Sashe 32
Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 7 min read
A ranar bayan sallar Azahar Fanan ta iso Haisam ne yaje ya d'aukko ta a Airport ita kadae tazo sai autar su Noor, bayan ta iso a d'akin Mom d'in su ta sauka aka hau haba haba da ita ana mata sannu da zuwa daga baya tace bari taje su gaisa da Hajiya, Jidderh ce taje baya ta sanar ma Fatuu zancen zuwan Fanan d'in suka taho tare, bayan sun je d'akin Mom d'in aka sanar masu tana d'akin Hajiya suka nufi can, tana zaune a bakin gado su Fatuu suka shigo suna had'a ido ta nufeta da gudu suka rungume juna su Hajiya da gwaggo da wasu dake cikin d'akin suna ta murmushi don ba K'aramin burge mutane sukai ba, d'agowa Fatuu tay ta duk'a kasa hannunta cikin na Fanan d'in ta gaishe da ita tayi mata an zo lpy tana ta murmushi ta ke amsa mata tana fad'in Amaryar su, daga baya tare suka tafi harda Jidderh suka nufi baya, d'akin su Aunty Mareeya ta kai ta Feenah na ganinta ta mik'e tana murmushi take fad'in "You are Welcome Uwargidan H,Zakee" murmushi kawae Fanan d'in ke yi ta nufi bakin gado ta Zauna Aunty Mareeya ta bita da kallo don ta gane itace kishiyar Fatuu, gaidata Fanan d'in tayi tana murmushi ta amsa tayi mata an zo lafiya tace lafiya lou, hira suka shiga yi sosae ta burge Aunty Mareeya yadda bata da d'agin kai ko kad'an, suna haka Jidderh da Fatuu suka kawo mata abinci da abun sha Aunty Mareeya na dariya ta kalli Fatuu tana fad'in su Zarah anga Yaya sai washe baki ake duk suka kalli Fatun ta kai hannu ta rufe fuska Fanan ce tace mata ya Amarya ba k'unshi kuma tace anjima zasu je ba wani mai yawa ne za'a mata ba tace Ok, daga baya su Fatun suka fita Aunty Mareeya tace mata taci Abincin mana tace ok ta saukko kan Carpet ta zauna Noor dai na wurin Hajiya, sosae suka shiga yin hira anan har Aunty Mareeya da Feenah na yaba mata kan namijin k'ok'arin da tayi tana d'an murmushi tace ai haka yakamata don in kace zaka ja da hukuncin Ubangiji to kai ne a wahala gaba d'aya suka ce hakane wllh, karshe dai a nan ta wuni.
Misalin k'arfe biyar na yamma lokacin su Fatuu na wurin kunshi dankara dankaran Motoci suka shigo cikin gidan da jiniya nan take aka gane Her Excellency Hajiya Zainab ce ta iso, a gaban Entry Hall na gidan Motocin suka parker nan da nan jama'ar cikin gidan suka fara fitowa wanda suka san itace da wanda ma basu san itace ba kawai jiniyar tasa su fitowa, wani Security ne daga cikin Escort d'inta na Motar gaba ya fito da sauri yazo ya bud'e mata k'opa ta zuro farar kafarta data k'unshi ga wani mayen takalmi golden sanye a k'afar, k'arasa fitowa tay tana sanye da rantsatstsen lace bak'i mai adon green da ratsin golden kad'an, tun daga kunnan ta zuwa wuyanta da yatsun hannunta duk gold ne ta yafa mayafi golden kalar takalmanta da jakarta abun sai dai ace Tubarkallah dama tana d'aya daga cikin Matan gwamnoni da suka san takan gayu, Security detail d'in ta mace ce ta fito tazo bayanta ta tsaya wani daga cikin Escort d'in nata ya nufi Motar dake bayan tata ya bud'e yaran ta ne suka fito cikin shiga ta Alfarma, Mota ta biyun k'arshe wani security d'in ya fito daga cikin Escort d'in Motar baya ya bud'e kopar bayan ta, kai