← Book details Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 66 OF 211

Sashe 66

Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Haisam ne ya shigo cikin d'akin jin sallama yasa ta d'aga ido ta kallo shi, k'arasowa yay ciki idon shi akanta suna ma juna murmushi, ta gefen inda take ya zagaya ya zauna a bakin gadon ta gaishe dashi ya jinjina mata kai, hannu ya kai ya shafi fuskar ta yace "Ya jikin ki?" tana murmushi tace mashi itafa lafiya lou take jin ta wllh, kai ya d'aga sai kuma yace to ya Baby d'in su tace yana nan lafiya bacci yake yanzu amman d'azun da suna fira yace ta gaishe mashi da Dad, dariya duk sukai yace Baby Boy ne kenan tace tana dai Fata amman duk wanda ta samu tana so ya jinjina mata kai, tambayar shi tay shi mi ya fi so ta haifa tun kan ta rufe baki ya girgiza mata kai yace kamar yadda ta fad'a duk abunda ta haifa zai yi farinciki yana fatan Allah ya k'ara mata lafiya da Babyn yasa ta haihu lafiya tana ta murmushi ta amsa da Amin, hannu ya kai ya jawota jikin shi da sauri ta shiga k'ok'arin kwacewa yay mata wani kallo, d'an yamutsa fuska tay tace mashi Mom take tsoron ta gan su haka, d'age mata gira yay yace in ta gan sun sunyi laifi ne a shagwa6e tace "to ai Hubby da kunya fa ka manta jinya nike" yadda tay Maganar ne yasa shi yin yar dariya har hak'oran shi suka bayyana, jawota yay sosae ya rungumeta a wurin kunnanta ya rad'a mata to Mom d'in bata nan sun fita da Aunty, shiru tay ta d'an ji hankalinta ya kwanta dama lokacin da ta gama sallar isha tana zaune kan prayer mat tana Addu'a taga shigowar ta bata jima ba kuma ta fita bayan ta yafa mayafi, tun bata saki jiki ba har dai ta saki ganin shi ba abunda ya dame shi, Maganar School tay mashi tace ran Wednesday suke komawa, jinjina mata kai yay yace ta bari zasu koma taci gaba da zuwa amman ba yanzu ba sai an d'an k'ara lokaci in ta kama sai ayi Magana can school d'in ta d'aga mashi kai, Wayar shi dake ruk'e a d'ayan hannun shi ya d'ago ya fara daddana ta idon ta akan Wayar, hotunan wasu Motoci ya fara nuna mata tana ta kallo har ya kai k'arshe guda Kusan Goma ne, maida idon shi kan Fatuu yay yace ta gan su ta d'ago ta kalle shi tace eh, tambayar ta yay wacce tayi mata da alamun rashin Fahimta tace bata gane abunda yake nufi ba, shiru ya d'an yi tana ta kallon shi kafin taji yace yana nufin tay choosing wadda take so a ciki, waro ido Fatuu tay da tsananin mamaki take kallon shi shima kallon nata yake da murmushi,

