Sashe 36
Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Lokacin da akai Sallar juma'a hidima ta kan kama bak'i yan Walima tuni sun fara zuwa, bayan an yi salla mai makeup tazo lokacin Fatuu na d'akin Laila ta shirya cikin dandatsetsen lace Swarovski d'an dubu d'aruruwa anyi mata d'inkin riga da skirt tasa su sark'ar diamond abun ba'a magana jikin Fatuu ya zama kud'i ko ince kud'ad'e, ba 6ata lokaci aka fara mata bridal Makeup d'in, tun ana cikin yi ake aikowa kiranta daga d'akin Mom don tazo a ganta, Laila ce ta kira Mom d'in nasu ta sanar mata ana mata kwalliya ne in aka gama zata kawo ta, Jama'a kuzo kuga Fatuu ya fillo don Allah ni Saboda kallon ta ma har saida Alk'alami na ya fad'i, abun sai dai ace Tubarakallah Ma sha Allah an k'ara jik'a kyau da ruwan Naira abun ba'a magana, Nan aka shiga yi mata hotuna harda su Video mai makeup d'in ma tana ta mata don ta d'aura a handles d'inta na social media gashi da yake Fatun a wayancenta take abun sai ya tsaru sosae, ana cikin yi Jidderh ta shigo tasha ankonta an mata yar Arzik'in Fitted gown (bana ce matsiyaciya ba😂) sosae d'inkin ya had'u an tsara shi da mix and match d'in ta fito a yar matan Abuja, ce ma Aunty Laila tayi Mom tace a kawo ta hakanan Friends d'inta ne zasu ganta, wani had'add'an gele mai shara shara ana ganin komai na jikin mutum baida girma sosae ta d'aukko ta yafa mata tasa takalma nasu tsini sosae hannun ta ruk'e da yar purse d'in su Laila ta kama hannunta suka tafi,
bayan sunje a parlor suka tsaya Mutanen ciki suka hau yabon gayun Amarya daga baya ta wuce da ita cikin Bedroom, duk k'awayen Mom ne a ciki wasu anko ne a jikin su na full embroidery har Hajiya Zainab ma da Mom ankon ne a jikin su anyi masu dogayen riguna sunyi kyau abun har ba'a magana, harda Hajiya Kubra ta Comment section a cikin su ashe itama mutuniyar First Lady ce tasha anko full embroidery, ciki Laila ta shiga da ita Jidderh ma na biye da su, bin su d'aya bayan d'aya ta shiga yi da Fatun suna ganinta tana gaishe dasu sai yabon kyaun ta suke nan aka shiga bata kyautar kud'i Laila na amsar mata harda wadda ta bata kyautar yan kunnan zinari ita dai Fatuu sai murmushi kawai take bakin ta ya mutu abun ya girmi tunanin ta, abun mata sai ya zama kamar gasa ma, ita Hajiya Zainab Account details d'in Fatun tace abata aka sa sowa ana mata kirari sai murmushi take daga baya aka kaita wurin Mom ta zaunar da ita kusa da ita a hankali Fatuu ta gaisheta tana murmushi tace "Ma sha Allah Daughter kin yi kyau" tace mata ta gode, bayan sun gama da nan Laila ta fito da ita suka nufi part d'in Hajiya daga nan kuma bayan sun fito baya suka nufa gaba d'aya rud'ewa su kai da ganin yadda Fatuu ta had'u, anan Laila ta barta ta tafi itama ta shirya don duk kusan kowa ya saka ankon shi kowa ka gani atamfar tayi mashi kyau daga bak'ak'en har fararen, sosae Fauzy da Mino suka yi kyau ita Fauzy fitted gown ce Mino kuma riga da skirt, su Aunty Mareeya da Feenah duk dogayen riguna aka masu styles masu kyau kalar na yan Abuja Fanan itama fitted gown aka mata sosae tayi kyau gashi a jikin atamfar akwae kalar gashinta, da Laila zata tafi ta bita don ayi mata makeup itama.