kace ba mutum aka bud'e mawa ba don ba alamun wani zai fito, saida aka d'an d'auki lokaci sannan ya zuro da k'afar shi guda mai sanye da wani dakakken bak'in takalmi half cover daga haka bai k'arasa fitowar ba, Hajiya Zainab nata Murmushi ta tunkari Mutanen da suka fito tarbarta Momyn Haisam ta taho suka rungume juna gwanin burgewa kasantuwar fuskar su iri d'aya ce, bayan sun saki juna mutane suka hau gaishe ta ana mata sannu da zuwa wad'anda ma basu santa ba basu san lokacin da suka hau washe baki ba suna mata sannu da zuwa a mutunce take d'aga hannu tana amsawa, k'arasa fitowa Sameer yayi yana sanye da bak'in jeans da top bak'a sai maroon d'in riga a sama mai ma6allai saidai ba'a sanya su ba a bud'e take hakan ya bayyana bakar ta cikin idanun shi na sanye da wani mayen bak'in glass, agogon hannunshi ma bak'a ce saidae daga wurin glass d'in kan yana reflecting maroon d'in cikin agogon kai da gani ba sai an fad'a maka zata yi kud'i ba ga sumar shi da ta sha gyara a kwance, nufar inda su Mom d'in shi ke tsaye yayi yana tafiya cike da izza, yana zuwa ya tsaya a gefen ta Mom d'in su Haisam ta kalle shi da faffad'an murmushi tace "U'r welcome my son" kai kawai ya jinjina mata fuskar shi ba yabo ba fallasa Aunty ma sannu da zuwa tayi mashi to itama d'in dai kai ta samu aka d'aga mata, Laila ce ta matsa gaban shi tana kallon shi da murmushi tace ita bazata yi mashi sannu da zuwa ba sai ya bud'e idanun ta kuma tabbatar ba makancewa yay ba da yake suna d'an shiri dashi, d'age mata gira yay itama ta d'aga mashi tata sai lokacin yanayin fuskar shi ya d'an canza a K'ok'arin shi na yayi murmushi, hannu ya kai ya cire glass d'in tace Yauwa to amman da ya rufe idanu basu ma san ko yana ganin su ba, sannu da zuwa tayi mashi ya d'aga mata kai daga haka ya fara k'ok'arin wucewa ciki yana maida glass d'in all eyes on him nan aka shiga darewa ana bashi hanya har ya shige ciki, a wurin dai da yawa ya tafi da imanin wasu ba kamar yan mata Aunty Mareeya data saki baki tana kallon shi har ya shige ta jinjina kai tace "banga laifin ka ba wllh, ga kyau ga kud'i ga Mulki ai abun da yawa mutum bama zai san lokacin da zai ringa jin izza ba" Feenah dake gefenta ta saki dariya, nufo shiga ciki Her Excellency tay aka bata hanya security d'inta na biye dasu bayan tayi gaba aka rufa mata baya suka shige ciki........
*ASM 080*
~_*✊💋BOSS LADIES WRITERS💋✊*_~
*DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAI JIN KAI*
.........Sameer na shiga cikin parlon ya nufi bene cike da isa ya haye ya nufi part d'in Haisam, bayan sun shigo d'akin Mom d'in su Haisam suka nufa, a parlor d'in ta duk aka zazzauna wasu akan kujeru wasu kuma a k'asa Security detail d'in ta na daga gefe a tsaye, gaisawa aka shiga k'ara yi ana mata an zo lafiya da fara'a take ta amsa ma kowa, bayan wani lokaci ta mik'e tace ma Mom zata shiga ciki ta d'an hutu before ayi sallar Magrib tace mata to Abinci ba, ce mata tayi bata jin yunwa saidai ko yara daga haka ta nufi hanyar Bedroom, dakatawa tay kafin ta shige tace ma security d'in tata ta zauna anan ta huta ta d'an rankwafa tayi mata godiya Mom ta bi bayanta suka nufi cikin Bedroom d'in.
