Sashe 191
Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Gidan Haisam ya zama biyu Abuja da Zaria, duk Weekend yake zuwa Zaria wani lokacin a mota ko kuma ya hau jirgi zuwa Kaduna daga nan ya wuto Zaria idan kuma bai samu zuwa da Weekend ba cikin ranakun aiki yake ware rana yazo ya kwana sai ya koma wani lokacin kuma Fatun ce ke zuwa can Abujar akwae driver musamman dake kai ta, su Twins da Esha dai duk suna a Villa wurin Mom sai Weekend Fanan ke ɗaukkosu nan wurinta, sosae Fatuu ke jinjina ƙokarin da Haisam ke yi na zaryar zuwa wurinta ta san duk don ƙaunarta da yake yi ne, duk in yazo haka zatai ta mashi godiya da Addu'o'i, bayan wasu watanni da fara karatun nata suka ji Yadikko ta haihu abun yazo masu a bazata don basu san da tana da ciki ba aikuwa sunyi murna karma Fatuu da Mino suji don ta daɗe bata haihu ba sun ma ɗauka ta gama ne duk da Yadikkon bata wani manyanta ba haka shima Baffan nasu ba wani manyanta yayi ba haihuwa ta biyar ce tayi gashi namiji ta haifa dama bata da ɗa namiji Fatuu taji daɗi data haihu cikin Weekend, da satin suna ya zagayo ranar Friday tana gama lectures ta wuce Abuja washe gari Asabar suna da safe suka bi jirgi zuwa Yola ita da Esha harda Fanan, daga gidan gwamnatin Yola aka tura Motar da zata ɗaukesu harda ta Security suka wuce garin nasu, lokacin da suka isa tayi mamakin ganin yadda aikin hanyar da ake masu yayi nisa harda rijiyoyin burtsatse aka yi masu Fanan sai yaba garin take tana faɗin ya burgeta, anan ta iske Gwaggo da Haulat su jiya suka zo sosae kowa ya nuna farincikin zuwan nasu sai nan nan ake dasu ba kamar Fanan, Yadikko ma sosae tayi murnar zuwansu nan Fatuu ta bata saƙon su Mom harda Aunty kayane masu kyau da tsada atamfofi da laces sai kayan baby wanda yaci sunan Arɗo wato Ibrahim, Fatuu sai santin Babyn take harda ce ma Yadikko ta bata shi tana dariya tace ta ɗauka Fanan da tunda suka zo tana ruƙe dashi tace a'a ita za'a ba sai dariya ake masu, lokacin da Fatuu ta kira Mino Vedio call harda ƙwalla tayi ganin an haɗu banda ita, washe gari da wuri suka fara shirin tafiya saboda bayan sun koma Abuja a ranar kuma Fatuu zata wuce Zaria, tunda Aysha taga suna shirin tafiya ta shiga roƙon Fatuu ta tafi da ita harda ƙwallanta Gwaggo tace da kuma tace ita zata bi Ayshar tace a'a yanzu Adda Fatuu take son bi, to itama Fatun taji tana son tafiya da ita dama Mino na niyyar ɗaukarta tace mata ta shirya kayanta su tafi, Yadikko najin hakan tace ya za'ai ta kama ta tafi da ita ba tare da izinin mijinta ba ai bai kamata kawai ace ta ɗauketa taje masu da ita ba Gwaggo tace hakane kamata yay ace sai ta ambayi izinin shi duk da tasan bazai ƙi ba amman dai yana da kyau ta tambaye shi izni tace to, lokacin data kira Haisam ta faɗi mashi tana son tahowa da Aysha don ta nuna tana son biyota Murmushi yay yace yanzu don zatayi hakan shine sai ta faɗi mashi kada ta manta shi da ita abu ɗaya ne duk abunda yayi mata to shima yayi mashi tana murmushin jin daɗi tayi mashi godiya, wurin ƙarfe sha ɗaya na safe aka zo ɗaukar su suka yi sallama da kowa sai Godiya da Addu'ar Allah ya bar zumunci ake ma Fanan, harda uban naman suna aka basu dana su Mom dama saboda su aka fara aikin naman tunda wuri, kamar kar a rabu haka aka rakosu tare da Aysha dake ta faman washe baki harda su Gwaggo da Haulat su sai gobe zasu tafi suma ta jirgi suka zo kuma tashi zasu koma. Tare da Aysha Fatuu ta koma Zaria Asabe mai aikin Fatun ke kula da ita in ta tafi Makaranta daga baya itama Ayshar Haisam ya sakata a wata private dake anan layout unguwar da suke aka sata aji ukku na Secondary.
