Sashe 168
Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Ai Kawu Amadu banda kuɗi Kyau ma nasa a so mutum kuma kana dashi" ɗan juya ido yay yace mata kenan ita don kyau take son shi tana dariya tace "a'a, don ka cancanci in so ka Kawu Amadu saboda kana da halin kirki" wani kalan murmushin daɗi yay yace "To nagode Allah ya tabbatar mana da Alkhairi ya ƙara mana ƙaunar junanmu, amman pls ina neman wata alfarma wannan Kawu Amadun da ake ce man a aje shi a gefe a rinƙa kirana da sunan da zansan nima na fara soyayya da aketa man gori da surutu ashe ma ni tuni Allah ya za6a man mata lokaci ne kawae baiba yanzu gashi lokacin yayi ta bayyana" gaba ɗayansu kallon juna suke cikin ido suna sakar ma juna ƙayataccen murmushi cikin kwantar da murya ta furta "Ok My Dear an canza maka in ma wannan bai yi ba sai a canza wani" wani farfar yay da ido yace "yayi sosae Sweetie nah" da sauri ta kai duka hannuwanta ta rufe fuska alamar kunya Amadun ya sa dariya, suna haka Mahaifinta ya dawo yabi su da kallo Amadu ya sunkuyar da kai ya gaishe dashi bayan ya amsa yace "kamar Amadu ko" kai ya ɗaga mashi yace eh shine Mahaifin nata yay ɗan murmushi tare da furta Ma sha Allah, daga haka ya juya zai shiga da sauri Haulat taja gefe tana mashi sannu da zuwa ya amsa kafin ya shige, kallonta Amadu yay yace Allah yasa data koma gidan Baban yace mata ace ya turo tana murmushi tace da wuri haka yace eh mana mi zasu tsaya yi gara suyi auren alabashshi sunyi soyayyar a gidansu tayi dariya, Mahaifinta na shiga ɗakin innarsu ya wuce tana kwancen har ta fara yin bacci saidai bai yi nisa ba, yana yin sallama ta buɗe ido ganin shine ta fara ƙoƙarin tashi zaune tana mashi sannu da zuwa ya nufi wurin gadon yana amsa mata, a bakin gadon ya zauna ta fara ƙoƙarin saukkowa tana faɗin bari a kawo Abinci ya dakatar da ita ta hanyar faɗin tukunna ta koma ta zauna, tambayarta yay mike tsakanin Haulatu da Yaron can Amadu ne ya gansu tsaye a ƙopar gida, murmushi tayi nan ta kwashe komai game da zuwan gwaggo ta faɗa mashi tun kafin ta ida ya hau jinjina kai tare da yin murmushi bayan ta gama faɗi mashi yace amman dai yayi farincikin jin zancen wllh don Amadu ba dai hankali ba ga ƙoƙarin neman na kai itama tace sosae taji dadin al'amarin don tana son Amadu, Mahaifin nasu yay fatan Allah ya tabbatar masu da Alkhairi ta amsa da Amin, bayan shigar Mahaifin Haulat basu jima ba sosae suka yi sallama harda kuɗi ya bata yace da safe ta siya ma Salma abunda takeso tace mashi don Allah ya barsu yay mata wani kallo yace badai iko zata nuna mashi da ɗiyar tashi ba, da sauri ta bashi haƙuri tana murmushi shima shi yake yi ta amsa tare da yi mashi godiya sukai bankwana cike da nuna ƙauna, kamo hanyar gida yayi sai faman sakin murmushi yake sai kace zautacce yana isowa ciki ya shige ya nufi ɗakin Gwaggo lokacin har ta kwanta ya shiga da sallama ta ɗago tana amsa mashi tare da kunna wayarta haske ya kawo tace mashi ya kunna wutar ɗakin, bayan ya kunna kujera ya nufa ya zauna sai faman murmushi yake Gwaggo ta tashi zaune tana kallonshi tace mashi ya akai ya bata amsa da Haulat ɗin ta amince mashi yanzu sai kawai a saka rana, ɗan buɗa baki Gwaggo tayi ta kai hannu ta ruƙe ha6a tace ko kunyarta bai ji da sauri ya sunkuyar da kai yana yar dariya yace yaga kamar tana son yayi auren ne shiyasa ta ɗan ta6e baki tace shikenan