← Book details Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 128 OF 211

Sashe 128

Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 6 min read

"na sani abokina ai rashin dacen mata babbar matsala ce baka ji wak'ar nan da ake ta mace ta gari ba wllh duk abunda aka fad'a a cikinta hakanne da kaga mutum ba natsuwa duk ya firgice to da ka bincika zaka samu bai yi dacen mata bane, yanzu dai look at you kaman ba Mujaheed d'in dana sani ba duk ka fara fita hayyacin ka ko rannan saida nayi maka magana kan ka rage wannan k'asumbar taka wanda a da yaushe ma har wani zai maka magana kan haka" d'an murmushin takaici Mujaheed d'in yayi ba tare daya ce mashi komai ba, shiru suka d'an yi can Mujaheed d'in yace mashi don Allah suna magana da Fauzy har saida Usman ya d'an waro ido jin sunan wadda ya ambata tare da maimaita sunan Fauzy Mujaheed ya jinjina mashi kai, tambayar shi Usman d'in yayi mi zai da lambar tata yace mashi hakanan yana son suyi magana da ita ne zai bata hak'uri don yana tunanin duk abun nan dake faruwa dashi harda hakkinta, d'an murmushi Usaman yayi yasan ba iya dalilin daya sa yake son lambar ta ba kenan, k'ara tambayar shi Mujaheed yay in yana da lambar ta pls ya bashi Usman d'in yace gaskiya baida ita yana tunanin ta canza layi ne don ada suna gaisawa amman yanzu sun dad'e ma basu yi magana ba, tambayar shi yayi to yana ganinta cikin gari haka yace mashi a'a ai bata cika zama a nan ba yanzu Saboda ta koma Katsina wurin Yayarta acan take karatu, shiru Mujaheed yay yasan Yayar tata wato Aunty Mareeya amman bai san a ina take ba a Katsina, daga baya dai sukai sallama ya tafi Usman nata d'an girgiza kai ba yadda bai nuna mashi ba kar ya bar Fauzy don in yayi mata hakan bai kyauta ba amman ya k'i ji k'arshe ma abun ya zamar masu kamar fad'a gashi nan yanzu tun ba'a d'auki lokaci ba sosae ya fara nadama mara amfani. Tun daga wannan lokacin son Fauzy ke ta d'awainiya dashi gashi yayi duk yadda zai yi don ya had'u da ita ko kuma ya samu lambarta abun yaci tura, Wata rana ne kwatsam ya ganta a bakin titi duk yadda yaso ta tsaya ta saurare shi ta k'iya hakan yasa Ranar ya bi bayanta gida da daddare aikuwa yana zuwa suka had'e da Mahaifinta ya same shi yay mashi tatas yace Idan ya k'ara ganin shi a k'opar gidan shi to hukuma ce zata raba su nan Mujaheed d'in yayi ta bashi hak'uri yana fad'in yasan yayi kuskure bai kyauta ba amman don girman Allah ya bashi dama a yanzu zai gyara kuskuren shi ne, a lokacin wani murmushin yaro yaro ne mahaifin nasu yay kafin ya d'aga yatsa sama yace mashi "Na rantse da Allah daya hallicce ne ko bayan ba raina bazaka auri Fauziyya ba, yarinyar da kaso kashe man ita kawai don Allah yasa da sauran numfashinta a gaba shine yanzu don baka da kunya ka iya tako k'afafun ka kazo man gida, to bari kaji, ka bar kopar gidan nan tunda arzuki in ba haka ba....ka jira in shiga in fito zaka ga abun da zan sa ayi maka" cike da 6acin rai ya k'arasa maganar tare da juyawa ya shige cikin gidan, jiki a sa6ule Mujaheed ya juya ya nufi Motarshi yana k'walla ya bud'e ya tafi, duk wannan abun Fauzy bata san da an yi ba, tun daga ranar Mujaheed ya hak'ura da neman Fauzy amman fa kullum son ta da nadamar abunda yayi mata k'aruwa yake a cikin ran shi, (Allah ka kiyashe mu aikin dana sani mara amfani Amin).

