← Book details Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 115 OF 211

Sashe 115

Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Ban ta6a tunanin wani zai man irin wannan kirkin ba a rayuwata har na rasa mi zan ce ma" cikin muryar kuka tayi Maganar tana kallon su Hajiya dake mata d'an murmushi, maida idonta tayi kan Fatuu bayan ta goge k'wallan tace "All i can say to you is thank you. Thank you so much for your generosity Zarah. You have shown me a kindness that I will never forget. Never" ta k'arasa tana jujjuya kai alamar tabbatar mata da abunda ta fad'a, jinjina kai Fatuu tay tana goge kwallanta gaba d'aya sauran Mutanen cikin dakin sunyi shiru suna bin su da kallo, mik'a mata Babyn tayi bayan Fatun ta amsa tana murmushi tace "Ba sai kin bani shi ba Zarah, We're one Family so duk abunda d'aya ya mallaka tamkar na kowa ne, I'm I right?" Da sauri Fatuu ta jinjina mata kai alamar eh Fanan d'in taci gaba "Gud, ko baki bani shi ba gaba d'ayan su yarana ne kuma in sha Allah zamu raine su mu basu tarbiya mai kyau tare" atare gaba d'aya aka had'a baki wurin furta "Allahu ya sha" Fanan tay d'an murmushi tace Ameen, Hajiya ce ta d'an yi gyaran murya duk suka maida idonsu kanta a nutse ta fara magana tace wannan abun daya faru babu wanda ya kai ta jin dad'i wllh, Fateema itama tayi abunda da k'yar a samu wadda zata iya yin hakan ga abokiyar zamanta kamar yadda itama Fanan d'in tayi gaba d'aya suka jinjina kai, kallon Haisam tayi tace "ina son ka sani duk Wannan sadaukarwar da suke Saboda son da suke maka ne hakan yasa duk suka fifita farincikin ka fiye da nasu don haka ina k'ara jan hankalin ka da ka k'ara jajircewa wurin ganin ka ruk'e su da amana ka kyautata masu, kaima ka fifita farincikin su fiye da naka don kuwa ba K'aramin dace kai ba wllh ka k'ara gode ma Allah, samun mata irin wannan a zamanin nan da muke ciki ba zan ce babu irin su ba amman ina mai tabbatar maka da samun su da wahala don koda mata suna son miji zaka ga basu damu da Farincikin shi ba Saboda haukan kishi kullum cikin tada mashi hankali suke a haka kuma wai don ana son shi ne, ina rok'on Allah daya k'ara had'a kan ku ya Albarkaci rayuwar ku gaba d'aya ya k'ara shirya mana ku ya kuma k'ara rufa mana asiri fiddunya Wal akhira yasa mu gama da duniya lafiya" a tare gaba d'aya suka amsa da Amin fuskokin su d'auke da Murmushi ta juya kan su Fatuu ta k'ara masu Nasiha kan su k'ara had'a kan su ta nuna masu hakan da suka za6ar ma kan su shi yafi masu Alkhairi don ko ba komai zasu kasance a cikin farinciki suma su cigaba da kyautata ma mijin su hakan shine kishin daya dace, sosae tayi masu Nasiha mai tsuma jiki duk fuskokin su d'auke da d'an murmushi suke jinjina mata kai, bayan ta gama dasu ta juyo kan Nameer dake manne da ita ta kai hannu cikin sumar shi tace "na dawo kan ka mage sarkin son jiki ko kuma in ce mazuru...." Gaba d'aya aka saka dariya, taci gaba "Allah kaima ya nuna mana bikin ka lafiya kaida yar fillon taka duk da dai ina jin ki shi" tay Maganar tare da d'an kwa6e fuska duk ta basu dariya, hira suka cigaba da yi gwanin sha'awa saida aka yi sallar Azahar duk suka tashi Fanan anan tayi sallar tun tana cikin yi yaran suka tashi suna kuka tana sallamewa ta taso ta nufo gadon tana tambayar mike damun su suke kuka Fatuu dake murmushi tace mata k'ilan yunwa suke ji tace to tay feeding nasu ta daina bari suna yin kuka pls yadda tayi Maganar har saida ta ba Fatuu dariya, ita ta taimaka mata ta fara shayar dasu saida duk suka k'oshi sannan Fanan ta d'auke su gaba d'aya tana masu wasa tana fad'in ga Mom d'in su tazo duk sukai mata k'uri da ido sai kace sun san mi take cewa sai faman saka Fatuu dariya take.

