Sashe 111
Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Wannan dad'in bai mana yawa ba kuwa?" Dad ya fad'a idon shi akan Haisam dake murmushi ya k'ara fad'in "Son banda son kai fa halan kai ne ka zabi sunan gaba d'aya?" Kai ya d'an girgiza calmly yace shi ne ya za6i nashi ita kuma ta za6i na grandpa, kallon Fatuu Dad yay tana murmushi ya furta "Daughter in akai haka bamu so kan mu da yawa ba kuwa karfa ayi kura da shan bugu gardi da k'wace jaka" gaba d'aya aka saka dariya a hankali tace a'a ai duk d'aya ne duk suka jinjina kai Dad harda yin godiya ya tambayi waye abokin nashi waye kuma Baban nashi duk aka nuna mashi Aunty tace sun kasa gane yadda zasu bambance su shiyasa suka bambanta masu kaya dama fin set biyu ta d'aukko wai ko zata haifi fin biyun duk akai dariya, jin haka yasa Momy ta fara k'ok'arin duba su taga ko zata samu abunda za'a rink'a Gane su, tunawa tayi da yadda ake gane ta ita da Mom d'in Sameer hakan yasa ta k'ura ma na hannun Dad wanda ta bashi wato Aliyu ido tana kallon idon shi dake a bud'e dama tunda Jidderh ta sunkuce shi yana bacci ya farka sosae ta k'ura ma idon nashi ido harda d'an bud'awa taga k'wayar bata ciza ba sosae ta d'an yi brown, juyawa tay kan d'ayan dake a hannun Affan shima ta shiga dubawa sai gashi tashi bak'a ce wuluk tana ganin haka ta d'ago tana dariya ta fad'i masu suma ga yadda za'a rink'a bambanta su duk saida suka ji mamaki ganin abu yazo d'aya suka shiga fad'in ikon Allah, Addu'oi Dad duk yayi masu bayan ya gama ya tambayi an fad'i ma su Hajiya Aunty tace a'a Saboda ba waya yace Ok bari ya sanar mata, Lokacin da kiran ya shiga bata dad'e da tashi daga kan abun salla ba ta koma ta kwanta bayan ta d'auka cikin girmamawa ya gaida ta tare da tambayar yadda take tace mashi Alhamdulillah kafin ta ce kiran sassafe mai tattare da abu biyu Alkhairi ko akasin haka tana fatan Alkhairin ne yasa aka kirata Dad dake dariyar Maganar tata yace eh Alkhairi ne dama zai sanar mata ne tayi Ya'ya yan samari amman d'aya a ciki kuma miji ne Daughter tayi mata tana jin haka ta fahimci zancen, cikin washe baki ta hau fad'in ma sha Allah Fateema Allah yayi an sauka kenan, tambayar lokacin da akai haihuwar tayi ya fad'i mata yace gasu ma a Asibitin ko sallamarta ba'a kai ga yi ba ta kara tambayar to ya jikinta nan ma yace lafiya lou take bari ya bata ya mik'a ma Fatun cikin murmushi ta gaishe da Hajiya tace "Fateema yau ai ni ya kamata in yi gaisuwa nida aka Haifa ma sabon miji, to barka, barkanmu da Arzik'i Fateema, sannu da k'ok'ari Allah ya k'ara maki lafiya ya raya mana ya kuma Albarkaci rayuwarsu" kaman bazata amsa ba sai kuma can k'asan mak'oshi ta amsa Kafin ta tambayi yaushe zata taho tace ai don yau ta riga tayi da ta taho amman gobe in sha Allahu tana nan tafe ai bata zauna ba wannan abun Arzik'in ya samu, bayan sun gama wayar tana niyyar mik'a ma Dad Jidderh tayi karaf ta amsa ko gaida Hajiyar bata yi ba ta hau zuzuta mata kyaun jariran da kuma girman su Hajiyar nata fad'in Ma sha Allah Tubarkallah kafin a k'agare tace