Allah ya tabbatar masu da Alkhairi zata yi ma dangin Baban shi magana kan hakan ya ɗago yace to, har zai miƙe yaji tace to yana da kuɗin yin Auren ko ya kalleta tare da ɗan sosa kai yace bazasu gagara ba tayi yar dariya tace yaje Allah ya taimaka yayi mata saida safe ya juya tabi shi da kallo tana murmushin daɗi don yana ɗaya daga cikin burinta a yanzu taga auren autan nata, yana fitowa wayar shi ta fara yin ringing ya duba ganin Haulat ce yasa shi nufar ɗakin shi da sauri saida yaje bakin kopar shiga ya ɗaga tare da ƙarasa shigewa, ce mashi tay dama ta kira ne taji ya ya koma gida jama'a zo kuga washe bakin daɗi wurin Amadu yace haka ta damu dashi wannan in sukai aure yasan ba ƙaramar kulawa zata bashi ba tana murmushi tace mashi in sha Allah fatan itama zai kula da ita da sauri yace tamkar ƙwai in sha Allah duk sukai dariya, a saman ƙatuwar katifar shi daya canza tuni ya kwanta suka cigaba da shan soyayya, sun ɗan ɗauki lokaci kafin sukai bankwana, bayan ya gama kiran Kamalu yayi ta wayar yace mashi ya kullo shagon ya shigo shi gashi nan har ya kwanta, a ranar kwanan farinciki yan gidan su Amadu da Haulat sukai karma dai su Masoyan.
Washe gari wurin misalin ƙarfe goma na Safe Gwaggo ta kira Fatuu bayan tayi ringing Fatun ta yanke ita ta kira dama haka take duk suka kirata, gaisawa sukai ta tambayi jikinta dasu twins da Babansu da Fanan duk ta amsa mata da suna lafiya,
"Dama na kira in maki Albishir ne duk da bansan ko wani yayi maki ba" da sauri Fatun tace mata a'a basu yi waya da kowa ba a ƙagauce ta tambayeta wane Albishir ne nan Gwaggon ta faɗi mata game da Amadu da Haulat, wata uwar ƙarar farinciki Fatuu ta saka ta hau fadin Alhamdulillah ya Allah Gwaggo nata dariya, bayan ta tsagaita da yin murnar da alamun mamaki ta tambayi Gwaggon ita tasa shi ya nemi auren Haulat ɗin ne tace mata a'a ta faɗi mata yadda sukai dashi,
"Kai amma naji dadi wllh, kinsan Gwaggo tun kwanaki nike raya inama Kawu Amadu ya auri Haulat, sai dai gani nike kamar bazai amince ba tunda ba budurwa bace abun Allah ashe har ya furta mata kuma ni bata yi man maganar ba ma" daga jin yadda take Magana zaka fahimci ba ƙaramin farinciki take ciki ba, Maganar saka rana Fatun tayi mata gwaggon tace yau take niyyar kiran dangin babanshi ta faɗa masu sai suzo nema mashi auren daga nan a saka rana gaba ɗaya, da sauri Fatuu tace "Gwaggo don Allah a saka sai bayan na haihu Ya Haisam yace bazan ƙara zuwa ba har sai na haihu kuma yanzu saura wata biyar tunda yayi wata haɗu" a marairaice tayi Maganar Gwaggon na dariya tace ai itama bata son a saka da wurin don tana son ayi ma gidan gyara sosae don anan take son su zauna tare, cike da murna Fatun tace yauwa hakan yayi ta tambayi kamar wata nawa za'a saka Gwaggon tace ko shidda ko bakwai Fatun tace a bari bakwai ɗin lokacin har wanka ta gama tace hakane to sai a barshi bakwai ɗin daga baya sukai sallama, suna gama wayar parlor ta nufa da sauri don taje ta faɗi ma Haisam da yake Weekend ne yana gida, yana kishingiɗe kan doguwar kujera su twins na kwance a kan ƙafafun shi suna yin kallo ta nufo su cikin Washe baki Haisam ya juya yana kallon ta, ganin farinciki akan fuskarta yasashi yi mata murmushi a kan hannun kujerar da ya jingina ta zauna ta kai hannu cikin sumar shi ta fara ɗan sosai mashi, ɗago fuskarshi yay ya kalleta idanunshi a ɗan lumshe ya