Bayan Fanan ta koma d'akin Laila dama anan take sauka in tazo gidan ta shiga kiran Mom d'inta wato Hajiya Maryam, bayan tayi picking suka gaisa tayi mata anzo lafiya Fanan d'in ta amsa mata tace ai tayi zaton zata tsaya Lagos ko duk murnar sunyi Y'ay'an ce tasa bata biya ba Fanan na dariya tace mata Kusan hakane ta k'agara da ta gansu gashi tare da Nameer suke tace to, "Mom you know What?" Fanan ta fad'a Mom d'in tace mata a'a mi akai, labarin abunda ya faru tsakaninta da Fatuu ta shiga bata yadda ta d'auki d'aya daga cikin yaran ta bata kyauta, d'an ta6e baki Hajiya Maryam d'in tayi tace mata in duk cikin salon neman wurin zama ne fa da sauri Fanan tace mata Wallahi har cikin zuciyarta ta bata don a gaban kowa akayi tace kuma su zama shaida, "to ce mata akai ke bazaki haihun bane?" Kai Fanan ta girgiza fuska a d'an yamutse tace "No Mom, kawai ta bani ne saboda k'aunata da take kuma taga ita ta riga haihuwan dama na fad'a maki wllh tana zaune dani da zuciya d'aya Mom, sam bata d'auke ni a matsayin kishiya ba" still bakin Hajiya Maryam d'in na a d'an ta6e tace mata to yanzu ita ta amshi yaron kenan tace mata a'a nan ta fad'i mata yadda sukai ta k'ara da cewa "nasan ko ban amsa ba bazata ta6a man iyaka da yaran ba so nima zasu zama kamar nawa ne kinga ko ban haihu ba na samu wanda zasu kira ni da Momy, don Allah Mom ki manta komai ki so Zarah sannan ki mana fatan Alkhairi" yar dariya tayi tace ita dama ai bata ce ta tsaneta ba tana masu fatan Alkhairi Allah ya k'ara had'a kawunan su itama kuma tana mata Addu'ar Allah yabata haihuwan, cike da jin dad'i cikin washe baki Fanan d'in ta amsa da Amin tare da Fad'in shiyasa take k'aunar ta Saboda she's a Mom like no other tana jiyo dariyar Hajiya Maryam d'in, tambayar yaushe zata zo taga Babies tayi tace mata tunda ita tana nan ba sai tazo ba, a shagwabe murya kamar zata yi kuka tace"Haba Mom, yanzu fa kika nuna man komai ya wuce kuma ai ni zuwana daban naki ma daban, don Allah ki zo, haka fa da biki kika k'i zuwa pls kizo hakan zai sa aga kin manta komai kuma ma yaran nan fa grandchildren d'in ki ne" tana dariya tace mata "to sarkin tsara zance wasa nike maki zan zo in sha Allah amman gaskiya sai Ranar suna don akwae kaya na da zasu iso ranar Asabar dole zan tsaya in ga isowar su" cike da Farinciki Fanan d'in tace to ba komai ai tunda zata zo d'in Allah ya kaimu Ranar lahadin harda tambayarta a cikin kayan da tayi Order d'in akwae na jarirai tace mata eh Fanan din tace to ta za6o ma Babies d'in su Unique ones masu yawa Hajiya Maryam d'in ta amsa da tunda ita ta bata kudin da ta siyo ko Fanan ta saka dariya, hira suka cigaba da yi Fanan bata tambayi Dad d'inta ba don tasan ta baro shi a America, kafin suyi sallama ta tambaye ta Farha tace mata tana d'akin ta k'ilan ko bacci take. Bayan sun gama wayar Farha ta shiga kira lokacin da tayi picking tana jin muryarta ta gane bacci take ta bata hakurin tashin ta da tayi tace mata ba komai, tambayar ta tayi tazo ne tace mata eh gata a Abuja nan ta shiga bata labarin irin kyawun Babies d'in da aka Haifa masu fuskar Farhar da d'an murmushi take sauraronta bayan ta gama tace Allah ya raya, tambayarta tayi zata biyo Mom tazo suna ko tace mata No, cikin sigar rarrashi tace mata don Allah ta manta komai ta d'auki Zarah matsayin yar'uwarta itama don tana da kirki sosae kuma tana k'aunarta, nan ta shiga bata labarin yadda ta bata kyautar Babyn da ta haifa tace in ba don tana kaunarta ba taya zata mata haka, daga k'arshe dai saida tayi nasarar shawo kan Farhar tace mata zata biyo Mom d'in nasu zo kaga murna a wurin Fanan.

Ranar Friday da rana Laila ta iso itama ta nuna farinciki sosae ganin yaran nan suka shiga shirye shiryen yin gagarumin suna, a ranar da daddare bayan sallar isha Haisam na zaune a parlon shi na saman bene yana operating laptop d'in shi jikinshi sanye da ash d'in jallabiya wayar shi tay k'ara alamar shigowar sak'o, hannu ya kai gefen shi ya d'aukko wayar ya shiga dubawa, bin sakon yayi da kallo bayan ya bud'e wanda credit alert ne na kud'i Naira miliyan d'aya da rabi daga Sameer, sam bai yi mamakin ganin kud'in ba duk da bai san na minene ba amman ba yau ya fara turo mashi kud'i ba don koda bikin shi da Fanan miliyan biyu ya bashi, fita yay daga cikin sak'on ya fara kokarin kiran Sameer d'in, saida ta kusa yankewa sannan ya d'aga suka gaisa Haisam d'in yace mashi suyi Vedio call ya furta mashi Ok, bayan ya maida kiran na gani Sameer d'in na zaune akan doguwar kujera a gidan shi dake a England wanda Company d'in su suka bashi, suma dare ne can har yayi shirin bacci yana sanye da robe da ta bayyanar da k'irjin shi wanda shima ke d'auke da kwantacciyar suma kamar dai yadda na Haisam yake, k'ara gaisawa sukai Haisam yay mashi ya aiki ya amsa da Alhamdulillah,
Chapter 115 · 0% Book details