mata tayo mata Vedion su yanzun nan ta gani da sauri tace to, bayan Hajiya ta gama wayar Gwaggo ta shiga kira lokacin itama bata dad'e da komawa ta kwanta ba wayar ta fara ringing koda ta d'aukko ganin mai kiran saida gabanta ya d'an fad'i, d'auka tayi da sallama Hajiya ta amsa tun kafin gwaggon ta k'ara cewa wani abu tace "to barkan mu da Arzuki Fateema dai Allah yayi ta sauka lafiya an samu yan samari" ba shiri gwaggo ta tashi zaune cikin washe baki take ta fad'in Alhamdulillah daga baya tayi Addu'ar Allah ya raya ya Albarkace su Hajiya ta amsa tace ai ita gobe in Allah ya kaimu ma zata tafi don harda maigida a ciki ta fad'i mata sunayen su Gwaggo tace ah lallai yakamata ta tafi da wuri ta tarbi sabon maigida tayi Maganar tana dariya, suna gama wayar ta fito ta nufi d'akin Mino har ta koma bacci tsabar farinciki ta tasheta ta fad'i mata zo kaga murna don wani kalan wuntsilowa tayi daga kan gado ta duk'a k'asa tayi sujjadar godiya ga Allah don kullum damuwarta itace yadda Adda Fatuu zata haihu, da gudu ta fito ta nufi d'akin Kawu Amadu shima har ya koma bacci ta fad'a d'akin tana faman kwad'a mashi kira aikuwa a fusace ya farka don tunda ta fara kiran nashi yana ji yayi shiru sai daga baya ya farka har zai rufeta da fad'a dama suna yawan haka duk aka aikota ta tashe shi ko kuma wata buk'ata tata kamar in tana son yayi mata Assignment, da sauri ta tari hanzarin shi cikin tsananin murna ta fad'i mashi Adda Fatuu ta haihu yan biyu duk maza nan take ya waro ido sai kuma ya washe baki, Bayan Hajiya ta kira gwaggo Hajiya Maryam ta shiga kira bayan ta d'aga ta gaishe da ita ta amsa kafin tace to tayi Ya'ya harda sabon maigida a ciki da rashin fahimta ta tambayi wani ya'ya ta fad'i mata itama ta nuna farincikinta ta yi Allah ya raya masu, lokacin da Haisam ya kira Fanan ya sanar mata Kusan suk'ewa tayi don dad'i tace miyasa da ana labour d'in bai kirata ba sunyi tare yace mata ya rud'e ne, sawa tayi ya maida kiran Vedio call lokacin da taga yaran sai kawai ta fashe da kukan dadi baiwar Allah bata da burin daya wuce ta haifi yaro mai kama da Haisam ashe ba itace mai rabon hakan ba ta raya a ranta saidai sosae take farinciki don tana da yak'inin yaran zasu zama tamkar nata, gaba d'aya saida su Dad sukai mata barka ta cikin wayar tana ta washe baki take amsawa, kan kace mi duk an kira yan'uwa da Abokan Arzik'i an sanar dasu game da haihuwar anata ba Fatuu suna mata barka a haka ma don Wayarta bata a hannun ta, lokacin da gwaggo ta kira Aunty Mareeya ta sanar mata Fauzy na cikin yin shirin Makaranta Aunty tazo d'akin nata cikin tsananin farinciki ta sanar mata har saida ta daka wani uban tsallan murna tana ta faman fad'in Wayyo Allah da Alhamdulillah, kiran layin Fatun suka shiga yi ba'a d'aga ba Aunty tace k'ilan bata tare da wayar ne gaba d'aya Fauzy a k'agare take da suyi magana Haisam ya fad'o mata a rai gashi kuma bata da lambar wayarta shi tunowa tayi da tana da Lambar Jidderh to itama data kira ba'a d'aga ba don ta bar wayarta a gida,, zuciyar ta ce ta bata