Da lokacin cin Abinci yayi a parlor aka shiga jerawa saman Dining tables an k'ara wasu guda ukku suma masu cin mutum sha biyu sai aka matsar da set guda na kujeru aka had'e su, Abinci ne kala daban daban sai wanda Mutun ke so sai kuma mutum ya ci ya ture nama kuwa ba don kar inyi k'arya ba sai ince duk tsoka tayi dunkulan hannun mutum in ma bata yi ba to ta kusa🤧 ga kaji Malam, drinks da ruwa su wannan kaman company d'in su ka zo ma, bayan an gama tsara wurin aka je aka sanar ma Mom da Aunty suka fito da Mutanensu aka zazzauna yan baya ma su Aunty Mareeya aka masu magana suka fito, yadikko bata son suje ai kauyanci hakan yasa taje tayi ma gwaggo magana kan in zai yiwu akawo masu nasu can gwaggon ta fahimceta tace to,
Table guda duk k'awayen Mom ne harda Hajiya Zainab Wani kuma Aunty ce da K'awayen ta wanda wasu k'awayen su ne gaba d'aya ita da Mom, a d'ayan table na ukku su Aunty Laila ne harda Amarya Fatuu da K'awayen su sai table na k'arshe nan su Aunty Mareeya suke harda Fanan da wasu yan uwan su yan Daura Ma'aikata nata Serving nasu abun gwanin burgewa kowa harkan gaban shi yake bai damu da yadda wani ke cin Abincin shi ba, a can cikin parlon ma a saman kujeru akwae mutane zazzaune suna cin Abincin, Haisam na part d'in shi da Abokan shi harda Najeeb da ya iso da daddare ya sauka a guest house d'in baban shi suma suna cin Abincin haka Nameer ma yana a part d'in shi da su Kawu Amadu da Tk da wasu Abokan shi, Senator ma na a part d'in shi da wasu Abokan shi da kuma yan uwan shi harda Baffan Fatuu dasu Ardo, sai da Baffan yayi masu hud'uba cikin hikima da zasu zo ya nuna masu abunda yakamata suyi don nan ba komai a ke masu ba sudai gyad'a kai ne nasu don yanzu mulkin ya koma kan Baffan Fatuu, duk wanda yazo sai Senator ya nuna masu dangin Amaryar sun gaisa, abun dai sai dae ace Ma sha Allah don Walima kam tayi Walima an ci an sha anyi hani'an kowa ka gani fuskar shi cike take da annuri bayan an gama aka hau yin hotuna gwaggo taje ta kira su Yadikko suka zo suma akayi hotunan da su, Fanan da kanta taje part d'in Haisam ta kira shi don ayi hotuna suka dawo dashi yana sanye da Farar shadda haka takalman shi da agogon shi duk farare ne yau dae Allah yayi an rufe kan da hula babbar rigar shi na ruk'e a hannun shi tare da Abbas suka fito shima yana sanye da riga da wando na farar shadda, idon Fatuu akan shi har suka k'araso wani irin dad'i take ji kaman ta kama yin rawa a yau ta k'ara jinjina girman Ubangiji ta k'ara gasgata Kalmar nan ta mahakurci mawadaci ne, bayan sun shigo Photographer yaci gaba da aiki, Mom da kanta ta kirawo Senator da Nameer don su zo ai hotuna dasu harda su Kawu Amadu su ka zo daga baya Senator d'in ya koma Saboda mutane d'aya baro, ana cikin hotunan Jidderh tazo wurin Fatuu tace mata ga bak'uwa Daddy yace akawo ta wurin ta, da farko Fatuu bata gane bak'uwar ba dake ta kallonta tana dariya hannunta ruk'e da yarinya da bazata wuce watanni ba, sai can da tay magana tace ma Fatun hala bata ganeta ba sannan Fatun ta d'an waro ido tace "Kaman Aunty Sadeeya?" tana dariya tace itace, mamaki ne ya kama Fatuu ganin k'anwar Khalid a wurin, hoton akayi masu tare bayan an gama ta nufi cikin parlon da ita suka zauna a saman 2 seater,