Abbas da Saleem wanda dama yana a Abujar zaune a cikin parlon Haisam Sameer ya turo k'opar ya shigo duk suka d'aga kai suka kalle shi, mik'ewa Abbas yayi da fara'a ya tarbe shi yana mashi sannu da zuwa kai kawai ya d'aga mashi Saleem dai na zaune yana bin su da ido don shima duk tafiyar su d'aya da Sameer d'in sai dai bambancin shi Salim miskilanci ne kawae Sameer kuma banda miskilanci harda izza ta bala'e, gaba d'aya kowa yasan kowa da kuma matsayin baban kowa tsakanin Sameer d'an Governor da Saleem d'an Deputy Governor, sai bayan da Sameer d'in ya zauna ya kai hannu ya cire glass d'in Fuskar shi sannan Salim ya d'an d'aga hannu yace mashi welcome Sameer d'in ya jinjina mashi kai daga haka ya maida idon shi akan Tv yaci gaba da kallon Film d'in da suke kallo, Abbas ne yace mashi Haisam d'in na wanka ne sai lokacin ya bud'e baki can k'asan mak'oshi ya furta Ok, hannu ya kai ya fiddo wayar shi daga cikin trouser pocket d'in shi ya fara latsa ta, bai dad'e da zama ba Haisam d'in ya fito yana sanye cikin k'ananan kaya kaman ko yaushe yana hango Sameer d'in ya d'an bud'a ido alamar mamaki don koda ya jiyo jiniya ya san Mom d'in shi ce amman bai yi zaton harda shi za'a zo ba don ko jiya sunyi Magana yake ce mashi ba zai zo ba yana da uzuri, nufo shi Haisam yayi yana zuwa ya zauna a gefen shi fuskar shi da murmushi ya mik'a mashi hannu tare da fad'in "What a surprise, u'r Welcome Bro" d'an gutsirin murmushi yayi a hankali ya furta mashi thanks, tambayar shi yay amman da yace bazai samu zuwa ba, kaman bazai bashi amsa ba sai kuma ya d'age gira yace to ya zo ko ya koma ne, yar dariya Haisam yay kawai Abbas dai yana ta kallon su da murmushi akan fuskar shi d'an Deputy kuwa tamkar ma bai san dasu a wurin ba,
Misalin k'arfe biyar na yamma lokacin su Fatuu na wurin kunshi dankara dankaran Motoci suka shigo cikin gidan da jiniya nan take aka gane Her Excellency Hajiya Zainab ce ta iso, a gaban Entry Hall na gidan Motocin suka parker nan da nan jama'ar cikin gidan suka fara fitowa wanda suka san itace da wanda ma basu san itace ba kawai jiniyar tasa su fitowa, wani Security ne daga cikin Escort d'inta na Motar gaba ya fito da sauri yazo ya bud'e mata k'opa ta zuro farar kafarta data k'unshi ga wani mayen takalmi golden sanye a k'afar, k'arasa fitowa tay tana sanye da rantsatstsen lace bak'i mai adon green da ratsin golden kad'an, tun daga kunnan ta zuwa wuyanta da yatsun hannunta duk gold ne ta yafa mayafi golden kalar takalmanta da jakarta abun sai dai ace Tubarkallah dama tana d'aya daga cikin Matan gwamnoni da suka san takan gayu, Security detail d'in ta mace ce ta fito tazo bayanta ta tsaya wani daga cikin Escort d'in nata ya nufi Motar dake bayan tata ya bud'e yaran ta ne suka fito cikin shiga ta Alfarma, Mota ta biyun k'arshe wani security d'in ya fito daga cikin Escort d'in Motar baya ya bud'e kopar bayan ta, kai kace ba mutum aka bud'e mawa ba don ba alamun wani zai fito, saida aka d'an d'auki lokaci sannan ya zuro da k'afar shi guda mai sanye da wani dakakken bak'in takalmi half cover daga haka bai k'arasa fitowar ba, Hajiya Zainab nata Murmushi ta tunkari Mutanen da suka fito tarbarta Momyn Haisam ta taho suka rungume juna gwanin burgewa kasantuwar fuskar su iri d'aya ce, bayan sun saki juna mutane suka hau gaishe ta ana mata sannu da zuwa wad'anda ma basu santa ba basu san lokacin da suka hau washe baki ba suna mata sannu da zuwa a mutunce take d'aga hannu tana amsawa, k'arasa fitowa Sameer yayi yana sanye da bak'in jeans da top bak'a sai maroon d'in riga a sama mai ma6allai saidai ba'a sanya su ba a bud'e take hakan ya bayyana bakar ta cikin idanun shi na sanye da wani mayen bak'in glass, agogon hannunshi ma bak'a ce saidae daga wurin glass d'in kan yana reflecting maroon d'in cikin agogon kai da gani ba sai an fad'a maka zata yi kud'i ba ga sumar shi da ta sha gyara a kwance, nufar inda su Mom d'in shi ke tsaye yayi yana tafiya cike da izza, yana zuwa ya tsaya a gefen ta Mom d'in su Haisam ta kalle shi da faffad'an murmushi tace "U'r welcome my son" kai kawai ya jinjina mata fuskar shi ba yabo ba fallasa Aunty ma sannu da zuwa tayi mashi to itama d'in dai kai ta samu aka d'aga mata, Laila ce ta matsa gaban shi tana kallon shi da murmushi tace ita bazata yi mashi sannu da zuwa ba sai ya bud'e idanun ta kuma tabbatar ba makancewa yay ba da yake suna d'an shiri dashi, d'age mata gira yay itama ta d'aga mashi tata sai lokacin yanayin fuskar shi ya d'an canza a K'ok'arin shi na yayi murmushi, hannu ya kai ya cire glass d'in tace Yauwa to amman da ya rufe idanu basu ma san ko yana ganin su ba, sannu da zuwa tayi mashi ya d'aga mata kai daga haka ya fara k'ok'arin wucewa ciki yana maida glass d'in all eyes on him nan aka shiga darewa ana bashi hanya har ya shige ciki, a wurin dai da yawa ya tafi da imanin wasu ba kamar yan mata Aunty Mareeya data saki baki tana kallon shi har ya shige ta jinjina kai tace "banga laifin ka ba wllh, ga kyau ga kud'i ga Mulki ai abun da yawa mutum bama zai san lokacin da zai ringa jin izza ba" Feenah dake gefenta ta saki dariya, nufo shiga ciki Her Excellency tay aka bata hanya security d'inta na biye dasu bayan tayi gaba aka rufa mata baya suka shige ciki........
