Sashe 68
Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 6 min read
"Ba abunda ya faru saidai matsalar ake k'ok'arin janyo mata a an k'i barinta ta huta kamar yadda likita ya bada doka" fuska a kwa6e ta k'arasa Maganar, har saida gaban Mom ya d'an fad'i a ranta ta shiga tunanin to mi take ma Fatuu da zata ce haka ita a iya saninta tana hutawa yadda yakamata amman gashi tace wai an k'i barinta ta huta , tana cikin zancen zucin ta ji Hajiyar taci gaba da fad'in "in banda jarabar tsiya k'iri k'iri fa yasan halin da yarinyar nan take ciki amman yaje ya bi ya kaddadabe ta shiyasa na maido ta nan ai sai in ga ta yadda zai rink'a zuwa wurin nata balle har ya takura mata" har saida Mom ta d'an ji sanyi don ta fahimci wanda yay laifin, d'an murmushi tay ta bata hak'uri Hajiyar tace Uhm kawai, mik'ewa Mom tay tayi mata saida safe cikin sakin fuska Hajiyar ta amsa mata ta tafi,
Misalin k'arfe goma da yan mintuna Senator ya shigo part d'in har lokacin Hajiyar na zaune a parlor tana kallo, amsa mashi sallamar da yayi tay idon ta a kanshi ya k'araso cikin parlon, zama yayi akan kujera gefen tata cike da girmamawa ya d'an sunkuyar da kai ya gaishe da ita tana murmushi ta amsa tay mashi an dawo yace eh, Ledar hannun shi ya mik'a mata yace ga furar ta, amsa tayi tay mashi godiya da sa Albarka ya amsa har zai yi magana ta riga shi fad'in da yayi ta wahalar siyo mata Furar kullum mi zai hana ya rink'a siyo ta kwana biyu tunda ga fridge nan sai ta saka, yana yar dariya yace mata ai ba abun wahala bane yafi son tana shan fresh ba wadda ta kwana ba kuma ai ba shi yake siyowa ba kawai dai shi yana shigowa da ita ne, jinjina kai tay alamar gamsuwa sai kuma ya k'ara cewa shi d'in ma zai iya zuwa ya rink'a siyo mata ai tunda neman Albarka yake, dariyar jin dad'i tay tace mashi wannan kullum cikin samunta suke koda ba furar saidae kuma don samun lada tunda tana jin dad'inta yana murmushi ya jinjina mata kai, d'ayar ledar ya d'ago yace ga ta Daughter nan yaje part d'in Mom ya kai mata aka ce ta dawo nan Hajiyar ta ce eh neman hanata ake ta bi dokar likita shiyasa ta maido ta nan, jinjina kai yay yana murmushi don Mom ta fad'i mashi komai, mik'ewa yay yace bari ya d'aukko mata cup tasha ko ta bi jiki tace mashi to ai taga ma kamar bata lalata ciki, d'an fridge d'in cikin parlon ya nufa ya bud'e bayan ya d'aukko cup d'in ya dawo wurinta da kanshi ya ciro robar furar ya zuba mata, bayan ta fara sha ya d'auki d'ayar ledar yace bari ya kaima Daughter d'in Hajiyar tace Allah yasa ma bata yi bacci ba saida tace mata in zatai kallo ta fito tace a'a kwanciya zatai, Bedroom d'in ya nufa saida yay sallama sau biyu sannan k'asa k'asa ya jiyo Muryarta tana amsawa, shiga yay Fatuu data d'ago kai tana ganin shi da sauri ta tashi zaune dama a kishingid'e take suna chat da Haisam da kuma Fauzy, cikin d'akin ya shigo ya tsaya daga gaban gadon da fara'a take kallon shi ta gaishe da shi, amsa mata yay ya tambayi ya yanayin jikin nata tace mashi lafiya lou ya jinjina kai, matsawa yay ya mik'a mata ledar yace to ga furar ta sai ta sha da sauri ta kawo duka hannuwanta ta amsa tay mashi godiya, saida safe yay mata ya juya ya tafi.