Yana zaunen idon shi akan Tv wayar shi dake a gefen shi ta shiga yin ruri, kai idon shi yay kanta yaga Usman ne mai kiran nashi ya kai hannu ya d'aukko ta tare da yin picking, bayan sun gaisa ne yace mashi yaga hotunan dake ta trending a social media Mujaheed d'in yace mashi a'a tun d'azun rabon shi da online Usman yace mashi Ok ya hau Facebook yanzu tambayar shi yay lafiya yace ya dai hau zai gani yace Ok, bayan ya katse Wayar kunna Data d'in shi yayi a ranshi yana ta raya to miye zai gani, yana hawa hotunan su Fauzy ya ci karo dasu farko bai ganeta ba koda ya karanta rubutun dake sama wanda aka sa d'an Governor d'in Nasarawa Sameer Bello Abdullahi zai yi Wuff da yar talakawa daga jahar Katsina a garin Funtua mai suna Fauziyya Ahmad Rufa'i, shiga yay cikin uban comments d'in mutane ya fara bi yana karantawa duk da hakan bai gane ita bace yana cikin karantawar Usman ya sake kiran shi bayan ya d'aga yace mashi yaga wadda zata auri d'an Governor d'in yace mashi eh ya gani ance yar nan Funtua ce wannan maganar yasa Usman ya gane bai ganeta ba yace "wai baka gane Amaryar bane?" Amsa ya bashi da eh da alamun mamaki Usman yace "lallai Mujaheed baka a cikin hayyacin ka wllh, yanzu Fauziyya d'in ce baka gane ba?" jin sunan Fauziyya yasa shi maimaita sunan sai lokacin hankalin shi ya koma kan sunan Amaryar da ya gani an rubuta nan take ya gane Fauzy ce, wani irin bugu gaban shi yayi da sauri ya mik'e tsaye.........

96

_ASM BY ZAINAB BATURE_

~_*✊💋BOSS LADIES WRITERS💋✊*_~

............Da tsananin Al'ajabi Mujaheed yace "U.....sman wai kana nufin Fauziyyata ce wannan Amaryar?" Amsa ya bashi da eh mana bai duba hoton bane sosae, kan Mujaheed ne ya d'aure fuska a hautsine ya shiga fad'in amman taya hakan zata faru taya za'a ce zata auri d'an Governor, Usman na murmushi yace abun Allah ai ba abun mamaki bane don wannan kad'an daga cikin ikon sane,

"ka gane Usman abunda nike nufi irin wannan Mutanen had'uwa da su ba abu ne mai sauk'i ba balle kuma har ta kaiga ace zasu yi aure kuma nasan labarin mahaifin yaron ba K'aramin mai kud'i bane yana daga cikin Governors masu kud'in gaske fa taya za'a ce hakan zai faru kodai ba ita bace suna ne yazo d'aya!" hankali tashe yake Maganar,

"Wannan duk ba wani abu bane Mujaheed da Allah ya so Shikenan zaka ga ya kasance cikin sauki tunda gaba d'ayan mu duk bayin sane shi yake iko da mu" yarfa hannu Mujaheed yay kaman zai saka kuka yace amman wai taya suka had'u ma, Usman yay yar dariya yace "ta yadda Allah ya had'a ku haka shima ya had'a su, ance ta dalilin karatun da take a Katsina suka had'u ni kaina nayi mamaki sosae lokacin da naga hotunan don ina gani na gane itace amman don in tabbatar sai na kira wani abokina d'an layin su shine ya tabbatar man yace suma duk basu san da abun ba kawai dai suna ganin ana yin manyan bak'i a gidan sannan kuma yanzu haka ma an canza ma gidan nasu suffa ya zama had'addan ginin benen gaske gaba d'aya dai komai cikin k'ank'anin lokaci ya faru har ma hoton gidan nasu ya turo man bari ka gan shi" yana fad'in hakan ya katse kiran don ya tura mashi hoton, komawa Mujaheed d'in yay cikin Facebook ya shiga sake kallon hotunan gaban shi na mashi wani irin bugu, sai yanzu ya tabbatar da ita d'in ce yana haka Usman ya turo mashi hoton gidan su Fauzy, Safa da Marwa ya shiga yi wayar shi ruk'e a hannunshi da k'yar yake fitar da numfashin shi da yaji yana neman k'wace mashi k'arshe ma sai yay wurgi da wayar tashi ya durk'ushe k'asa saman gwiwowin shi wasu irin k'walla masu zafi suka shiga zubo mashi..........
Chapter 128 · 0% Book details