tambayi ya akai yaga tana farinciki ta kashe mashi ido tace tana Bedroom ta tuno da shine mijinta shine take farincikin, wani kalan murmushin gefen baki yay yace ai kullum tasan shine mijinta yasan bata mantawa da hakan tana murmushi tace hakane in ma ta manta to kuwa bata cikin hayyacinta, faɗi mashi tayi Gwaggo ce ta kirata ta sanar mata da Kawu Amadu zai auri ƙawarta Haulat" sosae shima ya nuna farincikin shi yace Amadun ya kyauta ya tambayi yaushe za'a sa rana ɗin ta faɗi mashi yadda sukai da Gwaggo na sai nan da wata bakwai saboda za'a gyara gidan tana son su zauna anan ya jinjina kai yace Allah ya kaimu ta amsa kafin ta maida idonta kan su twins daketa kallon su kamar suna fahimtar abunda ake a Tv da fulatanci tace basu ga Mom bane Adam ne ya kalleta yana mata dariya shi kuwa miskili Abie ko kallon nata bai yi ba, saukkowa Adam yay da yake sun fara iya tafiya ya nufota yana zuwa ta ɗaukeshi ya kai hannu yana ta6a ƙirjinta alamar yana son tayi feeding nashi saida ta gyara zama sannan ta fara bashi Abie na ganin haka shima ya saukko daga kan kujerar zai nufota ta ɗan harare shi yaja ya tsaya yana kallonta da idanunshi tubarkallah Haisam nata kallon su yana murmushi, ganin kallon da take mashi yasa ya fara ta6e baki zai yi kuka da turanci Fatun tace mashi tunda bai damu da ita ba itama bata ƙara bashi abunta kawai sai ya kife fuskarshi a jikin Haisam ya fashe da kuka, suna haka Fanan ta fito tana sanye da skinny jeans da yar top ta nufo su da sauri tana faɗin waya ta6a mata Little Abie yanzu suyi faɗa, daukar shi tayi tana tambayar waye ya saka shi kuka da hannu ya nuna mata Fatuu ta juya tana kallonta ta ɗan ɗaure fuska tace miyasa zata saka shi kuka kafin ta bata amsa Adam ya saki breast ɗin ta dago yana gwaranci shi ala dole magana yake duk ya basu dariya, tambayar Haisam tayi abunda ya haɗa su yana murmushi ya faɗi mata ta nufi gefen Fatuu tana faɗin ayi haƙuri dasu haka halin su yake ba shareta sukai ba ta zauna kusa da ita tace ma Abie din yace mata Sorry saida ta maimaita mashi kusan sau ukku sannan ya faɗi Sorry ɗin, bayan ta gama ba Adam ɗin ta amshe shi shima ta fara bashi anan take faɗi mata zancen auren Amadu da Haulat itama Fanan ɗin ta nuna farinciki sosae tayi fatan Alkhairi.
Washe gari wurin misalin ƙarfe goma na Safe Gwaggo ta kira Fatuu bayan tayi ringing Fatun ta yanke ita ta kira dama haka take duk suka kirata, gaisawa sukai ta tambayi jikinta dasu twins da Babansu da Fanan duk ta amsa mata da suna lafiya,
"Dama na kira in maki Albishir ne duk da bansan ko wani yayi maki ba" da sauri Fatun tace mata a'a basu yi waya da kowa ba a ƙagauce ta tambayeta wane Albishir ne nan Gwaggon ta faɗi mata game da Amadu da Haulat, wata uwar ƙarar farinciki Fatuu ta saka ta hau fadin Alhamdulillah ya Allah Gwaggo nata dariya, bayan ta tsagaita da yin murnar da alamun mamaki ta tambayi Gwaggon ita tasa shi ya nemi auren Haulat ɗin ne tace mata a'a ta faɗi mata yadda sukai dashi,