Cikin ɗan lokaci HAIFAT TechWorld ya samu kar6uwa a faɗin ƙasar nan, bama nan kaɗai ba harda wasu ƙasashen don kamfani ne da babu kamar sa a yankin Africa ta bangaren technology dama kuma yanzu harkar fasaha ba ƙaramin ci take ba, akwae abubuwa da dama da kamfanin ke samarwa wanda ada sai an dangana da ƙasashen turai yanzu kam nesa tazo kusa a kowacce rana ba ƙaramar riba Kamfanin ke samu ba. A kwana a tashi ba wuya a wurin Ubangiji gashi har kamfanin yayi shekara ɗaya da buɗewa anyi Addu'o'i da bikin murnar cika shekarar inda aka bayyana irin nasarorin da companyn ya samu da kuma irin ayyukan cigaba da ya kawo ma ƙasar nan aka ƙara samun masu son saka hannun jari, an ci an sha an ba ma'aikatan kamfanin masu ƙwazo kyaututtuka shima Haisam ya samu lambobin yabo abun saidai ace Alhamdulillah, bayan cikar kamfanin shekara ɗaya da wasu watanni su Nameer suka dawo Nigeria gaba ɗaya don duk sun gama karatun su, bayan dawowar su Nameer ya fara aiki shima a kamfanin a matsayin Software engineer, ganin Fatuu na karatu a Zaria kuma tana zaune a can Nameer ya yanke nemawa Mino Admission don ta yi degree kan abunda ta karanta a America wato Nursing dama matsayin diploma ce tayi, ba tare da wata wahala ba aka samar mata itama ta fara karatu a can ta zauna a gidan Fatuu, hakan ba ƙaramin daɗi yayi ma Fatun ba dama gidan babban gida ne kowacce da part ɗinta in mazajen su suka zo amman in suka tafi gaba ɗaya harda Aysha a part ɗin Fatuu suke zama rayuwar karatun nasu gwanin daɗi sam basu da wata matsala.
A bangaren Kamalu har ya shiga shekara ta ukku itama Farha tana cikin yin Master's Degree ɗinta a jami'ir Lagos, a bangaren soyayyarsu suna cigaba da gudanar da ita sosae saidai matsalar da Kamalun ke fuskanta a wurinta shine ta cika kishin tsiya ba dama ta kirashi taji yana waya ko bai ɗauka ba sai ta fara zargin ko da wata yake waya ko kuma ya rage sonta haka dai yake ta haƙuri don yasan saboda son da take mashi ne yasa take mashi hakan kuma shima yana son ta sosae.
Kwance tashi har Kamalun ya gama karatun shi na Degree, cikin sa'a result ɗinshi yayi kyau sosae saura kuma yin Nysc, result ɗin nashi na fitowa Fatuu tayi ma Haisam magana kan in zai yuwu ya ɗauke shi aiki a company ɗinshi tunda abunda ya karanta ya danganci aikin kamfanin yace mata lafiya lou zasu ɗauke shi daya gama Service sosae taji daɗi dama ita abunda bata so shine ace Hajiya Maryam ce ta samar mashi aiki gudun wata rana a goranta mashi, Abuja Haisam yasa aka kawo shi yin bautar ƙasan a kamfanin shi ya zauna a gidan su kullum in Haisam ɗin zai tafi aiki tare suke tafiya hakan kuma ba ƙaramin daɗi yayi ma Fatuu ba, tun ma kafin Kamalun ya zama ma'aikacin kamfanin Haisam ya yaba da ƙwazon shi cikin ɗan lokaci Kamalun ya ƙara murmurewa ya zama kalar samarin Abuja, gab da Kamalu zai kammala bautar ƙasar aka fara shirye shiryen yin za6e yayin da waɗanda ke akan mulki duk suka bayyana muradinsu na yin tazarce ciki harda Dad ɗinsu Haisam wanda shi tun kafin ma ayi za6en mutane har sun za6e shi kawai don ya zama dole sai anyi zaben amman Al'umma basu ƙi kawai yaci gaba ba don a mulkinshi sun shar6i romon demokaraɗiyya ba kaɗan ba, a cikin shekaru huɗun da yayi abubuwa da dama sun inganta kama daga ilimi, lafiya, harkar tsaro, wutar lantarki, ruwan sha hanyoyi da dai sauransu gashi an tallafa ma talakawa ta yadda da yawa sun samu abun yi yanzu tun a makaranta ake koya ma yaro sana'a don ya tashi yana da sana'ar yi haka manoma ma harkar abinci ta inganta sosae ake amfani da abincin nan gida gashi da yawan mutanen mu masu ƙwazo dake aiki a ƙasashen waje yayi yadda yay suka dawo suna ma ƙasa aiki hakan ba ƙaramin inganta bangarorin da suke aiki yayi ba ciki harda Asibitoci yanzu saidai don ra'ayin mutum yaje asibitin ƙuɗi ko ya kai ƴaƴanshi makarantun kuɗi ba wai don rashin ingancin na gwamnati ba don komai ya gyaru haka tsofaffin masana'antu da suka daɗe da daina yin aiki duk an farfaɗo dasu abun dai sai son barka (Allah ka bamu shuwagabani irin haka Alfarmar Annabin rahama (S.A.W), Amin ya Hayyu ya ƙayyum).
