Sashe 159
Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 6 min read
Washe gari da Asuba Fatuu ta tashi don tayi salla su Aysha da Safnah ma da suka kwana anan ta tashesu, bayan duk sun gama komawa sukai suka kwanta don kowa a gajiye yake gashi yau su Safnah zasu tafi dasu Gwaggo amman banda Fatuu don Haisam yace nan zata tsaya, Fatuu bata daɗe da komawa ba har ta fara yin gyangyaɗi wayarta ta fara ringing ta kai hannu gefen filo ta ɗaukkota, koda taga mai kiran nata da alamun mamaki ta maimaita sunan Nameer a hankali ta furta "to lafiya???" gabanta har ɗan faɗuwa yake tay picking tare da ƙoƙarin tashi zaune, sallama tayi jin shiru bai yi magana ba bayan ta ɗaga sannan ya amsa ya gaishe da ita muryar shi ƙasa ƙasa bata ji komai ba don ya saba gaishe da ita, bayan ta amsa shiru yay bai ƙara cewa komai ba itama shirun tay tana jin fargabar abunda yasashi kiranta a wannan lokacin, jin baida niyyar magana yasa tace "Nameer lafiya kuwa ka kira kuma naji kayi shiru" tana jin sautin yar ajiyar zuciyar da yayi a hankali yace mata dama Don Allah wani taimako yake son tayi mashi da sauri tace to wane taimako taji yace zai zo ya ɗauketa yanzu in ba damuwa zasu je gidan shi, bugun da gabanta ke yi ne ya ƙaru cike da fargaba har muryarta ta bayyana tace mashi to amman lafiya kuwa shiru ya ɗan yi kafin yace mata lafiya lou ba wani abu bane Minon ce har yanzu keta kuka shine yake son taje ta rarrasheta, shiru Fatun ta ɗan yi tana juya abunda yace a ranta lokaci guda kuma zuciyarta ta raya mata wani abu da sauri tace mashi to yazo ya ɗauketan yace Ok gashi nan ma ya taho don Allah ta fito bakin entry hall da yazo sai su tafi bai son wani ya ganshi tay ɗan murmushi tace to, bayan sun gama wayar Haisam ta kira tana fara yin ringing ya ɗauka saida ta gaidashi sannan ta faɗi mashi zancen zuwa ɗaukarta da Nameer zai yi ya tambayeta lafiya tace haka yace mata lafiya lou Minon ce keta Kuka dama jiyan da ƙyar suka rabu yace Ok kafin yace ina su Abie tace bari ta kawo su nan wurin shi kafin ta dawo, Abie ta fara ɗaukkowa ta nufi part ɗin shi tana zuwa bakin benen suka haɗe da Haisam ɗin ya amshe shi ta juyo don ta ɗaukko Adam, sauri sauri ta canza kaya zuwa jallabiya tay rolling veil ta ɗauki purse bayan ta saka wayarta ta nufi ƙopar fita, tana fitowa daidai Motar Nameer ɗin na ƙarasowa yana tsayawa ta nufi gaba ta buɗe bayan ta shiga yaja suka tafi, yana sanye da brown ɗin jallabiya mai gajeran hannu gaisawa suka ƙara yi ba tare da ya kalleta ba daga haka basu ƙara cewa komai ba har suka ƙaraso gidan bayan an buɗe masu gate ya shiga a gaban entry hall ya parker Motar kusan a tare suka fito ya zagayo inda take ya ɗan kalleta tare da ce mata suje suka jera, saida yasa makulli ya buɗe kopar sannan suka shiga parlon tsaf dashi sai sanyin Ac mai haɗe da ƙamshi ke tashi, hanyar Bedroom ɗin suka nufa suna zuwa bakin corridor ɗin ya tsaya ta kalle shi yace mata ta shiga tana nan ciki, tambayar shi tayi a wane ɗaki take yace wanda suka barta jiya ta ɗaga kai tare da juyawa ta shige cikin corridor ɗin, a hankali ta tura kopar gabanta na faɗuwa ta leƙa kai, acan saman gado ta hango Mino ta takure guri guda jikinta lullu6e da duvet, a hankali tayi sallama ta shiga shiru Minon bata motsa ba ta nufi gadon, zama tayi a baki idonta a kanta har lokacin gabanta faɗuwa yake, kiran sunan Minon tayi shiru bata amsa ba hakan yasa ta ƙara ɗaga murya ta kirata lokacin Minon ta yaye duvet ɗin da sauri, koda Fatuu tay arba da fuskarta wani irin bugu da ƙarfi gabanta yay ganin yadda fuskar tay jajir ga idanuwanta duk sun kumbura haka la66anta ma sun ɗan kumbura sunyi ja kamar jini ya kwanta, yaye duvet ɗin tayi da sauri ta nufo Fatuu tana zuwa ta faɗa jikinta ta fashe da matsanancin kuka har sai da Fatuu ta ɗan runtse ido jin yadda jikin Minon yay zafi sosai, cikin fullanci take mata Magiyar don Allah ta tafi da ita gida kada ta sake barinta anan