Wuraren k'arfe sha d'aya da rabi Fanan ta gama shiryawa cikin had'add'iyar rigar bacci lokacin Laila tayi bacci, gaban dressing mirror ta nufa ta kwance gashinta ta fara gyara shi, bayan ta gama ta hau yan shafe shafe da feshe feshen turarurruka, press ta nufa bayan ta bud'e ta fiddo after dress cikin kayanta data jera, d'aura ta tay a saman rigar baccin tata da iyakar ta gwuiwa ta yafa veil d'in asaman kanta daga haka ta nufi hanyar k'opa, saida ta saka flat shoe dake a bakin k'opar sannan ta bud'e ta fuce, part d'in Haisam ta nufa bayan taje can ta cire rigar saman. Da Asuba bayan ya dawo daga Masallaci lokacin itama ta gama salla har ta koma ta kwanta, jikin shi sanye da farar jallabiya ya hau gadon idonta akan shi tana mashi murmushi ta gaishe da shi yay mata ta tashi lafiya ta amsa mashi, matsowa tay ta d'aura kan ta a saman chest din shi nan take mashi Maganar aikinta tace sunyi waya da Dad d'inta jiya yake tambayar yaushe zata koma don hutun data d'auka ya k'are har anyi mashi magana, shiru Haisam d'in yay kamar mai nazarin wani abu har saida ta d'aga kai ta kalle shi, ce mata yay nan da 2 weeks shima zai koma yana ganin in ba matsala ta bari sai su tafi tare tace Ok zata ma Dad d'in ta magana sai a k'ara mata hutun ya jinjina mata kai sai kuma ta k'ara mashi Maganar tafiyarta Lagos idon ta akan shi, d'age mata gira yay yace tana sauri ne tana murmushi tace a'a, ce mata yay ta bari ta k'ara ko 1 week tana murmushin jin dad'i tace to.
Sam Fatuu bata wani laulayin ciki ba kamar wanccan data samu ba wannan cikin bata wani ciwo kuma komai ci take gashi sosae cin Abincin ta ya k'aru, kawai wani lokacin in taji k'amshin da bai mata ba take jin zuciyar ta ta d'an tashi sai kuma in taci Abinci wani lokacin nan ma tana jin tashin zuciyar har ta d'an yi amai shima zata iya k'irga sau nawa tayi. Gaba d'aya Hajiya ta kasa ta tsare tun abun bai damun Fatuu har ta fara shiga damuwar hakan ba kamar data ga har lokacin Fanan na a gidan kuma dai tasan dole wani abu na shiga tsakanin ta da Haisam, Haisam d'in na yawan zuwa duba ta sai dae bata wani sakewa da shi koda yazo Hajiyar bata a cikin d'akin d'an bayan lokaci take shigowa tace yazo ya wuce ya bata wuri, kullum daga kwanciya sai kallo sai latsa waya ko main parlor bata cika zuwa ba Saboda a ranakun aiki yan gidan ma ba zama suka cika yi ba a parlon. Bayan sati d'aya ranar asabar Fanan ta tafi dama Hajiya Maryam nata k'orafin ta maido mata yarinya ta hanata zuwa School, bayan tafiyar Fanan su Laila da Nameer suma suka fara shirin tafiya, ranar laraba Laila ta tafi Malaysia Nameer kuma Haisam yace ya bari su tafi tare tunda a can yake karatun dama, gaba d'aya Fatuu ta k'ara shiga takura dama dasu Fanan d'in take yin hira wani lokacin ga damuwar tafiyar da Haisam zai yi ranar Sunday zaije Lagos daga can ran Monday zasu tafi, sosae Fatuu ta shiga damuwa don in tace bata buk'atar mijinta to tayi k'arya ba kamar in ta tuna zai tafi tare da Fanan sai zuciyarta tay ta raya mata zasu je can suyi ta shan soyayyar su,
