Sashe 95
Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 6 min read
Washe gari lahadi da yamma Aunty Mareeya ta dawo gaba d'aya bakinta bai rufuwa harda kudin da zasu siya kayan da zasu raba ma mutane aka bata, a ranar da daddare Mijin Aunty ya fita dasu suka je wani shopping mall dake kusa dasu suka siyo haddadun manyan biscuits dasu sweet kala kala da chocolate dama ta taho da goro da aka Siya acan Funtua, Washe gari bayan sunje Makaranta Fauzy taba Fatuu kayan ta raba ma mutane amman tace kada ta fad'i wanda zata aura haka Aunty Mareeya tace, sai bayan da aka yi masu break sannan ta rarraba ma yan ajin tana fad'i masu kayan sa rana d'in Fauziyya Ahmad ne akai ta mata Allah yasa Alkhairi harda yan ajin kusa dasu aka rarraba mawa, bayan an gama rabon ne Zainab tazo seat d'in su ta zauna a saman desk tace ma Fatuu amman da gani itama Fauzy dai mai kud'i ne zata aura ko, dariya Fatuu tayi tace miyasa tace haka tace ai ita tunda take bata ta6a ganin an raba irin wannan kayan a saka rana ba kana cin biscuit kunnan ka na motsi har saida ta ba Fauzy dariya, magiya ta hau yi ma Fatuu kan wai ta fad'i mata waye zata aura tana murmushi tace mata d'an uwan mijinta ne, zaro ido Zainab tayi tace bayan k'anwarta da zata auri k'anin shi itama Fauzy kuma d'an uwan shi zata aura tace mata eh cousin d'in shi ne, langa6ar da kai Zainab tayi ta marairaice fuska tace "Wayyo ni Zainabu baiwar Allah ni shine ban samu ko mai aikin gidan ba duk da ba son shi zan yi ba, Don Allah Fateema Ard'o nima ku samo man d'an uwan mijin naki" tana rufe baki Fauzy dake dariya tace mata basu son bak'ar mace sai fara Fatuu kau mi zatayi in ba dariya ba Zainab d'in tace abu mai sauk'i ai hakan ba abu ne mai wuya ba sai ta koma farar, Fauzy ta sake cewa to ai basu son farin bleaching, haka tay ta tsokanar Zainab d'in. Saida aka saka ranar da kwana ukku sannan suka yi waya da Sameer shima ita ta kira shi don ta gaishe shi kuma ko Maganar saka rana d'in bai mata ba har suka gama wayar a fili ta furta lalle akwai aiki a gabanta.
After a Month.......
lokacin cikin Fatuu ya shiga wata na shidda sai lokacin ta fara laulayi sosae, ba komai take ci ba yanzu ga amai da take yi duk da ba sosae take yin shi ba amman data ji k'amshi ko taci abunda bai mata ba sai tayi aman ga kuma kwadayin ciki tafi son abu mai tsami ko yaji a lokacin har an tabbatar da ba d'a d'aya bane a cikin nata sosae kuma ya k'ara girma.
Ranar Alhamis lokacin suna cikin Class wayar Fauzy ta fara vibration alamar ana kiranta, fiddo ta tayi daga cikin Aljihun rigarta lokacin data ga mai kiran nata d'an waro ido tayi gashi akwae malami ba damar ta d'auka, bayan kiran ya yanke sai ga wani ya sake shigowa hakan ya tabbatar mata da magana yake son su yi don in dai ya kirata sau d'aya bata kusa to bai sake kira har sai in ita ta gani ta kira sannan ya k'ara kira, d'agowa tay ta juya ta kalli Fatuu suka had'a ido ganin yanayin fuskar ta yasa k'asa k'asa tace mata ya akai ne sai da ta fakaici idon Malamin nasu sannan tace mata Sameer ne keta kira, d'an bud'a ido Fatuu tay sai kuma tace mata ta d'auki excuse sai taje suyi wayar ta d'aga mata kai, bayan ta maida wayar cikin aljihun ta mik'e ta nufi gaban ajin, tambayar malamin nasu tayi don Allah zata je ta yi fitsari da turanci ya d'aga