mutuwa zatayi gaba ɗaya a gigice take hakan yasa Fatuu ruɗewa ta ɗagota Fuska a yamutse take ce mata mi ya faru ta faɗi mata cikin kuka take faɗin Ya Nameer ne bai sonta mugu ne shi ashe bata ga abunda yayi mata ba so yake ya kasheta, cikin sheshsheka take Maganar jikinta sai 6ari yake Fatuu tay shiru ta bita da ido sosae take jin mamakin Maganar Mino a cikin ranta ta shiga raya badai Mino bata san miye aure ba, maidata tayi jikinta ta shiga ɗan bubbuga bayanta alamar rarrashi tana faɗin tayi shiru to in dai tana son ta tafi da ita ɗin aikuwa sai gashi ta daina sai ajiyar zuciya da take saukewa a jere, ɗagota Fatuu tay tana ɗan murmushi ta shiga goge mata ƙwallan fuskarta bayan ta gama bin ta tayi da kallo ta rasa ta ina ma zata fara fahimtar da ita can tace mata a Makarantar su ba'ayi masu bayani kan Aure ba, cikin disashshiyar murya Mino ta tambayeta islamiyya ko boko Fatun tace mata duka tace a islamiyya ana yi masu wa'azi kan mata ta rinƙa yima mijinta ladabi da biyayya kuma ta rinƙa nuna mashi soyayya sannan in ta haihu taba yaran tarbiyya mai kyau sannan a Boko a islamic studies anyi masu bayanin minene aure da kuma yadda ake yin shi, kai Fatuu ta jinjina kafin tace to ba'a yi masu bayanin yadda ake haihuwa ba tace anyi masu a cikin Biology a Reproduction Fatun ta tambayeta ma'anar shi ta faɗi mata harda ire iren shi, gyara zama Fatuu tayi don anzo inda take so cikin types ɗin ta tambayeta wanda ya shafi abunda take son ta sani tace tayi mata bayanin shi ta shiga yi mata tiryan tiryan, murmushi Fatuu tay tace to bata san haɗuwar da ake nufi in mace da namiji sun yi ba ake samun cikin da ta faɗa Minon tace mata ana nufin in akayi aure aka cigaba da soyayya, jinjina kai Fatuu ta shiga yi don ta fahimci da gaske Minon bata fahimci abunda ake nufi ba,
"Ba daga anyi aure ana soyayya ba ake samun ciki ba tunda in hakane ai kafin kuyi auren kuna soyayya miyasa baki samu ba, abunda ya faru tsakanin ki da Nameer shi ake nufi da in mace da namiji sun haɗu don haka ba laifi yayi ba, hakan kusan shine auren ma dole sai ana hakan zaki samu ciki kuma duk lokacin da hakan ya faru tsakanin ku lada zaku samu",
yamutsa Fuska Minon ta shiga yi idanunta cike da ƙwalla murya na rawa tace "amman Adda Fatuu da wuya fa sosae wllh har matuwa nayi na dawo" tana kai Maganar ta fashe da kuka kasa daurewa Fatuu tay saida tayi yar dariya tace ta suma dai ana mutuwa a dawo ne, Kuka sosae Minon keyi Fatuu ta zura mata ido bata ji mamaki sosae ba don tasan akwai ƙarancin wayewa a tattare da Mino gashi ita ba mai shiga mutane bace sosae kuma bata da shige ma ƙawaye wani lokacin kamar miskila haka take, ajiyar zuciya Fatuu ta sauke ta dafata tana faɗin to miye abun kuka ai ba ta dingi jin zafin ba kenan daga yanzu bazata ƙara ji ba, duk da haka taƙi daina yin kukan sai faɗin Allah bazata iya ba da wuya take,
"Ba daga anyi aure ana soyayya ba ake samun ciki ba tunda in hakane ai kafin kuyi auren kuna soyayya miyasa baki samu ba, abunda ya faru tsakanin ki da Nameer shi ake nufi da in mace da namiji sun haɗu don haka ba laifi yayi ba, hakan kusan shine auren ma dole sai ana hakan zaki samu ciki kuma duk lokacin da hakan ya faru tsakanin ku lada zaku samu",
yamutsa Fuska Minon ta shiga yi idanunta cike da ƙwalla murya na rawa tace "amman Adda Fatuu da wuya fa sosae wllh har matuwa nayi na dawo" tana kai Maganar ta fashe da kuka kasa daurewa Fatuu tay saida tayi yar dariya tace ta suma dai ana mutuwa a dawo ne, Kuka sosae Minon keyi Fatuu ta zura mata ido bata ji mamaki sosae ba don tasan akwai ƙarancin wayewa a tattare da Mino gashi ita ba mai shiga mutane bace sosae kuma bata da shige ma ƙawaye wani lokacin kamar miskila haka take, ajiyar zuciya Fatuu ta sauke ta dafata tana faɗin to miye abun kuka ai ba ta dingi jin zafin ba kenan daga yanzu bazata ƙara ji ba, duk da haka taƙi daina yin kukan sai faɗin Allah bazata iya ba da wuya take,