Ranar Friday da yamma gaba d'aya Fatuu tunanin yadda zata je part d'in Haisam take tana haka dubara ta fad'o mata, tana sanye da riga da skirt na lace ta nufi cikin Bedroom lokacin Hajiya na zaune tun bayan data gama sallar la'asar take tasbih, daga gefenta d'an nesa da ita ta zauna akan carpet ta shiga yin wasa da yatsunta na k'afa, bata dad'e da zama ba taji Muryar Hajiyar tana tambayarta ya kai, shiru tay ta fara motsa baki da k'yar murya na d'an rawa tace mata dama tazo tambayar ta ne Ya Haisam ne yace taje ta had'a mashi kaya tay wuri wuri da ita ta k'arasa Maganar, bin ta da ido Hajiya tay ta shiga yan kame kame,
Misalin k'arfe goma da yan mintuna Senator ya shigo part d'in har lokacin Hajiyar na zaune a parlor tana kallo, amsa mashi sallamar da yayi tay idon ta a kanshi ya k'araso cikin parlon, zama yayi akan kujera gefen tata cike da girmamawa ya d'an sunkuyar da kai ya gaishe da ita tana murmushi ta amsa tay mashi an dawo yace eh, Ledar hannun shi ya mik'a mata yace ga furar ta, amsa tayi tay mashi godiya da sa Albarka ya amsa har zai yi magana ta riga shi fad'in da yayi ta wahalar siyo mata Furar kullum mi zai hana ya rink'a siyo ta kwana biyu tunda ga fridge nan sai ta saka, yana yar dariya yace mata ai ba abun wahala bane yafi son tana shan fresh ba wadda ta kwana ba kuma ai ba shi yake siyowa ba kawai dai shi yana shigowa da ita ne, jinjina kai tay alamar gamsuwa sai kuma ya k'ara cewa shi d'in ma zai iya zuwa ya rink'a siyo mata ai tunda neman Albarka yake, dariyar jin dad'i tay tace mashi wannan kullum cikin samunta suke koda ba furar saidae kuma don samun lada tunda tana jin dad'inta yana murmushi ya jinjina mata kai, d'ayar ledar ya d'ago yace ga ta Daughter nan yaje part d'in Mom ya kai mata aka ce ta dawo nan Hajiyar ta ce eh neman hanata ake ta bi dokar likita shiyasa ta maido ta nan, jinjina kai yay yana murmushi don Mom ta fad'i mashi komai, mik'ewa yay yace bari ya d'aukko mata cup tasha ko ta bi jiki tace mashi to ai taga ma kamar bata lalata ciki, d'an fridge d'in cikin parlon ya nufa ya bud'e bayan ya d'aukko cup d'in ya dawo wurinta da kanshi ya ciro robar furar ya zuba mata, bayan ta fara sha ya d'auki d'ayar ledar yace bari ya kaima Daughter d'in Hajiyar tace Allah yasa ma bata yi bacci ba saida tace mata in zatai kallo ta fito tace a'a kwanciya zatai, Bedroom d'in ya nufa saida yay sallama sau biyu sannan k'asa k'asa ya jiyo Muryarta tana amsawa, shiga yay Fatuu data d'ago kai tana ganin shi da sauri ta tashi zaune dama a kishingid'e take suna chat da Haisam da kuma Fauzy, cikin d'akin ya shigo ya tsaya daga gaban gadon da fara'a take kallon shi ta gaishe da shi, amsa mata yay ya tambayi ya yanayin jikin nata tace mashi lafiya lou ya jinjina kai, matsawa yay ya mik'a mata ledar yace to ga furar ta sai ta sha da sauri ta kawo duka hannuwanta ta amsa tay mashi godiya, saida safe yay mata ya juya ya tafi.