mata kai ta juya da sauri ta fita, can k'arshen barandar ajin taje ta kai hannu ta fiddo wayar ta fara k'ok'arin kiran shi, har ta yanke bai d'aga ba tay tsaye tana jira ya sake kira aikuwa sai gashi bada dad'ewa ba ya sake kira, d'auka tayi a nutse tayi mashi sallama ya amsa tace ya kira tana cikin class ne kuma akwae malami yanzu ma excuse ta d'auka ta fito ya furta Ok, tambayar ta yayi k'arfe nawa suke tashi tace mashi k'arfe biyu saura kwata nan ma Ok ya furta daga haka taji yace ta koma Class, tsaye tayi turus a wurin a ranta ta shiga tunanin to miyasa ya tambaya, wata zuciyar ce ta raya k'ilan nufin shi ya sake kira can kuma wata zuciyar ta raya mata ko kuma zuwa zai yi, har saida gabanta yay wani dammm ta d'an zaro ido, kokonton anya zuwa zai yi ba tare daya sanar mata ko yazo garin ba ta shiga yi wani sashe na zuciyar tane ya shiga raya mata yana iya zuwan fa abunda tasan halin shi, tunanin kiran Aunty Mareeya tayi ta sanar mata,
"To iya haka yace maki?" Aunty ta tambaya bayan ta kirata tace mata eh, "humm, yanzu in zuwan yay ya zamuyi kenan, ace zuwa ba sanarwa in banda abun suriki na mak'erin rocket, shiru Fauzy tay tama rasa abun cewa, "kuma fa wllh da alama zuwan yayi tunda kince sau biyu yana kiran ki gashi kuma ya tambayi k'arfe nawa kuke tashi k'ilan zuwa zai yi Makarantar kuma dai in dai yazo wurin ki nasan ai da wuya bai zo nan ba" still shiru Fauzy tayi Aunty tace wai ta wani yi shiru bazata bada shawarar abun yi ba, d'an yamutsa fuska Fauzy tay ta yarfa hannu d'aya tace to ai ita tama rasa tunanin da zata yi ne, nannauyar ajiyar zuciya ta saki tace mata to ko ta kira shi ta tambayi zuwa zai yi shiru Fauzy ta d'an yi kafin ta d'an yi guntun tsoki tace gaskiya ba sai ta kira shi ba tunda da ya so ai da ya sanar mata ko kuma ma yana iya ganin kaman wani abu ne yasa aka tambaya, cewa Aunty tayi Shikenan bari tana ganin abunda za'ai kawai ayi shirin kota kwana yanzu dai lokaci ma ya k'ure in ace a shirya lafiyayyen Abinci in zuwan yayi tana ganin bari taje tayi ma maman taufiq magana akwae wata k'awarta chef ce
"In kuma ba zuwan yayi ba fa" Fauzy ta tambaya ta bata amsa da "ke zaki cinye shi kuwa" dariya Fauzy ta saka tace to ita miye laifinta tana yar dariya tace ita kuwa keda laifi tunda laifin shi nata ne don mi in baya ga yana 6aud'add'e zai zo bai sanar dasu ba, a kan hakan sukai sallama ta koma aji, sai bayan da malamin ya fita sannan suka yi magana da Fatuu itama dai zargin k'ilan zuwan zai yi tayi, gaba d'aya hankalin Fauzy ya kasu biyu tana tunanin ko zuwa Sameer zai yi tana kuma sauraren abunda ake masu a haka har aka tashi, tare suka fito da Fatuu ta rakata inda take Parking Motar ta kamar kullum, sallama suka yi tace mata k'ilan dai ba zuwan yayi ba tunda bai sake kira ba watak'il dama kiranta ne zai yi su yi magana Fauzy tace eh itama yanzu haka take tunani tayi mata Allah ya tsare sai sun had'u gobe,
After a Month.......
lokacin cikin Fatuu ya shiga wata na shidda sai lokacin ta fara laulayi sosae, ba komai take ci ba yanzu ga amai da take yi duk da ba sosae take yin shi ba amman data ji k'amshi ko taci abunda bai mata ba sai tayi aman ga kuma kwadayin ciki tafi son abu mai tsami ko yaji a lokacin har an tabbatar da ba d'a d'aya bane a cikin nata sosae kuma ya k'ara girma.
