Sashe 192
Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 5 min read
Bayan gudanar da za6e tuni President Ali Adamu Zakee ya koma kan kujerar shi aka ci gaba daga inda aka tsaya, bayan yin za6en Kamfanin Haisam ya cika shekara ukku batun nasarorin da ya samu ko yake samu abun ba'a magana, a yadda suke yi duk ƙarshen shekara ake raba ribar da aka samu kuma duk in suka raba sai yaba Fatuu da Fanan wani kaso mai tsoka zuwa shekaru ukkun sai gashi Fatuu ta tara kuɗi masu ɗan yawa a yadda ta tsara in suka kai kuɗin zuwa Hajjin mutum biyu sai ta biya ma Baffanta da Gwaggo. Kamalu na gama bautar ƙasar shi aka fara shirye shiryen auren shi da Farha lokacin itama ta kammala karatunta, ba ƙaramin shagali aka sha ba bikin ɗiyar Minister ɗiyar shugaban ƙasa, gaba ɗaya hidimar bikin a Abuja aka yi ta gashi wata gwaninta da Hajiya Maryam tayi ta ban mamaki itace gaba ɗaya Amaryar da Angon ta haɗa tayi masu lefe dama tunda bikin ya taho ta sanar ma Hajiya a faɗi ma su Gwaggo kada ayi ma Farhar lefe lokacin har wasu sukai tunanin ko don tasan ba lalle Kamalun yayi lefen daya dace bane sai gashi ta bada mamaki ai kuwa gaba ɗaya ƙasa ta ɗaukka sai zancen ake na ta ba talaka ɗiyarta kuma tayi masu lefe gaba ɗaya, tun kafin bikin Haisam ya roƙi Dad dinshi kan yaba Kamalun gidan da zai zauna kafin ya mallaki nashi tunda zasu fara aiki tare, ɗaya daga cikin gidajen shi na Sabuwar Estate ɗin shi dake a Gwarinpa ya ba Kamalun, ganin babban gidane yasa Haisam ɗin yace mashi ya faɗi mashi yadda zai rinƙa biyan haya Dad ɗin nashi yace dama ɗa yana haya a gidan babanshi ne ai Kamalun kamar ɗan shi yake don haka bashi yay ya zauna kafin Allah yasa ya mallaki nashi, sosae Haisam yaji daɗin hakan yay mashi godiya da Addu'oi, lokacin har Hajiya Maryam tayi niyyar basu gidan da zasu zauna aikuwa hakan da Haisam yayi ba ƙaramin daɗi yayi ma Fatuu da Amadu ba dama sune masu gudun ayi ma Kamalun abun da za'a iya goranta mashi, ko ban faɗa ba kunsan ba ƙananun kayan ɗaki akai ma Farhar ba wanda in nace zan bayyana to ni kaina wasu abubuwan bansan ya zan faɗe su ba gida dai yayi kyau! yayi kyau!! abun saidai ace Ma sha Allah Kamalu anyi auren gata abun na Allah ne, ƙarshe dai Farha ta zama matar Kamalu ɗan fillo duk wanda yaga hotonunsu da sukai na pre wedding sai ya sake kallo wasu mutanen ma har ƙaryata cewa Kamalun ɗan talakawa ne suke domin ba kama ba alama, sai fatan Allah ya basu zaman lafiya da zuri'a ɗayyiba Amin, bayan bikin Hajiya Maryam ta basu kyautar motoci masu kyau Kamalun ya fara yin aiki a Kamfanin Haisam ita kuma Farhar Mom ɗinta ta samo mata aiki a Federal Inland Revenue.
A cikin shekarar lokacin da zuwa aikin Hajji yayi Kawu Mani ya biya ma Gwaggo bayan duk Matan shi ya biya masu sunje aikuwa sosae su Fatuu sukai Farinciki itama Gwaggon tayi farincikishi sai hamdala take, bayan gama murnar biya ma Gwaggon Haisam da Nameer sukai ma su wata irin bazata Haisam ya biya ma Baffansu shi kuma Nameer ya biya ma Yadikko wayyo daɗi! farincikin yayi yawa saida aka dangana da yan koke koke, bayan tafiyarsu ne ciwo ya tasar ma Arɗo sosae har saida su Fatuu da Haisam da Nameer suka je dubashi kafin su baro saida su Haisam ɗin suka kai shi Yola asibiti aka kwantar dashi ya miƙa kulawar shi a hannun Khalid, bayan kwana biyar aka sallame shi ba laifi ya ɗan samu sauƙi suka koma gida, gaba ɗaya hankalin Baffansu Fatuu a tashe yake da jin zancen ciwon sosae yake ma mahaifin nashi Addu'a acan Makka kan Allah ya bashi lafiya, Alhamdulillah Mahajjata sun dawo gida lafiya su Gwaggo an zama Hajiya ma sha Allah, kwana ukku da dawowar su Baffa Allah yay ma Arɗo cikawa, akace mahaifi mahaifi ne duk da dama arɗon ya tsufa sosae Baffansu Fatuu yaji mutuwar tashi harda kukan shi don yasan mahaifin nashi ba ƙaramin son shi yake ba ko kafin ya rasu saida ya bar wasiyyar cewa shi zai gaji mulkin shi na arɗo kuma ya roƙe shi kan ya haɗa kan iyalin kada ya bari a samu 6araka, lokacin da Fatuu taji labarin rasuwar sosae ta damu harda kukanta sa6anin lokacin da tana yarinya bata da burin daya wuce arɗon ya rasu duk da harda ƙuruciya, washe gari suka tafi gaisuwa suna can Mom da Aunty suka je dasu Fanan da Jidderh har Aunty Laila ma tazo Lokacin Fauzy basu ƙasar shiyasa bata zo ba amman Hajiya Zainab tazo, sosae suka yi ma su Fatun kara har mai girma shugaban ƙasa ya turo wakilci an zo anyi masu gaisuwa, duk a ranar dasu Mom suka zo suka koma amman su Fatuu sai da akayi sadakar uku washe gari suka dawo.
