushi ta furta yayi haƙuri taji daɗin Maganarshi ne, dama tun ba yanzu ba da suna ƙawance tana yawan ta6a shi tun yana sharewa ganin abun na yin yawa yace mata ta bar ta6a shi ba kyau kada su rinƙa samun zunubi, ce mashi tayi yazo suje ya gaida Mom ɗin ta ya ɗan waro ido tare da buɗa baki yace ba matsala kuwa tay yar dariya tace mashi he should be a man ba abund zai faru shima yay dariya yace to ko ta jirashi a falon Gwaggo ko Aunty Haulat ya shirya tace Ok ta juya tana faɗin yayi kyau sosae yace to, shiryawa yay cikin ƙananun kaya baƙin jeans da jar t-shirt anyi bakin rubutu a gabanta ƙafafunshi yasa baƙaƙen takalma sai agogo itama baƙa sumar nan tashi tubarkalla dama koda yaushe a kwance take ya ƙara gyarata sai salƙi take ya feshe jikinshi da turare ko maƙiyinshi sai dai don ƙiyayya yace bai yi kyau ba, lokacin da suka fito Amadu na shago yaje yace mashi zai je gaida surukarshi yay mashi Addu'a yay Maganar yana dariya shima Amadun dariyar yayi yace to Allah yasa a wanye lafiya in sun ji shiru kuma zasu zo beli Kamal ɗin yay dariya, tunda suka shigo harabar gidan gabanshi ke ɗan faɗuwa hakanan ya daure, lokacin da suka shigo cikin parlon ba kowa su Husnarh na Kitchen don rana tayi ta nufi bedroom ɗin Hajiya tare dashi, ita ta fara shiga shi kuma yay tsaye saida ta kalli cikin ɗakin taga yadda suke sannan ta juyo tace mashi ya shigo mana, ƙasa ƙasa da murya yace ta fara faɗi masu mana Hajiya dake kishingiɗe akan lallausan carpet ɗin gaban gado ta tada kai da tuntun ta ɗan ɗaga murya tace ita da waye anan ta maido kanta cikin ɗakin tana murmushi tace Kamal ne, tashi zaune sosae Hajiyar tayi tana faɗin to ya shigo mana shida ɗakin matarshi, tare suka shiga yay sallama ta amsa tana murmushi lokacin da idanunshi suka sauka akan Hajiya Maryam dake kwance saman gado ta rufe odo ƙananun kitson kanta sun bayyana sai da gabanshi ya buga sosae da sauri ya kauda idon, nuna mashi wuri Hajiya tay gefenta tace ya zauna Farha ma ta zauna cikin muryarshi mai daɗi ta bafullatanin daya ji hausa ya gaishe da Hajiya ta amsa tare da yi mashi ya jiki tace ai tukur ya faɗi mata yana can yana zazza6i Masoyiyarshi ta 6ace, da sauri ya sunnar da kan shi don wata irin kunya ce ta rufe shi data yi maganar Farha dake murmushi tace ko School baya zuwa,
"To ai yanzu sai kaci gaba da zuwa tunda gata ta bayyana" ta faɗa tana yar dariya shima murmushi yake bai ce komai ba, juyawa tay kan Hajiya Maryam tace tayi bacci ne ga ɗanta yazo su gaisa shiru bata motsa ba Hajiyar tace ƙilan tayi bacci dama bayan ta gama cin abinci tace bacci take ji, miƙewa Farha tay ta rankwafa saman gadon ta shiga ɗan bubbugata, buɗe ido tay da alamu baccin ne ya ɗauketa fuska a yamutse tace lafiya ta tashe ta nuna mata saitin Kamal tayi tace dama shine yazo gaidata ta wurga mata wani kallo mai kamar harara, har zata faɗi wata magana sai kuma tayi shiru ta maida idonta kan Kamal Farha tace mashi su gaisa ya ɗago ido ya kalli Hajiya Maryam ɗin cikin faɗuwar gaba yace mata ina wuni kamar bazata amsa ba sai kuma ta ɗaga mashi kai ya ƙara cewa an zo lafiya kamar wadda akai ma dole tace lafiya daga haka ta maida idanunta ta rufe, cigaba da jan shi da magana Hajiya tayi har tana tambayar yanayin karatunshi yana dai maida hankali ko yace mata eh, bayan wani ɗan lokaci yay mata sallama ya miƙe Farha ma ta miƙe Hajiya ta kalleta tana murmushi tace Juliet za'a raka Romeo tayi dariya, buɗe ido Hajiya Maryam tayi tabi Kamal ɗin da kallo har suka fita Hajiya data lura da tana kallon Kamal ɗin bayan fitar su tana murmushi tace to ya taga surukin nata tayi shiru bata ce komai ba,