*ASM 080*
~_*✊💋BOSS LADIES WRITERS💋✊*_~
*DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAI JIN KAI*
.........Sameer na shiga cikin parlon ya nufi bene cike da isa ya haye ya nufi part d'in Haisam, bayan sun shigo d'akin Mom d'in su Haisam suka nufa, a parlor d'in ta duk aka zazzauna wasu akan kujeru wasu kuma a k'asa Security detail d'in ta na daga gefe a tsaye, gaisawa aka shiga k'ara yi ana mata an zo lafiya da fara'a take ta amsa ma kowa, bayan wani lokaci ta mik'e tace ma Mom zata shiga ciki ta d'an hutu before ayi sallar Magrib tace mata to Abinci ba, ce mata tayi bata jin yunwa saidai ko yara daga haka ta nufi hanyar Bedroom, dakatawa tay kafin ta shige tace ma security d'in tata ta zauna anan ta huta ta d'an rankwafa tayi mata godiya Mom ta bi bayanta suka nufi cikin Bedroom d'in.
Abbas da Saleem wanda dama yana a Abujar zaune a cikin parlon Haisam Sameer ya turo k'opar ya shigo duk suka d'aga kai suka kalle shi, mik'ewa Abbas yayi da fara'a ya tarbe shi yana mashi sannu da zuwa kai kawai ya d'aga mashi Saleem dai na zaune yana bin su da ido don shima duk tafiyar su d'aya da Sameer d'in sai dai bambancin shi Salim miskilanci ne kawae Sameer kuma banda miskilanci harda izza ta bala'e, gaba d'aya kowa yasan kowa da kuma matsayin baban kowa tsakanin Sameer d'an Governor da Saleem d'an Deputy Governor, sai bayan da Sameer d'in ya zauna ya kai hannu ya cire glass d'in Fuskar shi sannan Salim ya d'an d'aga hannu yace mashi welcome Sameer d'in ya jinjina mashi kai daga haka ya maida idon shi akan Tv yaci gaba da kallon Film d'in da suke kallo, Abbas ne yace mashi Haisam d'in na wanka ne sai lokacin ya bud'e baki can k'asan mak'oshi ya furta Ok, hannu ya kai ya fiddo wayar shi daga cikin trouser pocket d'in shi ya fara latsa ta, bai dad'e da zama ba Haisam d'in ya fito yana sanye cikin k'ananan kaya kaman ko yaushe yana hango Sameer d'in ya d'an bud'a ido alamar mamaki don koda ya jiyo jiniya ya san Mom d'in shi ce amman bai yi zaton harda shi za'a zo ba don ko jiya sunyi Magana yake ce mashi ba zai zo ba yana da uzuri, nufo shi Haisam yayi yana zuwa ya zauna a gefen shi fuskar shi da murmushi ya mik'a mashi hannu tare da fad'in "What a surprise, u'r Welcome Bro" d'an gutsirin murmushi yayi a hankali ya furta mashi thanks, tambayar shi yay amman da yace bazai samu zuwa ba, kaman bazai bashi amsa ba sai kuma ya d'age gira yace to ya zo ko ya koma ne, yar dariya Haisam yay kawai Abbas dai yana ta kallon su da murmushi akan fuskar shi d'an Deputy kuwa tamkar ma bai san dasu a wurin ba,