"Amman Saboda mi to zan za6a" ta tambaya da alamun mamaki yace mata Saboda za'a kawo mata ne, k'ara zaro ido tay ta furta "Motar!" Kai ya d'aga mata had'i da d'an lumshe ido a shagwabe tace "ni dai Hubby a'a ka barshi ba duk akwae Motoci ba har acan gidan Hajiya ma" kallon ta kawai yake sam bai yi mamakin jin hakan ba don yasan halin ta kan hakan bata son ya kashe kud'in shi yay mata abu in bai zama dole ba gashi kuma ita ba tambayar shi abu take ba, ganin kallon da yake mata yasa ta fara tura mashi baki ya kai hannu ya d'an matse bakin ta yi d'an sauti alamun taji zafi, sigh yay yace shima kyauta ce zai bata kan wadda ta bashi cike da shagwaba tace to ai ita ba ita ta bashi ba ko Allah ne ya bashi, yana murmushi yace yasan da wannan amman ai a jikinta yake ko, yamutsa fuska ta shiga yi yana murmushi yace mata wannan ce kyauta ta farko da ya fara bata a matsayin su na ma'aurata dole sai ta amsa tace ba ga uban lefen da yayi mata ba nan, ce mata yay Wannan ai ba gift bane tunda ya zama al'ada kuma bashi kadae yayi shi ba, sai shagwaba take mashi kanta na a kan shoulder en shi da alama ma ta manta da inda suke, bud'e mata Motocin yay yace in bata za6a ba bazai ji dad'i ba yayi zaton zatai murna ne ya bata gift in kuma wannan bai mata ba ta fad'i duk abunda take so, da sauri ta kai hannu ta tallabo gefen fuskar shi tace "a'a Hubby naji dad'i wllh kawae naga kaman wannan kyautar tayi girma ne kuma naga akwae Motocin" ce mata yay to su motocin dake akwae d'in nata ne ta girgiza mashi kai yace to yanzu ta za6a sai ya zama itama tana da nata ko, kai ta d'aga mashi tana murmushi har ta maida idanunta akan Motocin sai kuma ta d'ago da sauri tace "amman Aunty Fanan fa?" d'an murmushin gefe yay ya furta banda ita, waro ido tay sai kuma ta hau girgiza kai tace a'a don Allah bazata ji dad'i ba wllh itama gaskiya a bata yana murmushi ya furta Justice for Fanan da sauri ta d'aga kai tace eh, sosae yaji dad'in hakan data yi ta tabbatar mashi da Maganar da tayi mashi na zata taimaka mashi yayi masu Adalci, ce mata yay kada ta damu Fanan ma nada Mota a can Us ya siya mata ba'a dad'e ba,

"Da gaske?" ta d'age mashi gira shiru yay yana kallon ta, sake ce mashi tay da gaske yake ya siya mata yana murmushi yace "da k'arya" dariya ta saki don tasan wasa yake itama hakanan jan magana yasa ta tambayi da gasken tunda tasan bazai mata k'arya ba, maida idonta tay kan Screen d'in tace to bari ta za6a, gaba d'aya ta rud'e don kowacce ta had'u kama daga Camry, Hyundai, Corolla Mercedes da sauran su, wata Jeep ya bud'e har zai wuce da sauri tace mashi ya tsaya, k'ura ido tay tana kallon ta sosae ta burgeta don dama tana son Mota Jeep kuma tana son farar Mota to itama Jeep d'in fara ce, ganin tana ta kallon ta yasa shi ce mata tayi mata, jimm tay sai kuma ta d'aga ido ta kalle shi ya d'age mata gira alamar ta amsa mashi, kai ta d'aga ya furta Ok da d'an murmushi sai kuma da sauri Fatun tace "amman nawa take?" shiru kamar ba zai yi magana ba slowly yace tunda tayi mata Shikenan ai mi zatai da kud'in ta, a shagwabe tace ita dai ya fad'i mata gaskiya in mutum zai siya Mota ba sai an fad'i mashi kudin ba, dariya yay bai san ranar da zata daina wauta ba, ce mata yay to ita siya zata yi ne,

"eh ai tunda kai zaka siya man to kaman ni zan siya ko" ta k'are Maganar ta d'an tura mashi baki, d'an lumshe mata ido yay ba zato taga ya matso da face d'in shi yay pecking lips d'in nata ta d'an waro ido ya d'ago yana murmushi, rigimar sai ya fad'i mata kud'in Motar taci gaba da yi ya tambayi to mi zatai wai in taji kud'in tace hakanan take so taji, still murmushi yake wasu abubuwan ta kaman Hajiya, ya gane wai wayo take son yi mashi in taji tayi kud'i sosae tace bata son ta, girgiza mata kai yay yace an gama Magana ba sai taji ba shima ba siya yayi ba, k'una k'uni ta fara tana ita dae Allah bata yarda ba tunda shi yace ta za6a to ya fad'i mata kud'in, gaba d'aya yadda take mashi ta tafi da shi sai kallon ta yake dama d'an kwana biyun nan har ya fara jin kewar ta a tare da shi, ganin irin kallon da yake mata ne yasa ta dakata da abunda take suka zuba ma juna ido breathing d'in su na had'uwa, sun d'an d'auki lokaci a haka fuskar Fatuu da d'an murmushi kawai sai gani tay ya matso da fuskar shi ya had'e da tata, had'e lips d'in su yay farko fara k'ok'arin kwacewa tay amman yak'i bata dama daga baya kuma ta biye mashi don itama tayi kewar hakan,
Chapter 66 · 0% Book details