Sashe 182
Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 4 min read
"Uhm, to ke kin isa ki hana faruwar wani abun ne, yaran yanzu ana hanasu abunda suke so ne, kina iya kiga ai kin hanashi yin tarayya da ita su zagaye can suna soyayyarsu ƙarshe kuma abunda kike gudun yazo ya faru don haka ki rabu dasu ayi masu fatan alkhairi ba abunda zai faru face abunda Ubangiji ya ƙaddaro zai faru", kai Gwaggo ta jinjina tace hakane Allah ya tabbatar da alkhairi Hajiyar ta amsa da Amin tace shikenan, Gwaggo har taji ta ɗan samu natsuwa bayan wani lokaci tayi mata sallama ta tafi. A ranar Minister Hajiya Maryam ta sauka Lagos dama duk Friday take dawowa sai ranar Lahadi da yamma ta koma a yadda suka tsara da maigidan nata wani lokacin shi zaije can Abujar tare da yara, sosae sukai murnar zuwan Momyn nasu tayi shiga ta alfarma ada ma tayi ado balle yanzu da suke da ƙasa, bayan an gama murnar zuwan nata Bedroom ɗin Daddyn su ta wuce dama shiya ɗaukkota daga Airport, da daddare tare suka ci abinci cikin nishaɗi bayan sun gama suka koma falo nan ta shiga tambayar yaran nata buƙatunsu kowa na faɗi da aka zo kan Farha yamutsa fuska tay tace ita bata da wata buƙata kawai so take su kasance tare koda yaushe don kula da yaran nan na bata wahala Hajiya Maryam ɗin na dariya tace to wace wahala take sha abunda akwae masu aiki ba girki take masu ba ba wanki da guga take masu ba haka ba shara take ba Farhar tace duk da haka basu barin kunnuwanta su huta Hajiya Maryam ɗin tace to ta ɗan ƙara haƙuri bada jimawa ba zasu koma Abuja baki ɗaya sai suci gaba da yin School acan nan kuma da Weekend ko lokacin hutu sai su rinƙa zuwa nan fa su Abraham suka shiga yin murna, sun ɗan dauki lokaci a falon kafin sukai ma juna saida safe kowa ya wuce part ɗin shi itama suka wuce tare da Dr Mohammad part ɗin shi suna saƙale da hannun juna, Washe gari Asabar tun da wuri aka kai yaran gidan islamiyya ya rage sai Farha don ita tunda tayi sauka ta daina zuwa, wuraren ƙarfe goma suka zauna yin breakfast duk sunyi wanka sai ƙamshi suke, Farha ce ta fara tashi daga kujerarta alamar ta ƙoshi Dad ɗinta yace ta jira shi a parlor zasu yi magana tace Ok, a tare suka gama da Hajiya Maryam ɗin suka nufi parlon duk suka zazzauna tun ma kafin Dad ɗin yayi magana ta yanke a ranta Maganar Emran zai mata, bayan sun zauna a nutse da turanci Dad ɗin nata ya fara mata magana yace mike faruwa ne tsakaninsu da Emran ya kirashi cikin tashin hankali yace tace bazata aure shi ba gaba ɗaya ya tada ma iyayen shi hankali suma sun kira shi kan Maganar, da alamun mamaki Hajiya Maryam ta maimaita bazata aure shi ba Dad ɗin yace haka Emran ɗin yace mashi tace, kallon Farha tayi tace miya faru tsakanin su ne da zata ce haka ta fara yamutsa fuska ta kasa yin magana Dad ɗinta yace kar taji komai ta faɗi masu in wani ƙwaƙƙwaran dalili ne zasu goya mata baya, muryarta kaman zata yi kuka tace ita ta daina son shi gaskiya ta samu wani wanda take so shi zata aura, a tare iyayen nata suka kalli juna alamar mamaki,
"Yaushe kika samu wanin da mu bamu sani ba?" Hajiya Maryam ta tambaya Farhar ta shiga motsa baki kafin tace sun ɗan daɗe tare sun fi shekara, tambayarta Dad ɗinsu yay waye shi kuma a ina yake saida cikinta ya ɗan kaɗa fargabar faɗin ko waye ta kamata ba kowa take tsoron yaji ko waye ba face Hajiya Maryam don inda Dad ɗinta ne kaɗai bazata ji komai ba zata faɗi mashi, Mom ɗin su ce ta ɗan ɗaga murya tace ita suke saurare suna da abun yi, da ƙyar ta tattaro ƙwarin gwuiwa idonta akan Dad ɗinsu tace a Katsina y
ake Yayan abokiyar zaman Sis Fanan ne, ɗan waro ido Hajiya Maryam tay tace wace abokiyar zaman Fanan ɗin badai wannan dangin shanun take nufi ba cikin tura baki Farhar tace ita, wata gigitacciyar tsawa data daka mata sai da suka tsorata su duka hada Dad ɗin
a fusace tace "tsabar kin raina mu yasa kike dubar idanun mu kina faɗin Mutumin daji zaki kawo mana mu aura maki!!!!" idanun Farhar ne suka ciko da ƙwalla tana tura baki tace ai ba a daji yake ba ko yana nan gidan kakar shi a Katsina kuma yanzu haka yana cikin yin Degree ɗin shi a Umyuk,
"Yaushe kika samu wanin da mu bamu sani ba?" Hajiya Maryam ta tambaya Farhar ta shiga motsa baki kafin tace sun ɗan daɗe tare sun fi shekara, tambayarta Dad ɗinsu yay waye shi kuma a ina yake saida cikinta ya ɗan kaɗa fargabar faɗin ko waye ta kamata ba kowa take tsoron yaji ko waye ba face Hajiya Maryam don inda Dad ɗinta ne kaɗai bazata ji komai ba zata faɗi mashi, Mom ɗin su ce ta ɗan ɗaga murya tace ita suke saurare suna da abun yi, da ƙyar ta tattaro ƙwarin gwuiwa idonta akan Dad ɗinsu tace a Katsina y
ake Yayan abokiyar zaman Sis Fanan ne, ɗan waro ido Hajiya Maryam tay tace wace abokiyar zaman Fanan ɗin badai wannan dangin shanun take nufi ba cikin tura baki Farhar tace ita, wata gigitacciyar tsawa data daka mata sai da suka tsorata su duka hada Dad ɗin
a fusace tace "tsabar kin raina mu yasa kike dubar idanun mu kina faɗin Mutumin daji zaki kawo mana mu aura maki!!!!" idanun Farhar ne suka ciko da ƙwalla tana tura baki tace ai ba a daji yake ba ko yana nan gidan kakar shi a Katsina kuma yanzu haka yana cikin yin Degree ɗin shi a Umyuk,