"Amman Aunty Sadeeya ya akai kika san da walimar nan har kika zo?" Fatuu ta tambaya da alamun mamaki akan fuskar ta, tana murmushi tace "tare da Dad muka zo shi ya kira ni ya sanar dani yace zamu zo dashi, ni da yake ina nan ina Aure ban fi shekara guda da watanni ba, gyad'a kai Fatuu tay tace Allah sarki,
"kin yi kyau sosae wllh kaman bake ba duk da dama kina da kyau an ma kin canza sosae kin k'ara girma kuma, na taya ki murna sosae Allah yasa Alkhairi ya baku zaman lafiya da zuriya d'ayyiba" Fatuu nata Murmushi ta amsa mata da Amin, shiru suka d'an yi dukkan su murmushi ne akan fuskar su can Fatuu ta tambaye ta Mom d'in su tace tana nan tama san zasu zo don sunyi waya take sanar mata tace ma ta kirata tayi mata Allah yasa Alkhairi, kai Fatun ta jinjina suka d'an k'ara yin shiru can Sadeeyar tace "baki tambayi Ya Khalid ba" har saida gaban Fatuu ya fad'i jin sunan Khalid, d'an murmushi tay a sanyaye tace ma Sadiyar yana ina,
bayan sunje a parlor suka tsaya Mutanen ciki suka hau yabon gayun Amarya daga baya ta wuce da ita cikin Bedroom, duk k'awayen Mom ne a ciki wasu anko ne a jikin su na full embroidery har Hajiya Zainab ma da Mom ankon ne a jikin su anyi masu dogayen riguna sunyi kyau abun har ba'a magana, harda Hajiya Kubra ta Comment section a cikin su ashe itama mutuniyar First Lady ce tasha anko full embroidery, ciki Laila ta shiga da ita Jidderh ma na biye da su, bin su d'aya bayan d'aya ta shiga yi da Fatun suna ganinta tana gaishe dasu sai yabon kyaun ta suke nan aka shiga bata kyautar kud'i Laila na amsar mata harda wadda ta bata kyautar yan kunnan zinari ita dai Fatuu sai murmushi kawai take bakin ta ya mutu abun ya girmi tunanin ta, abun mata sai ya zama kamar gasa ma, ita Hajiya Zainab Account details d'in Fatun tace abata aka sa sowa ana mata kirari sai murmushi take daga baya aka kaita wurin Mom ta zaunar da ita kusa da ita a hankali Fatuu ta gaisheta tana murmushi tace "Ma sha Allah Daughter kin yi kyau" tace mata ta gode, bayan sun gama da nan Laila ta fito da ita suka nufi part d'in Hajiya daga nan kuma bayan sun fito baya suka nufa gaba d'aya rud'ewa su kai da ganin yadda Fatuu ta had'u, anan Laila ta barta ta tafi itama ta shirya don duk kusan kowa ya saka ankon shi kowa ka gani atamfar tayi mashi kyau daga bak'ak'en har fararen, sosae Fauzy da Mino suka yi kyau ita Fauzy fitted gown ce Mino kuma riga da skirt, su Aunty Mareeya da Feenah duk dogayen riguna aka masu styles masu kyau kalar na yan Abuja Fanan itama fitted gown aka mata sosae tayi kyau gashi a jikin atamfar akwae kalar gashinta, da Laila zata tafi ta bita don ayi mata makeup itama.