Ƙarshe dai kuɗin da Fatuu ke tarawa canza ra'ayi tayi tunda an kai Baffan nata makka ta yanke buɗe Foundation da zata fara tallafa ma talakawa a Katsina, koda Fanan taji niyyarta nan tace itama tana so su buɗe tare Haisam daya ji ya basu goyon baya harda gudunmawa, haka su Mom harda Hajiya Maryam da President duk suma sun basu gudunmawa, daga baya aka buɗe Foundation ɗin mai suna HAIFAT FOUNDATION, bayan buɗe shi a hannun Gwaggo suka damƙa kula da shi su kawu Amadu da Tk da matansu su Haulat da Husnah suka zama masu taimaka mata wurin gudanar da ayyukanshi harda Aunty Mareeya da Feenah duk sun shiga cikin masu gudanar da ayyukan shi sai fatan Allah ya sanya albarka,
A cikin shekarar lokacin da zuwa aikin Hajji yayi Kawu Mani ya biya ma Gwaggo bayan duk Matan shi ya biya masu sunje aikuwa sosae su Fatuu sukai Farinciki itama Gwaggon tayi farincikishi sai hamdala take, bayan gama murnar biya ma Gwaggon Haisam da Nameer sukai ma su wata irin bazata Haisam ya biya ma Baffansu shi kuma Nameer ya biya ma Yadikko wayyo daɗi! farincikin yayi yawa saida aka dangana da yan koke koke, bayan tafiyarsu ne ciwo ya tasar ma Arɗo sosae har saida su Fatuu da Haisam da Nameer suka je dubashi kafin su baro saida su Haisam ɗin suka kai shi Yola asibiti aka kwantar dashi ya miƙa kulawar shi a hannun Khalid, bayan kwana biyar aka sallame shi ba laifi ya ɗan samu sauƙi suka koma gida, gaba ɗaya hankalin Baffansu Fatuu a tashe yake da jin zancen ciwon sosae yake ma mahaifin nashi Addu'a acan Makka kan Allah ya bashi lafiya, Alhamdulillah Mahajjata sun dawo gida lafiya su Gwaggo an zama Hajiya ma sha Allah, kwana ukku da dawowar su Baffa Allah yay ma Arɗo cikawa, akace mahaifi mahaifi ne duk da dama arɗon ya tsufa sosae Baffansu Fatuu yaji mutuwar tashi harda kukan shi don yasan mahaifin nashi ba ƙaramin son shi yake ba ko kafin ya rasu saida ya bar wasiyyar cewa shi zai gaji mulkin shi na arɗo kuma ya roƙe shi kan ya haɗa kan iyalin kada ya bari a samu 6araka, lokacin da Fatuu taji labarin rasuwar sosae ta damu harda kukanta sa6anin lokacin da tana yarinya bata da burin daya wuce arɗon ya rasu duk da harda ƙuruciya, washe gari suka tafi gaisuwa suna can Mom da Aunty suka je dasu Fanan da Jidderh har Aunty Laila ma tazo Lokacin Fauzy basu ƙasar shiyasa bata zo ba amman Hajiya Zainab tazo, sosae suka yi ma su Fatun kara har mai girma shugaban ƙasa ya turo wakilci an zo anyi masu gaisuwa, duk a ranar dasu Mom suka zo suka koma amman su Fatuu sai da akayi sadakar uku washe gari suka dawo.
Ƙarshe dai kuɗin da Fatuu ke tarawa canza ra'ayi tayi tunda an kai Baffan nata makka ta yanke buɗe Foundation da zata fara tallafa ma talakawa a Katsina, koda Fanan taji niyyarta nan tace itama tana so su buɗe tare Haisam daya ji ya basu goyon baya harda gudunmawa, haka su Mom harda Hajiya Maryam da President duk suma sun basu gudunmawa, daga baya aka buɗe Foundation ɗin mai suna HAIFAT FOUNDATION, bayan buɗe shi a hannun Gwaggo suka damƙa kula da shi su kawu Amadu da Tk da matansu su Haulat da Husnah suka zama masu taimaka mata wurin gudanar da ayyukanshi harda Aunty Mareeya da Feenah duk sun shiga cikin masu gudanar da ayyukan shi sai fatan Allah ya sanya albarka,