ta kira Sameer sai ta tambaye shi lambar Haisam d'in, bayan ta kira saida ta yanke sannan ya kirata, gaida shi tayi kafin tace mashi don Allah lambar Haisam take so farko shiru ya d'an yi sai kuma taji ya tambayi mi zatai da shi a tunanin ta yasan da haihuwar tace mashi tanata kiran layin matar shi ne tayi mata barka to bai shiga shine take son ta kira shi sai ya bata, tambayarta yayi barkan mi zata ma wife en nashi nan ta gane bai san da haihuwar ba ta fad'i mashi yace bai sani ba Allah ya raya, karanto mata lambar yay tayi mashi godiya suna gama wayar ya kira Haisam d'in bayan ya d'aga sun gaisa Sameer d'in yace mashi tunda shi bai so yasan sun yi babies yaji wani wuri Haisam d'in na dariya ya bashi hak'uri yace baya tare da wayarshi ne bai dad'e da ya d'aukko ta daga gida ba ya tambayi ina yaje ya sanar mashi suna hospital ne yace Ok, tambayar lafiyar yaran da Mom d'in su yay Haisam d'in yace mashi duk suna cikin k'oshin lafiya bari ya maida Vedio call ya ga babies d'in nan ma Ok yace, bayan ya maida kiran Vedio nuna mashi yaran ya shiga yi Sameer na kallon shi yanayin fuskar shi da d'an murmushi daga baya yaba Fatuu suka gaisa yay mata barka, bayan Haisam ya amsa Sameer d'in na wani murmushin gefen baki yace Babies d'in sun bayyana he's very active shiyasa sukai Kamannin shi Haisam d'in yay murmushi kawai don su Mom na wurin gudun kada ya k'ara fad'in wata Maganar yasa shi saurin ce mashi ga su Mom yayi masu barka, suna gama yin wayar da Sameer kiran Fauzy na shigowa Haisam ne ya d'auka bayan sun gaisa tayi mashi barka sannan ta fad'i mashi ko wacece ya mik'a ma Fatuu, cikin tsananin farinciki suka yi mata barka harda Aunty suma harda Vedio call suka ga yaran lokacin da Fauzy ta gansu murna kamar kamar me, haka dai akaita yin waya dasu ta wayar Haisam d'in har su gwaggo suma ta nan suka kira, bayan kiraye kirayen wayar sun lafa Dad yace ma su Yasmeen su tashi ya tafi dasu suyi shirin School tun kafin ya rufe baki Mubeen da Mubeena suka tur6une fuska cikin shagwaba suka hau rok'on a k'yale su yau ba sai sunje ba suna Welcoming Babies d'in su Mom tace to ba Babies na nan ba ko sun dawo zasu gansu, da k'yar suka tashi zasu bi shi Jidderh ma ta mik'e zata bi su don akwae abunda take son yi a gidan kafin a sallamo Fatuu, bayan tafiyar su Mom tace bari ta kira Iya a d'aura ruwa Aunty tace a'a tana ganin ba sai anyi wannan ba don bp d'in Fatun ya d'an hau so bata buk'atar ruwan zafi sosae yanzu lafiya lou in sun koma zata iya amfani da na heater zuwa bp d'in ya daidai ta duk da haka ba ruwa masu zafi zata rink'a amfani dasu ba Mom tace Ok kafin cike da kulawa ta kalli Fatuu tace maijego mi take son a dafa mata ne Fatun tayi murmushi kawai gaba d'aya idanunsu na akanta harda Haisam wani irin son ta ne ke mashi yawa a jini jiki, Aunty ce tace a yanzu dai ai tasan zata fi buk'atar farfesu tace ma Fatun hakane ko Daughter ta d'aga mata kai still da murmushi a fuskar tata, masu aikin girkin gidan Mom ta kira ta basu umarnin kalolin farfesun da zasu yi..........