Da lokacin cin Abinci yayi a parlor aka shiga jerawa saman Dining tables an k'ara wasu guda ukku suma masu cin mutum sha biyu sai aka matsar da set guda na kujeru aka had'e su, Abinci ne kala daban daban sai wanda Mutun ke so sai kuma mutum ya ci ya ture nama kuwa ba don kar inyi k'arya ba sai ince duk tsoka tayi dunkulan hannun mutum in ma bata yi ba to ta kusa🤧 ga kaji Malam, drinks da ruwa su wannan kaman company d'in su ka zo ma, bayan an gama tsara wurin aka je aka sanar ma Mom da Aunty suka fito da Mutanensu aka zazzauna yan baya ma su Aunty Mareeya aka masu magana suka fito, yadikko bata son suje ai kauyanci hakan yasa taje tayi ma gwaggo magana kan in zai yiwu akawo masu nasu can gwaggon ta fahimceta tace to,
Table guda duk k'awayen Mom ne harda Hajiya Zainab Wani kuma Aunty ce da K'awayen ta wanda wasu k'awayen su ne gaba d'aya ita da Mom, a d'ayan table na ukku su Aunty Laila ne harda Amarya Fatuu da K'awayen su sai table na k'arshe nan su Aunty Mareeya suke harda Fanan da wasu yan uwan su yan Daura Ma'aikata nata Serving nasu abun gwanin burgewa kowa harkan gaban shi yake bai damu da yadda wani ke cin Abincin shi ba, a can cikin parlon ma a saman kujeru akwae mutane zazzaune suna cin Abincin, Haisam na part d'in shi da Abokan shi harda Najeeb da ya iso da daddare ya sauka a guest house d'in baban shi suma suna cin Abincin haka Nameer ma yana a part d'in shi da su Kawu Amadu da Tk da wasu Abokan shi, Senator ma na a part d'in shi da wasu Abokan shi da kuma yan uwan shi harda Baffan Fatuu dasu Ardo, sai da Baffan yayi masu hud'uba cikin hikima da zasu zo ya nuna masu abunda yakamata suyi don nan ba komai a ke masu ba sudai gyad'a kai ne nasu don yanzu mulkin ya koma kan Baffan Fatuu, duk wanda yazo sai Senator ya nuna masu dangin Amaryar sun gaisa, abun dai sai dae ace Ma sha Allah don Walima kam tayi Walima an ci an sha anyi hani'an kowa ka gani fuskar shi cike take da annuri bayan an gama aka hau yin hotuna gwaggo taje ta kira su Yadikko suka zo suma akayi hotunan da su, Fanan da kanta taje part d'in Haisam ta kira shi don ayi hotuna suka dawo dashi yana sanye da Farar shadda haka takalman shi da agogon shi duk farare ne yau dae Allah yayi an rufe kan da hula babbar rigar shi na ruk'e a hannun shi tare da Abbas suka fito shima yana sanye da riga da wando na farar shadda, idon Fatuu akan shi har suka k'araso wani irin dad'i take ji kaman ta kama yin rawa a yau ta k'ara jinjina girman Ubangiji ta k'ara gasgata Kalmar nan ta mahakurci mawadaci ne, bayan sun shigo Photographer yaci gaba da aiki, Mom da kanta ta kirawo Senator da Nameer don su zo ai hotuna dasu harda su Kawu Amadu su ka zo daga baya Senator d'in ya koma Saboda mutane d'aya baro, ana cikin hotunan Jidderh tazo wurin Fatuu tace mata ga bak'uwa Daddy yace akawo ta wurin ta, da farko Fatuu bata gane bak'uwar ba dake ta kallonta tana dariya hannunta ruk'e da yarinya da bazata wuce watanni ba, sai can da tay magana tace ma Fatun hala bata ganeta ba sannan Fatun ta d'an waro ido tace "Kaman Aunty Sadeeya?" tana dariya tace itace, mamaki ne ya kama Fatuu ganin k'anwar Khalid a wurin, hoton akayi masu tare bayan an gama ta nufi cikin parlon da ita suka zauna a saman 2 seater,
"Amman Aunty Sadeeya ya akai kika san da walimar nan har kika zo?" Fatuu ta tambaya da alamun mamaki akan fuskar ta, tana murmushi tace "tare da Dad muka zo shi ya kira ni ya sanar dani yace zamu zo dashi, ni da yake ina nan ina Aure ban fi shekara guda da watanni ba, gyad'a kai Fatuu tay tace Allah sarki,
"kin yi kyau sosae wllh kaman bake ba duk da dama kina da kyau an ma kin canza sosae kin k'ara girma kuma, na taya ki murna sosae Allah yasa Alkhairi ya baku zaman lafiya da zuriya d'ayyiba" Fatuu nata Murmushi ta amsa mata da Amin, shiru suka d'an yi dukkan su murmushi ne akan fuskar su can Fatuu ta tambaye ta Mom d'in su tace tana nan tama san zasu zo don sunyi waya take sanar mata tace ma ta kirata tayi mata Allah yasa Alkhairi, kai Fatun ta jinjina suka d'an k'ara yin shiru can Sadeeyar tace "baki tambayi Ya Khalid ba" har saida gaban Fatuu ya fad'i jin sunan Khalid, d'an murmushi tay a sanyaye tace ma Sadiyar yana ina,