Wuraren k'arfe sha d'aya da rabi Fanan ta gama shiryawa cikin had'add'iyar rigar bacci lokacin Laila tayi bacci, gaban dressing mirror ta nufa ta kwance gashinta ta fara gyara shi, bayan ta gama ta hau yan shafe shafe da feshe feshen turarurruka, press ta nufa bayan ta bud'e ta fiddo after dress cikin kayanta data jera, d'aura ta tay a saman rigar baccin tata da iyakar ta gwuiwa ta yafa veil d'in asaman kanta daga haka ta nufi hanyar k'opa, saida ta saka flat shoe dake a bakin k'opar sannan ta bud'e ta fuce, part d'in Haisam ta nufa bayan taje can ta cire rigar saman. Da Asuba bayan ya dawo daga Masallaci lokacin itama ta gama salla har ta koma ta kwanta, jikin shi sanye da farar jallabiya ya hau gadon idonta akan shi tana mashi murmushi ta gaishe da shi yay mata ta tashi lafiya ta amsa mashi, matsowa tay ta d'aura kan ta a saman chest din shi nan take mashi Maganar aikinta tace sunyi waya da Dad d'inta jiya yake tambayar yaushe zata koma don hutun data d'auka ya k'are har anyi mashi magana, shiru Haisam d'in yay kamar mai nazarin wani abu har saida ta d'aga kai ta kalle shi, ce mata yay nan da 2 weeks shima zai koma yana ganin in ba matsala ta bari sai su tafi tare tace Ok zata ma Dad d'in ta magana sai a k'ara mata hutun ya jinjina mata kai sai kuma ta k'ara mashi Maganar tafiyarta Lagos idon ta akan shi, d'age mata gira yay yace tana sauri ne tana murmushi tace a'a, ce mata yay ta bari ta k'ara ko 1 week tana murmushin jin dad'i tace to.
Sam Fatuu bata wani laulayin ciki ba kamar wanccan data samu ba wannan cikin bata wani ciwo kuma komai ci take gashi sosae cin Abincin ta ya k'aru, kawai wani lokacin in taji k'amshin da bai mata ba take jin zuciyar ta ta d'an tashi sai kuma in taci Abinci wani lokacin nan ma tana jin tashin zuciyar har ta d'an yi amai shima zata iya k'irga sau nawa tayi. Gaba d'aya Hajiya ta kasa ta tsare tun abun bai damun Fatuu har ta fara shiga damuwar hakan ba kamar data ga har lokacin Fanan na a gidan kuma dai tasan dole wani abu na shiga tsakanin ta da Haisam, Haisam d'in na yawan zuwa duba ta sai dae bata wani sakewa da shi koda yazo Hajiyar bata a cikin d'akin d'an bayan lokaci take shigowa tace yazo ya wuce ya bata wuri, kullum daga kwanciya sai kallo sai latsa waya ko main parlor bata cika zuwa ba Saboda a ranakun aiki yan gidan ma ba zama suka cika yi ba a parlon. Bayan sati d'aya ranar asabar Fanan ta tafi dama Hajiya Maryam nata k'orafin ta maido mata yarinya ta hanata zuwa School, bayan tafiyar Fanan su Laila da Nameer suma suka fara shirin tafiya, ranar laraba Laila ta tafi Malaysia Nameer kuma Haisam yace ya bari su tafi tare tunda a can yake karatun dama, gaba d'aya Fatuu ta k'ara shiga takura dama dasu Fanan d'in take yin hira wani lokacin ga damuwar tafiyar da Haisam zai yi ranar Sunday zaije Lagos daga can ran Monday zasu tafi, sosae Fatuu ta shiga damuwa don in tace bata buk'atar mijinta to tayi k'arya ba kamar in ta tuna zai tafi tare da Fanan sai zuciyarta tay ta raya mata zasu je can suyi ta shan soyayyar su,
Ranar Friday da yamma gaba d'aya Fatuu tunanin yadda zata je part d'in Haisam take tana haka dubara ta fad'o mata, tana sanye da riga da skirt na lace ta nufi cikin Bedroom lokacin Hajiya na zaune tun bayan data gama sallar la'asar take tasbih, daga gefenta d'an nesa da ita ta zauna akan carpet ta shiga yin wasa da yatsunta na k'afa, bata dad'e da zama ba taji Muryar Hajiyar tana tambayarta ya kai, shiru tay ta fara motsa baki da k'yar murya na d'an rawa tace mata dama tazo tambayar ta ne Ya Haisam ne yace taje ta had'a mashi kaya tay wuri wuri da ita ta k'arasa Maganar, bin ta da ido Hajiya tay ta shiga yan kame kame,