Cikin ɗan lokaci HAIFAT TechWorld ya samu kar6uwa a faɗin ƙasar nan, bama nan kaɗai ba harda wasu ƙasashen don kamfani ne da babu kamar sa a yankin Africa ta bangaren technology dama kuma yanzu harkar fasaha ba ƙaramin ci take ba, akwae abubuwa da dama da kamfanin ke samarwa wanda ada sai an dangana da ƙasashen turai yanzu kam nesa tazo kusa a kowacce rana ba ƙaramar riba Kamfanin ke samu ba. A kwana a tashi ba wuya a wurin Ubangiji gashi har kamfanin yayi shekara ɗaya da buɗewa anyi Addu'o'i da bikin murnar cika shekarar inda aka bayyana irin nasarorin da companyn ya samu da kuma irin ayyukan cigaba da ya kawo ma ƙasar nan aka ƙara samun masu son saka hannun jari, an ci an sha an ba ma'aikatan kamfanin masu ƙwazo kyaututtuka shima Haisam ya samu lambobin yabo abun saidai ace Alhamdulillah, bayan cikar kamfanin shekara ɗaya da wasu watanni su Nameer suka dawo Nigeria gaba ɗaya don duk sun gama karatun su, bayan dawowar su Nameer ya fara aiki shima a kamfanin a matsayin Software engineer, ganin Fatuu na karatu a Zaria kuma tana zaune a can Nameer ya yanke nemawa Mino Admission don ta yi degree kan abunda ta karanta a America wato Nursing dama matsayin diploma ce tayi, ba tare da wata wahala ba aka samar mata itama ta fara karatu a can ta zauna a gidan Fatuu, hakan ba ƙaramin daɗi yayi ma Fatun ba dama gidan babban gida ne kowacce da part ɗinta in mazajen su suka zo amman in suka tafi gaba ɗaya harda Aysha a part ɗin Fatuu suke zama rayuwar karatun nasu gwanin daɗi sam basu da wata matsala.
A bangaren Kamalu har ya shiga shekara ta ukku itama Farha tana cikin yin Master's Degree ɗinta a jami'ir Lagos, a bangaren soyayyarsu suna cigaba da gudanar da ita sosae saidai matsalar da Kamalun ke fuskanta a wurinta shine ta cika kishin tsiya ba dama ta kirashi taji yana waya ko bai ɗauka ba sai ta fara zargin ko da wata yake waya ko kuma ya rage sonta haka dai yake ta haƙuri don yasan saboda son da take mashi ne yasa take mashi hakan kuma shima yana son ta sosae.
Kwance tashi har Kamalun ya gama karatun shi na Degree, cikin sa'a result ɗinshi yayi kyau sosae saura kuma yin Nysc, result ɗin nashi na fitowa Fatuu tayi ma Haisam magana kan in zai yuwu ya ɗauke shi aiki a company ɗinshi tunda abunda ya karanta ya danganci aikin kamfanin yace mata lafiya lou zasu ɗauke shi daya gama Service sosae taji daɗi dama ita abunda bata so shine ace Hajiya Maryam ce ta samar mashi aiki gudun wata rana a goranta mashi, Abuja Haisam yasa aka kawo shi yin bautar ƙasan a kamfanin shi ya zauna a gidan su kullum in Haisam ɗin zai tafi aiki tare suke tafiya hakan kuma ba ƙaramin daɗi yayi ma Fatuu ba, tun ma kafin Kamalun ya zama ma'aikacin kamfanin Haisam ya yaba da ƙwazon shi cikin ɗan lokaci Kamalun ya ƙara murmurewa ya zama kalar samarin Abuja, gab da Kamalu zai kammala bautar ƙasar aka fara shirye shiryen yin za6e yayin da waɗanda ke akan mulki duk suka bayyana muradinsu na yin tazarce ciki harda Dad ɗinsu Haisam wanda shi tun kafin ma ayi za6en mutane har sun za6e shi kawai don ya zama dole sai anyi zaben amman Al'umma basu ƙi kawai yaci gaba ba don a mulkinshi sun shar6i romon demokaraɗiyya ba kaɗan ba, a cikin shekaru huɗun da yayi abubuwa da dama sun inganta kama daga ilimi, lafiya, harkar tsaro, wutar lantarki, ruwan sha hanyoyi da dai sauransu gashi an tallafa ma talakawa ta yadda da yawa sun samu abun yi yanzu tun a makaranta ake koya ma yaro sana'a don ya tashi yana da sana'ar yi haka manoma ma harkar abinci ta inganta sosae ake amfani da abincin nan gida gashi da yawan mutanen mu masu ƙwazo dake aiki a ƙasashen waje yayi yadda yay suka dawo suna ma ƙasa aiki hakan ba ƙaramin inganta bangarorin da suke aiki yayi ba ciki harda Asibitoci yanzu saidai don ra'ayin mutum yaje asibitin ƙuɗi ko ya kai ƴaƴanshi makarantun kuɗi ba wai don rashin ingancin na gwamnati ba don komai ya gyaru haka tsofaffin masana'antu da suka daɗe da daina yin aiki duk an farfaɗo dasu abun dai sai son barka (Allah ka bamu shuwagabani irin haka Alfarmar Annabin rahama (S.A.W), Amin ya Hayyu ya ƙayyum).