"Kai amma naji dadi wllh, kinsan Gwaggo tun kwanaki nike raya inama Kawu Amadu ya auri Haulat, sai dai gani nike kamar bazai amince ba tunda ba budurwa bace abun Allah ashe har ya furta mata kuma ni bata yi man maganar ba ma" daga jin yadda take Magana zaka fahimci ba ƙaramin farinciki take ciki ba, Maganar saka rana Fatun tayi mata gwaggon tace yau take niyyar kiran dangin babanshi ta faɗa masu sai suzo nema mashi auren daga nan a saka rana gaba ɗaya, da sauri Fatuu tace "Gwaggo don Allah a saka sai bayan na haihu Ya Haisam yace bazan ƙara zuwa ba har sai na haihu kuma yanzu saura wata biyar tunda yayi wata haɗu" a marairaice tayi Maganar Gwaggon na dariya tace ai itama bata son a saka da wurin don tana son ayi ma gidan gyara sosae don anan take son su zauna tare, cike da murna Fatun tace yauwa hakan yayi ta tambayi kamar wata nawa za'a saka Gwaggon tace ko shidda ko bakwai Fatun tace a bari bakwai ɗin lokacin har wanka ta gama tace hakane to sai a barshi bakwai ɗin daga baya sukai sallama, suna gama wayar parlor ta nufa da sauri don taje ta faɗi ma Haisam da yake Weekend ne yana gida, yana kishingiɗe kan doguwar kujera su twins na kwance a kan ƙafafun shi suna yin kallo ta nufo su cikin Washe baki Haisam ya juya yana kallon ta, ganin farinciki akan fuskarta yasashi yi mata murmushi a kan hannun kujerar da ya jingina ta zauna ta kai hannu cikin sumar shi ta fara ɗan sosai mashi, ɗago fuskarshi yay ya kalleta idanunshi a ɗan lumshe ya tambayi ya akai yaga tana farinciki ta kashe mashi ido tace tana Bedroom ta tuno da shine mijinta shine take farincikin, wani kalan murmushin gefen baki yay yace ai kullum tasan shine mijinta yasan bata mantawa da hakan tana murmushi tace hakane in ma ta manta to kuwa bata cikin hayyacinta, faɗi mashi tayi Gwaggo ce ta kirata ta sanar mata da Kawu Amadu zai auri ƙawarta Haulat" sosae shima ya nuna farincikin shi yace Amadun ya kyauta ya tambayi yaushe za'a sa rana ɗin ta faɗi mashi yadda sukai da Gwaggo na sai nan da wata bakwai saboda za'a gyara gidan tana son su zauna anan ya jinjina kai yace Allah ya kaimu ta amsa kafin ta maida idonta kan su twins daketa kallon su kamar suna fahimtar abunda ake a Tv da fulatanci tace basu ga Mom bane Adam ne ya kalleta yana mata dariya shi kuwa miskili Abie ko kallon nata bai yi ba, saukkowa Adam yay da yake sun fara iya tafiya ya nufota yana zuwa ta ɗaukeshi ya kai hannu yana ta6a ƙirjinta alamar yana son tayi feeding nashi saida ta gyara zama sannan ta fara bashi Abie na ganin haka shima ya saukko daga kan kujerar zai nufota ta ɗan harare shi yaja ya tsaya yana kallonta da idanunshi tubarkallah Haisam nata kallon su yana murmushi, ganin kallon da take mashi yasa ya fara ta6e baki zai yi kuka da turanci Fatun tace mashi tunda bai damu da ita ba itama bata ƙara bashi abunta kawai sai ya kife fuskarshi a jikin Haisam ya fashe da kuka, suna haka Fanan ta fito tana sanye da skinny jeans da yar top ta nufo su da sauri tana faɗin waya ta6a mata Little Abie yanzu suyi faɗa, daukar shi tayi tana tambayar waye ya saka shi kuka da hannu ya nuna mata Fatuu ta juya tana kallonta ta ɗan ɗaure fuska tace miyasa zata saka shi kuka kafin ta bata amsa Adam ya saki breast ɗin ta dago yana gwaranci shi ala dole magana yake duk ya basu dariya, tambayar Haisam tayi abunda ya haɗa su yana murmushi ya faɗi mata ta nufi gefen Fatuu tana faɗin ayi haƙuri dasu haka halin su yake ba shareta sukai ba ta zauna kusa da ita tace ma Abie din yace mata Sorry saida ta maimaita mashi kusan sau ukku sannan ya faɗi Sorry ɗin, bayan ta gama ba Adam ɗin ta amshe shi shima ta fara bashi anan take faɗi mata zancen auren Amadu da Haulat itama Fanan ɗin ta nuna farinciki sosae tayi fatan Alkhairi.