"I will never do that to you, My Love, i'm very grateful for accepting me for who i am, ban ta6a tunanin zaki so ni haka ba saboda tazarar dake tsakanin mu ajin ki ya wuce na ki soni shiyasa koda kika nemi da muyi ƙawance saida na jinjina abun sosae yanzu gashi kin za6i ma in zama abokin rayuwarki, i can't thank you enough, but, i give you all my heart in return" wani kalan murmushin daɗi tay ta faɗa jikinshi tare da lumshe ido yay shiru ƙirjin shi na bugawa don hakan abu ne da bai ta6a faruwa dashi ba ya haɗa jikin shi da mace koda kuwa yar'uwarshi tun bayan daya balaga duk da su a al'adarsu hakan ba wani abu bane amman su da yake suna da ilimin addini sun san hakan haramun ne shiyasa bai ta6a kowacce mace, hannu ya kai ya ɗagota suka haɗa ido tana ɗan murmushi ta furta yayi haƙuri taji daɗin Maganarshi ne, dama tun ba yanzu ba da suna ƙawance tana yawan ta6a shi tun yana sharewa ganin abun na yin yawa yace mata ta bar ta6a shi ba kyau kada su rinƙa samun zunubi, ce mashi tayi yazo suje ya gaida Mom ɗin ta ya ɗan waro ido tare da buɗa baki yace ba matsala kuwa tay yar dariya tace mashi he should be a man ba abund zai faru shima yay dariya yace to ko ta jirashi a falon Gwaggo ko Aunty Haulat ya shirya tace Ok ta juya tana faɗin yayi kyau sosae yace to, shiryawa yay cikin ƙananun kaya baƙin jeans da jar t-shirt anyi bakin rubutu a gabanta ƙafafunshi yasa baƙaƙen takalma sai agogo itama baƙa sumar nan tashi tubarkalla dama koda yaushe a kwance take ya ƙara gyarata sai salƙi take ya feshe jikinshi da turare ko maƙiyinshi sai dai don ƙiyayya yace bai yi kyau ba, lokacin da suka fito Amadu na shago yaje yace mashi zai je gaida surukarshi yay mashi Addu'a yay Maganar yana dariya shima Amadun dariyar yayi yace to Allah yasa a wanye lafiya in sun ji shiru kuma zasu zo beli Kamal ɗin yay dariya, tunda suka shigo harabar gidan gabanshi ke ɗan faɗuwa hakanan ya daure, lokacin da suka shigo cikin parlon ba kowa su Husnarh na Kitchen don rana tayi ta nufi bedroom ɗin Hajiya tare dashi, ita ta fara shiga shi kuma yay tsaye saida ta kalli cikin ɗakin taga yadda suke sannan ta juyo tace mashi ya shigo mana, ƙasa ƙasa da murya yace ta fara faɗi masu mana Hajiya dake kishingiɗe akan lallausan carpet ɗin gaban gado ta tada kai da tuntun ta ɗan ɗaga murya tace ita da waye anan ta maido kanta cikin ɗakin tana murmushi tace Kamal ne, tashi zaune sosae Hajiyar tayi tana faɗin to ya shigo mana shida ɗakin matarshi, tare suka shiga yay sallama ta amsa tana murmushi lokacin da idanunshi suka sauka akan Hajiya Maryam dake kwance saman gado ta rufe odo ƙananun kitson kanta sun bayyana sai da gabanshi ya buga sosae da sauri ya kauda idon, nuna mashi wuri Hajiya tay gefenta tace ya zauna Farha ma ta zauna cikin muryarshi mai daɗi ta bafullatanin daya ji hausa ya gaishe da Hajiya ta amsa tare da yi mashi ya jiki tace ai tukur ya faɗi mata yana can yana zazza6i Masoyiyarshi ta 6ace, da sauri ya sunnar da kan shi don wata irin kunya ce ta rufe shi data yi maganar Farha dake murmushi tace ko School baya zuwa,
"To ai yanzu sai kaci gaba da zuwa tunda gata ta bayyana" ta faɗa tana yar dariya shima murmushi yake bai ce komai ba, juyawa tay kan Hajiya Maryam tace tayi bacci ne ga ɗanta yazo su gaisa shiru bata motsa ba Hajiyar tace ƙilan tayi bacci dama bayan ta gama cin abinci tace bacci take ji, miƙewa Farha tay ta rankwafa saman gadon ta shiga ɗan bubbugata, buɗe ido tay da alamu baccin ne ya ɗauketa fuska a yamutse tace lafiya ta tashe ta nuna mata saitin Kamal tayi tace dama shine yazo gaidata ta wurga mata wani kallo mai kamar harara, har zata faɗi wata magana sai kuma tayi shiru ta maida idonta kan Kamal Farha tace mashi su gaisa ya ɗago ido ya kalli Hajiya Maryam ɗin cikin faɗuwar gaba yace mata ina wuni kamar bazata amsa ba sai kuma ta ɗaga mashi kai ya ƙara cewa an zo lafiya kamar wadda akai ma dole tace lafiya daga haka ta maida idanunta ta rufe, cigaba da jan shi da magana Hajiya tayi har tana tambayar yanayin karatunshi yana dai maida hankali ko yace mata eh, bayan wani ɗan lokaci yay mata sallama ya miƙe Farha ma ta miƙe Hajiya ta kalleta tana murmushi tace Juliet za'a raka Romeo tayi dariya, buɗe ido Hajiya Maryam tayi tabi Kamal ɗin da kallo har suka fita Hajiya data lura da tana kallon Kamal ɗin bayan fitar su tana murmushi tace to ya taga surukin nata tayi shiru bata ce komai ba,