Ranar Alhamis lokacin suna cikin Class wayar Fauzy ta fara vibration alamar ana kiranta, fiddo ta tayi daga cikin Aljihun rigarta lokacin data ga mai kiran nata d'an waro ido tayi gashi akwae malami ba damar ta d'auka, bayan kiran ya yanke sai ga wani ya sake shigowa hakan ya tabbatar mata da magana yake son su yi don in dai ya kirata sau d'aya bata kusa to bai sake kira har sai in ita ta gani ta kira sannan ya k'ara kira, d'agowa tay ta juya ta kalli Fatuu suka had'a ido ganin yanayin fuskar ta yasa k'asa k'asa tace mata ya akai ne sai da ta fakaici idon Malamin nasu sannan tace mata Sameer ne keta kira, d'an bud'a ido Fatuu tay sai kuma tace mata ta d'auki excuse sai taje suyi wayar ta d'aga mata kai, bayan ta maida wayar cikin aljihun ta mik'e ta nufi gaban ajin, tambayar malamin nasu tayi don Allah zata je ta yi fitsari da turanci ya d'aga mata kai ta juya da sauri ta fita, can k'arshen barandar ajin taje ta kai hannu ta fiddo wayar ta fara k'ok'arin kiran shi, har ta yanke bai d'aga ba tay tsaye tana jira ya sake kira aikuwa sai gashi bada dad'ewa ba ya sake kira, d'auka tayi a nutse tayi mashi sallama ya amsa tace ya kira tana cikin class ne kuma akwae malami yanzu ma excuse ta d'auka ta fito ya furta Ok, tambayar ta yayi k'arfe nawa suke tashi tace mashi k'arfe biyu saura kwata nan ma Ok ya furta daga haka taji yace ta koma Class, tsaye tayi turus a wurin a ranta ta shiga tunanin to miyasa ya tambaya, wata zuciyar ce ta raya k'ilan nufin shi ya sake kira can kuma wata zuciyar ta raya mata ko kuma zuwa zai yi, har saida gabanta yay wani dammm ta d'an zaro ido, kokonton anya zuwa zai yi ba tare daya sanar mata ko yazo garin ba ta shiga yi wani sashe na zuciyar tane ya shiga raya mata yana iya zuwan fa abunda tasan halin shi, tunanin kiran Aunty Mareeya tayi ta sanar mata,
"To iya haka yace maki?" Aunty ta tambaya bayan ta kirata tace mata eh, "humm, yanzu in zuwan yay ya zamuyi kenan, ace zuwa ba sanarwa in banda abun suriki na mak'erin rocket, shiru Fauzy tay tama rasa abun cewa, "kuma fa wllh da alama zuwan yayi tunda kince sau biyu yana kiran ki gashi kuma ya tambayi k'arfe nawa kuke tashi k'ilan zuwa zai yi Makarantar kuma dai in dai yazo wurin ki nasan ai da wuya bai zo nan ba" still shiru Fauzy tayi Aunty tace wai ta wani yi shiru bazata bada shawarar abun yi ba, d'an yamutsa fuska Fauzy tay ta yarfa hannu d'aya tace to ai ita tama rasa tunanin da zata yi ne, nannauyar ajiyar zuciya ta saki tace mata to ko ta kira shi ta tambayi zuwa zai yi shiru Fauzy ta d'an yi kafin ta d'an yi guntun tsoki tace gaskiya ba sai ta kira shi ba tunda da ya so ai da ya sanar mata ko kuma ma yana iya ganin kaman wani abu ne yasa aka tambaya, cewa Aunty tayi Shikenan bari tana ganin abunda za'ai kawai ayi shirin kota kwana yanzu dai lokaci ma ya k'ure in ace a shirya lafiyayyen Abinci in zuwan yayi tana ganin bari taje tayi ma maman taufiq magana akwae wata k'awarta chef ce
"In kuma ba zuwan yayi ba fa" Fauzy ta tambaya ta bata amsa da "ke zaki cinye shi kuwa" dariya Fauzy ta saka tace to ita miye laifinta tana yar dariya tace ita kuwa keda laifi tunda laifin shi nata ne don mi in baya ga yana 6aud'add'e zai zo bai sanar dasu ba, a kan hakan sukai sallama ta koma aji, sai bayan da malamin ya fita sannan suka yi magana da Fatuu itama dai zargin k'ilan zuwan zai yi tayi, gaba d'aya hankalin Fauzy ya kasu biyu tana tunanin ko zuwa Sameer zai yi tana kuma sauraren abunda ake masu a haka har aka tashi, tare suka fito da Fatuu ta rakata inda take Parking Motar ta kamar kullum, sallama suka yi tace mata k'ilan dai ba zuwan yayi ba tunda bai sake kira ba watak'il dama kiranta ne zai yi su yi magana Fauzy tace eh itama yanzu haka take tunani tayi mata Allah ya tsare sai sun had'u gobe,